Mayah TV

Mayah TV MayahTV

Tsohon Sanatan Adamawa ta Arewa, Dr. Ishaku Elisha Abbo, ya tabbatar da mutuwar aurensa da matarsa, Patience, bayan shaf...
09/06/2025

Tsohon Sanatan Adamawa ta Arewa, Dr. Ishaku Elisha Abbo, ya tabbatar da mutuwar aurensa da matarsa, Patience, bayan shafe shekaru biyu da rabi da aure.

Wannan na zuwa ne bayan Patience Abbo din ta wallafa sako a shafinta na Facebook a safiyar Talata, 3 ga Yuni, 2025, inda ta ce:

“Mun shafe shekaru biyu da rabi tare. Mun yi ƙoƙari, amma yanzu ya fi dacewa mu rabu juna, Lallai mun fita daga rayuwa mara dadi, Ina yi maka fatan alheri, wannan shafin kuma an rufe shi.”

Awa guda bayan hakan, tsohon Sanatan ya wallafa nasa sakon inda ya ce:

“Ina sanar da mutuwar aurenmu ni da Patience. Don Allah a girmama sirrinmu, Allah ya albarkaci kowa. Na gode.”

Mutuwar auren nasu ta janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda jama’a ke tofa albarkacin bakinsu kan dalilan rabuwarsu.

Arewa Update

Cc; Inside Bauchi State

Bazan ci amanar Buhari da 'Yan Najeriya ba - Zababben shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu Zababben shugaban kasar...
25/05/2023

Bazan ci amanar Buhari da 'Yan Najeriya ba - Zababben shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu

Zababben shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, bayyana cewar, ba zai ci amanar shugaba Muhammadu Buhari da miliyoyin ‘yan Nijeriya ba, bisa ga yarda da amince wa dashi a su kayi, a ranar Alhamis, a Abuja.

Inda ya kuma tabbatar da cewa ya fahimci girman karramawar da aka yi masa da kuma aikin da ke gabansa.

Tinubu yayi wannan alkawari ne a yayin da yake jawabinsa na karbar gaisuwar bayan da aka ba shi a matsayin babban kwamandan gwamnatin tarayya na kasa a dakin taro na dake fadar shugaban kasa a Abuja.

14/05/2023



Takarar kakakin majalisar Wakilan Najeriya 2023: Rt. Hon. Mukhtar Aliyu Betare ya samu goyon bayan mafi rinjaye a majalisar, har ma da abokan takarar sa


Aisha Binani mace ta farko da ta zama gwamna a kasar Najeriya A safiyar Lahadi ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa I...
16/04/2023

Aisha Binani mace ta farko da ta zama gwamna a kasar Najeriya

A safiyar Lahadi ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana Sanata Aishatu Dahiru Binani a matsayin wacce ta lashe zaben gwamnan jihar Adamawa karƙashin inuwar jam'iyyar APC

Kwamishinan zabe na jihar Barista Hudu Yunusa ne ya bayyana hakan bayan kammala zaben da aka gudanar ranar Asabar.

Cikakkun bayanin na zuwan muku nan gaba...

16/03/2023

Bidiyon yadda Shugaba Najeriya Muhammadu Buhari yayi kira ga al'ummar jihar Kano da su zabi dakta Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin gwamnan jihar Kano

Shin a tunanin ku menene dalilin da yasa INEC ta dage zaben? Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta cimma matsay...
08/03/2023

Shin a tunanin ku menene dalilin da yasa INEC ta dage zaben?

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta cimma matsayar dage zaben gwamnoni da na ‘yan majalisun a fadin Jihohin kasar, wanda ya kamata a gudanar ranar Asabar zuwa 18 watan Maris shekarar 2023

Ministan Sadarwa na kasa,  Sheikh Isa Ali Pantami ya sumbaci takardar shaidar lashe zaben, zababben shugaban kasar Najer...
03/03/2023

Ministan Sadarwa na kasa, Sheikh Isa Ali Pantami ya sumbaci takardar shaidar lashe zaben, zababben shugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayin da ya kai masa ziyarar taya murna

03/03/2023

Yadda Shugaba Buhari yayi kira ga 'yan Kaduna da su zabi Uba Sani a matsayin gwamnan su a zaben ranar Asabar

Hotunan yadda shugaban hukumar  zabe ta INEC  Mahmood Yakubu ya damka wa zababben shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ta...
01/03/2023

Hotunan yadda shugaban hukumar zabe ta INEC Mahmood Yakubu ya damka wa zababben shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu tare da maitaimakin sa Kashim Shettima takardar shaidar lashe zaben shugaban kasar Najeriya a yau Laraba, 1 ga wata Maris na shekarar 2023.

📸Daga shafin Buhari Sallau

Nasarar Tinubu Ta Yi Nuni Da Yadda Dimokwaradiyya Ta Yi Aikinta -  Gwamna GandujeGwamna Ganduje ya bayyana Nasarar dan t...
01/03/2023

Nasarar Tinubu Ta Yi Nuni Da Yadda Dimokwaradiyya Ta Yi Aikinta - Gwamna Ganduje

Gwamna Ganduje ya bayyana Nasarar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben 2023, a matsayin shugaban kasa a Najeriya, ta nuna yadda aka yi dimokaradiyya ta gaskiya.

A wani martani ga nasarar da Tinubu ya samu, Gwamna Ganduje ya yaba da gwagwarmayar siyasa da jajircewar daular siyasar Tinubu, wadda ta samar da wasu abubuwa daga ko’ina a fadin kasar nan, wajen tabbatar da cewa dan takarar shugaban kasa ya yi nasara baki daya.

“Sahihancin jarin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a kan ɗan adam, ci gaban ƙasa da haɗin kan ƙasa ya taka muhimmiyar rawa wajen fifita shi ga dukkan sassan ƙasar,” in ji shi.

Ya kara da cewa, “Yakin da Tinubu ya kwashe shekaru da dama yana yi na maido da mulkin dimokuradiyya a kasar nan, ‘yan Najeriya sun fahimta sosai. Don haka, muna ganin hikima da kuma dalili mai kyau na jinginar da makomarmu gare shi.”

Yayin da yake tabbatar da cewa, zababben shugaban kasar zai bullo da dabarun tunkarar matsalolin da s**a addabi al’ummar kasar nan, Gwamna Ganduje ya yabawa shugabannin jam’iyyar da mambobin jam’iyyar da s**a tsaya tsayin daka har zuwa wannan lokaci.

Tinubu, a cewar Ganduje, “Mai ƙwazo ne mai dabara, maginin mutum da sararin samaniya, ƙwararren shugaba na siyasa, shugaba mai yada al’umma, mai jurewa da tabbatar da dimokuradiyya mai dorewa da ci gaba kuma ƙwararren mai motsawa.”

Da wadannan abubuwan da s**a gabata da ma wasu da dama da s**a yi tasiri wajen ganin wanda ya lashe zaben shugaban kasa, Gwamna Ganduje ya kara bayyana cewa, “Tare da zababben shugaban kasarmu, Tinubu, ya jagoranci dimokuradiyya mafi girma a Afirka, tabbas nahiyarmu za ta ci gajiyar dimbin kwarewa. domin ci gaban nahiyar.

"Nasarar da Tinubu ya samu ba wai kawai kasarmu ta uwa ta Najeriya za ta amfana ba, zai kuma zama wani kwarin gwiwa ga Afirka, a matsayinta na nahiya da kuma aiwatar da tsarin dimokuradiyya a duniya," in ji shi.

Cc: alheekmahbogs

01/03/2023

: Kalli Bidiyon dai-dai lokacin da shugaban hukumar zabe, Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda la samu nasarar lashe zaɓen shugaban kasar Najeriya, da misalin karfe 2:30 na dare ranar Talata, a filin tattara sakamakon zabe na kasa, a ranar Talata 28 ga watan Fabrairu shekarar 2023

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya (INEC) ta bayyana Bola Ahmed Tinubu matsayin wanda ya yi nasarar  lashe a zaɓen ...
01/03/2023

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya (INEC) ta bayyana Bola Ahmed Tinubu matsayin wanda ya yi nasarar lashe a zaɓen shugaban ƙasar Najeriya a karkashin inuwar jam'iyyar APC

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mayah TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mayah TV:

Share