Voice of Arewa VOA

Voice of Arewa VOA Voice of Arewa VOA is a Broadcasting Media and Production Company

25/07/2025

Babu kamshin gaskiya a labaran dake yawo na cewa Abubakar Baba Zango ya bar Jam'iyar sa ta APC

Rayuwar Marigayi Sarkin Gusau cike take da hidima da sadaukarwa ga jama’a —Shugaba TinubuShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu...
25/07/2025

Rayuwar Marigayi Sarkin Gusau cike take da hidima da sadaukarwa ga jama’a —Shugaba Tinubu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhini da jimami kan rasuwar Sarkin Katsinan Gusau, Dr Ibrahim Bello, wanda ya rasu da safiyar Juma’a a birnin tarayya Abuja yana da shekaru 71 a duniya.

A cikin wata sanarwa daga mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yada labarai da dabarun watsa bayanai, Mista Bayo Onanuga, Shugaba Tinubu ya bayyana rasuwar marigayi sarkin a matsayin babban rashi da ya wuce iyakar masarautar Gusau, yana mai cewa rayuwarsa cike take da hidima da sadaukarwa ga jama’a a matakai daban-daban na rayuwa.

Shugaban ƙasa ya yabawa marigayin da kishinsa da jajircewa wajen kula da walwala da ci gaban jama’arsa. Ya ce za a ci gaba da tunawa da sarkin bisa jagoranci na nagarta da baiwar jagoranci da Allah ya h**e masa.

Shugaba Tinubu ya mika sakon ta’aziyyarsa ga gwamnatin jihar Zamfara, al’ummar Gusau da kuma iyalan marigayin, tare da addu’ar Allah ya jikan sa, ya sa Aljannah Firdausi ta zama makoma gare shi.

25/07/2025

Babu wani PDP da ya sauya sheke a yankin na Mubi duk labaran karya kawai ake yadawa

ADAMAWA STATE POLICE COMMAND25/7/2025 *SHOOTING RANGE EXERCISE* The Adamawa State Police Command wishes to announce to t...
25/07/2025

ADAMAWA STATE POLICE COMMAND

25/7/2025

*SHOOTING RANGE EXERCISE*

The Adamawa State Police Command wishes to announce to the Public that the Command's Operatives attached to special protection unit (SPU) will conduct a one-day shooting range exercise/Training at Counter Terrorism Unit (CTU) Base, along Mubi road, Girei local Government area, on 27th July, 2025. from 0700hrs (7:am) to 1300hrs (1:pm).

2. The Command calls on members of the Public, especially those residing at Nas Radio station, Sangere FUTY, Federal Housing Hayin Gada amongst others to keep off from the area and not to panic at the sound of shootings until the exercise is over.

3. The Commissioner of Police *CP Dankombo Morris, Psc (+),* appreciates the law-abiding people of Adamawa State for their understandings, cooperation and continuous support in this regard and assured them of the command 's commitment to protecting lives and property.

Signed,
SP SULEIMAN YAHAYA NGUROJE, NIPR,
POLICE PUBLIC RELATIONS OFFICER,
FOR: COMMISSIONER OF POLICE,
ADAMAWA STATE COMMAND.

An zaɓi Farfesa Nentawe Yilwatda A Matsayin Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Bayan Saukar GandujeJam’iyyar APC ta zaɓi Minis...
24/07/2025

An zaɓi Farfesa Nentawe Yilwatda A Matsayin Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Bayan Saukar Ganduje

Jam’iyyar APC ta zaɓi Ministan Harkokin Jinƙai da Rage Talauci, Farfesa Nentawe Goshwe Yilwatda, a matsayin sabon Shugaban Jam’iyyar na ƙasa. Zaɓen ya gudana ne a ranar Alhamis yayin zaman Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na jam’iyyar, inda aka zaɓe shi ba tare da hamayya ba, don maye gurbin Dr Abdullahi Umar Ganduje, wanda ya sauka daga mukamin bisa wasu dalilai na lafiya.

Farfesa Nentawe, wanda aka haifa a ranar 8 ga watan Agusta, 1968 a garin Dungung, ƙaramar hukumar Kanke ta Jihar Filato, fitaccen masani ne a fannin Injiniyan na’ura mai kwakwalwa da Lantarki. Ya yi karatunsa na farko a Jami’ar Noma ta Tarayya da ke Makurdi, sannan ya samu digirinsa na biyu daga ATBU Bauchi, da kuma digirin digirgir daga Jami’ar Najeriya Nsukka. Ya kwashe sama da shekaru 26 yana koyarwa da gudanar da manyan ayyuka a jami’o’i, kuma ya taka rawa a matsayin darektan ICT na farko a jami’ar Makurdi.

Baya ga aikin ilimi, Farfesa Yilwatda ya taka rawa a bangaren kirkire-kirkire da sauyi ta fannin fasaha a ciki da wajen gwamnati. A matsayinsa na kwararre a harkar sadarwa da fasahar zamani, ya yi aiki da manyan kungiyoyin duniya irinsu EU, UNICEF, Bankin Duniya da TECHVILE USA. A shekarar 2017, ya zama kwamishinan zaɓe na INEC, inda ya kawo muhimman sauye-sauye a tsarin zaɓe da s**a haɗa da tsarin kada kuri’a ga ’yan gudun hijira da masu buƙata ta musamman.

Yanzu da ya zama shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Yilwatda ya shigo da ƙwarewa ta musamman, hangen nesa, da sadaukarwa da zai amfani jam’iyyar da ƙasa baki ɗaya. A matsayinsa na shugaban kamfen ɗin Tinubu/Shettima a Jihar Filato, kuma Ministan Jinƙai, yana da zurfin alaƙa da ɓangarori da dama na gwamnati da ƙungiyoyin ci gaba, wanda hakan zai taimaka wajen jagorantar jam’iyya cikin hadin kai da nasara.

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon DajiGwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da sababbin cibiyoyi...
24/07/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da sababbin cibiyoyi guda uku na zamani domin kula da masu fama da cutar daji (cancer) a sassa daban-daban na ƙasar nan.

Cibiyoyin sun haɗa da na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Benin (UBTH) a Jihar Edo, Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Katsina, da kuma Asibitin Koyarwa na Jami’ar Nijeriya (UNTH) da ke Enugu.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafin sa na X, inda ya ce wannan cigaba wani ɓangare ne na shirin farfaɗo da harkar lafiya da gwamnatin Shugaba Tinubu ke aiwatarwa a faɗin ƙasar nan.

A cewar ministan, shi da sauran abokan aikin sa, Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate, da Ministan Kuɗi, Mista Wale Edun, sun halarci bikin ƙaddamar da ɗaya daga cikin manyan ayyukan, wanda ya gudana a Jihar Katsina.

Cibiyoyin da aka ƙaddamar na cikin zagaye na farko na shirin gina sababbin cibiyoyin maganin ciwon daji guda shida a manyan Asibitocin Koyarwa na Tarayya a ƙasar nan.

Wannan cigaba wani muhimmin mataki ne wajen rage wahalar da marasa lafiya ke fuskanta wajen samun ingantacciyar kulawa, da kuma hana fita ƙasashen waje don neman magani.

Gwamnatin ta tabbatar da cewa sauran cibiyoyin da s**a rage za su kammala nan ba da jimawa ba domin cika alƙawarin samar da ingantaccen tsarin lafiya ga kowa da kowa a Nijeriya.

24/07/2025

An tiki rawa a wani taron APC da al'ummar Vere Zone s**a gabatar a karkashin jagorancin Hon. Abdullahi Umar Yapak

23/07/2025

Allah Sarki mutane na cikin wani yanaiy Kalli abin da Gidauniyar AB Haske Foundation tayi na ceto rayuwar al'ummar

Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, inji Ministan Yaɗa LabaraiMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Ka...
23/07/2025

Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, inji Ministan Yaɗa Labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yana da cikakken goyon baya ga ’yancin faɗar albarkacin baki da ’yancin ’yan jarida, tare da fahimtar muhimmancin rawar da kafafen yaɗa labarai suke takawa wajen gina ƙasa.

Da yake jawabi a taron lacca na shekara-shekara na kamfanin jaridar Blueprint wanda aka gudanar a ranar Talata a Abuja, Idris ya ce tun farkon naɗin sa, Shugaba Tinubu ya bayyana masa cewa ya ba shi dama ya yi aikin sa yadda ya ga ya dace a matsayin sa na ƙwararre.

Ya ce: “Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu babban mai goyon bayan kafafen yaɗa labarai ne. Yana da masaniyar cewa kafafen yaɗa labarai suna da matuƙar muhimmanci wajen gina ƙasa, kuma ya sha gaya mini cewa in ci gaba da aiki na yadda na ga ya dace, kasancewa ta ƙwararre.”

Ya ƙara da cewa, “Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ba zai taɓa, a kowace hanya ko salo, tauye ko hana ci gaban aikace-aikacen kafafen yaɗa labarai a wannan ƙasa ba. Amma dole ne mu duka ‘yan jarida da masu aikin yaɗa labarai mu haɗa kai, mu bi wannan hanya mai sarƙaƙiya, mu tabbatar da cewa al’umma tana ci gaba da zama cikin haɗin kai, yayin da muke riƙe shugabanni da gwamnati da alhakin aikin su.”

Idris ya jaddada muhimmancin kafafen yaɗa labarai wajen kula da tsarin dimokiraɗiyya, inda ya shawarci ’yan jarida da su kula da rawar da suke takawa domin kada su zama abin da zai jawo ruɗani ko rikici a cikin al’umma.

“A yayin da kuke yin wannan aiki, kuna da babban nauyi na riƙe gwamnati da shugabanni da alhakin aikin su. Amma ko da kuna yin hakan, dole ne ku sani cewa saboda matsayin ku na musamman da rawar da kuke takawa, za ku iya taimaka wa ƙasa matuƙa, amma idan ba a yi taka-tsantsan ba, ayyukan ku na iya cutar da al’umma,” inji shi.

Ya bayyana buƙatar sanin ya kamata da hankali wajen tantance sahihin bayani daga wanda zai iya ɓata zaman lafiya ko raba kan al’umma.

Ministan ya ce duk da ƙalubalen da ke fuskantar fannin yaɗa labarai, akwai haske a gaba domin kafafen sun ci gaba da nuna jajircewa da ɗorewa.

Ya kuma bayyana cewa ba shi ba ne Shugaban kamfanin jaridar Blueprint ba tun bayan da aka naɗa shi Minista.

“Ba ni ne shugaban jaridar Blueprint ba yanzu. Ni ma baƙo ne aka gayyata zuwa wannan taro. Na san cewa a baya ni ne ke gaba wajen shirya wannan taron na Blueprint, musamman tun lokacin da aka kafa ta shekaru 14 da s**a wuce. Dole ne in gode wa waɗanda aka gayyata su haɗu da ni a watan Mayun 2005 domin tunanin fara jaridar Blueprint: Malam Ibrahim Sheme; Manajan Darakta, Malam Salisu Umar; Shugabar Kwamitin Tace Labarai, Hajiya Zainab Okino, da dukkan ma’aikatan jaridar Blueprint.

“Na gode da cigaba da tafiyar da abin da muka faro cikin nasara. Na shekara guda ban ziyarci ofishin ba, amma ina ganin lokaci ya yi da zan yi hakan. Ina so in ga ko har yanzu kuna ci gaba da tafiyar da abin da muka faro. Ina alfahari kuma ina farin ciki da cewa abin da muka fara ya ci gaba da bunƙasa,” inji shi.

Idris ya taya waɗanda s**a samu kyaututtuka murna, inda ya bayyana cewa ba a yi masu kyautar bisa wani son zuciya ko tasiri daga wani waje ba, sai hukuncin jaridar ne kaɗai.

Cikin manyan baƙin da s**a halarci taron akwai Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume; Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin; Ministan Ma’adanai, Dakta Dele Alake; Ministan Raya Noman Dabbobi, Idi Mukhtar Maiha; Etsu Nupe, Mai Martaba Alhaji Yahaya Abubakar, da babban baƙon jawabi na taron, Farfesa Attahiru Jega.

23/07/2025

Wannan shine wasu nasarori da rundunar Yan Sandan Jihar Adamawa ta samu a cikin Wata uku

RASUWAR BUHARI!Tinubu Ya Koka, Ya Gargadi Gwamnonin Najeriya: "Rasuwar Buhari ta girgiza ni sosai har ga tsokokin jiki n...
22/07/2025

RASUWAR BUHARI!
Tinubu Ya Koka, Ya Gargadi Gwamnonin Najeriya:

"Rasuwar Buhari ta girgiza ni sosai har ga tsokokin jiki na. Ban samu barci ba tsawon kwana biyu da s**a wuce.
Saboda haka, ni Jagaban, ina kira ga duk masu rike da madafun iko, musamman gwamnonin jihohi ku yi hattara!"

"Na dade ina turawa jihohinku tiriliyan-tiriliyan, amma babu abin kirki da ake gani —musamman a fannin ayyukan ci gaba da na jin dadin jama’a.
Abin da kawai kuke yi shine almubazzaranci. Ku sani, babu abin da ke dorewa. Wata rana, za mu tsaya gaban Allah mu bada amsa!"

~ Shugaba Tinubu ga Gwamnonin Najeriya – TVC

22/07/2025

Kalaman da tsofaffin kwamishinoni daga 2015 zuwa 2019 s**ayi a kan APC da kuma Malam Nuhu Ribadu

Address

Yola

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Voice of Arewa VOA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Voice of Arewa VOA:

Share