28/05/2026
’Yan fashi sun kai hari ɗakunan kwanan dalibai mata a Makarantar SPY dake Adamawa Tare Da sace wayoyi
Daga: Dahiru B Siddiki
Alhamis, 28/Mayu/2026 6:15 na yamma
Wasu ɓarayi dauke da bindigogi, wukake da adduna sun kutsa cikin ɗakin kwanan dalibai mata na harabar Numan ta Kwalejin Fasaha ta Jihar Adamawa, inda s**a kwace wayoyi 15 da sauran kayayyaki masu daraja daga hannun daliban.
Shaidu sun ce wasu dalibai da s**a yi ƙoƙarin hana ɓarayin sace wayoyinsu sun samu raunuka, inda har wata ta suma sak**akon firgici da tashin hankalin harin.
Jaridar DAILY POST ta tattaro da safiyar Alhamis cewa lamarin ya faru ne da sassafe ranar Laraba, 27 ga Mayu, yayin da Musulmi ke shirye-shiryen bikin Sallah.
Daliban da abin ya shafa, suna kuka da halin da s**a shiga, sun zargi hukumomin makarantar da sakaci da kuma rashin tsaro a harabar makarantar.
Harabar Numan ta Kwalejin Fasaha ta Jihar Adamawa ita ce ta biyu mafi girma bayan babbar harabar da ke cikin birnin Jimeta na Yola.
Jami’in hulɗa da jama’a na kwalejin, Mista Albert Matila, ya tabbatar da aukuwar lamarin a harabar Numan, yana mai cewa shugabannin makarantar za su ziyarci ɗakunan kwanan daliban mata da abin ya shafa domin tantance abin da ya faru