Voice of Arewa VOA

Voice of Arewa VOA Voice of Arewa (VOA) is a broadcasting media and production company based in Northern Nigeria.

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da shirin gaggawa na kula da lafiyar jarirai a Jihar KanoHukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (...
18/09/2025

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da shirin gaggawa na kula da lafiyar jarirai a Jihar Kano

Hukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIA) ta kaddamar da wani sabon shiri na gaggawa domin rage mace-macen jarirai da ƙara samun damar kula da lafiyar jarirai a asibitocin gwamnati a faɗin ƙasar nan.

An kaddamar da wannan shirin ne a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano da ke jihar Kano, inda shugaban NHIA, Dr Kelechi Ohiri, ta ce shirin zai mayar da hankali kan jarirai da ke fuskantar matsalolin gaggawa bayan haihuwa.

Dr Ohiri, wadda Dr Salawudeen Sikiru ya wakilta, ya bayyana cewa shirin ya samo asali daga wani tsari na kulawa da lafiyar iyaye mata da aka fara fiye da shekara guda da ta gabata.

“Mun fara wannan shiri ne don rage mace-macen iyaye mata da jarirai. Matakin farko ya shafi uwa, yanzu kuma mun kaddamar da bangaren jarirai domin magance matsalolin gaggawa bayan haihuwa,” in ji shi.

Ya ce yanzu haka NHIA tana ɗaukar nauyin kuɗin magani ga jarirai a asibitocin gwamnati, inda asibitoci ke karɓar kudaden da s**a kashe a kowane mako bayan an tabbatar da bayanan jinya.

“Ayyukan da shirin ya ƙunsa sun haɗa da kula da jariran da aka haifa ba su gama girma ba, matsalolin rashin numfashi bayan haihuwa, rawayar ido da fata (jaundice), cutar jini (sepsis) da matsalolin tiyata ga jarirai,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa shirin ba zai tsaya kawai kan kulawar gaggawa ba, domin bayan an ceto jaririn za a yi masa rajista a kan inshorar lafiya ta ƙasa domin ya ci gaba da samun kulawa.

Shirin zai shafi iyalai marasa galihu ne kawai, tare da buƙatar lambar NIN domin tabbatar da sahihancin rajista.

A cewarsa, wannan matakin na farko zai gudana har zuwa shekarar 2027, tare da burin ganin kowane jariri mai buƙata ya samu kulawa a asibitocin da s**a shiga cikin shirin.

Shugaban Asibitin Koyarwa na Aminu Kano, Farfesa Abdulrahman Sheshe, ya yaba wa Gwamnatin Tarayya da NHIA bisa wannan mataki, yana mai cewa zai taimaka wajen rage mace-macen jarirai da kuma ƙara inganta ayyukan lafiya a manyan asibitoci.

Ya kuma yi kira ga gwamnati da ta ci gaba da ɗaukar nauyin irin waɗannan shirye-shirye na dogon lokaci, yana mai cewa su ne ginshikin tabbatar da tsarin kiwon lafiya da ya dace da bukatun ’yan ƙasa.

17/09/2025

Allah Sarki wannan shine halin da al'ummar bajabure na jihar Adamawa suke ciki

Shugaba Tinubu ya kawo ƙarshen dokar ta-baci a Jihar RiversShugaba Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da kawo ƙarshen dokar ta-...
17/09/2025

Shugaba Tinubu ya kawo ƙarshen dokar ta-baci a Jihar Rivers

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da kawo ƙarshen dokar ta-baci da aka sanya a Jihar Rivers tun a ranar 18 ga Maris, 2025.

A cikin jawabin da ya gabatar daga fadar shugaban ƙasa, Tinubu ya ce an kafa dokar ta-bacin ne sakamakon rikicin siyasa da ya yi ƙamari tsakanin Gwamnan jihar, Siminalayi Fubara, da ’yan majalisar dokokin jihar.

Shugaban ya bayyana cewa rikicin ya kai ga gaza gudanar da harkokin gwamnati, inda aka samu rarrabuwar kawuna tsakanin ’yan majalisar, guda huɗu na goyon bayan gwamna yayin da sauran 27 ke goyon bayan kakakin majalisar.

Ya ce hakan ya hana gabatar da kasafin kuɗi, abin da ya haddasa durƙushewar gwamnati gaba ɗaya, lamarin da Kotun Koli ta tabbatar da shi a hukuncinta, inda ta bayyana cewa babu gwamnati a Rivers State.

Tinubu ya ce duk da ƙoƙarinsa da na wasu ’yan Najeriya don shawo kan rikicin, bangarorin biyu sun ƙi sasantawa, lamarin da ya tilasta shi amfani da sashe na 305 na kundin tsarin mulkin 1999 wajen kafa dokar ta-baci.

“Idan ban ɗauki wannan mataki ba a lokacin da aka kai ga mummunan halin da gwamnati ta gaza aiki, to da na gaza wajen kare zaman lafiya da tsaron jama’a,” in ji Shugaba Tinubu.

Ya kuma gode wa majalisar dokokin tarayya, sarakunan gargajiya da jama’ar Rivers bisa goyon bayan da s**a bayar yayin dokar ta-bacin.

Shugaban ya ce bayan samun sabon yanayi na fahimtar juna da shirye-shiryen komawa ga tsarin dimokuraɗiyya, ba bu dalilin ci gaba da dokar ta-bacin bayan cikar watanni shida.

Saboda haka, daga misalin ƙarfe 12 na daren 17 ga Satumba, 2025, dokar ta-bacin ta ƙare. Gwamna Fubara, mataimakiyarsa Ngozi Nma Odu, da kakakin majalisar, Martins Amaewhule, tare da ’yan majalisar za su koma bakin aiki daga ranar 18 ga Satumba, 2025.

Shugaba Tinubu ya yi amfani da damar wajen tunatar da sauran gwamnonin jihohi da majalisun dokoki cewa zaman lafiya da kyakkyawan shugabanci su ne tushen kawo romon dimokuraɗiyya ga ’yan ƙasa.

17/09/2025

Masu tafiya su tafi mu Muna tare da Fintiri Inji Turakin Shinko

Gwamnatin Tarayya ta fara aikin  samar da wutar lantarki daga hasken rana a  Asibitin Koyarwa na Aminu Kano.Shugaban Huk...
17/09/2025

Gwamnatin Tarayya ta fara aikin samar da wutar lantarki daga hasken rana a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano.

Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Makamashi ta Ƙasa (ECN) Dr Mustapha Abdullahi ya ce wutar lantarkin mai ƙarfin Megawatt huɗu (4MW) za ta bai asibitin damar rabuwa da layin wutar lantarki na ƙasa baki ɗaya.

Dr Mustapha Abdullahi, ya ce aikin na daga cikin manufofin Renewed Hope Agenda na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Ya bayyana cewa wannan tsari zai kawo ƙarshen matsalar yawan yanke wuta a asibitin, lamarin da a baya ya haddasa asarar rayukan marasa lafiya guda uku a lokacin da ayyukan asibitin s**a tsaya cak.

“Da wannan tsari, ba za a sake samun irin waɗannan matsaloli ba. Burinmu shi ne mu samar da makamashi mai tsafta da nagarta wanda zai ƙarfafa cibiyoyin kiwon lafiya tare da inganta rayuwar ’yan Najeriya,” in ji shi.

Hukumar Kwastan ta Najeriya ta dakatar da aiwatar da harajin kashi 4% na kayan da ake shigo da su bisa umarnin Ma’aikata...
16/09/2025

Hukumar Kwastan ta Najeriya ta dakatar da aiwatar da harajin kashi 4% na kayan da ake shigo da su bisa umarnin Ma’aikatar Kudi

Hukumar Kwastan ta Najeriya (NCS) ta bayyana cewa ta karɓi umarnin Ma’aikatar Kudi na dakatar da aiwatar da harajin kashi 4% na Farashin kaya kafin ɗauko su daga ƙasar da aka samo su wato Free-on-Board (FOB) da aka ɗora kan kayayyakin da ake shigo da su ƙasar nan.

A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Dr Abdullahi Maiwada, ya fitar a ranar Litinin, hukumar ta ce tana godiya da wannan matakin da Ma’aikatar Kudi ta ɗauka tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da bin manufofin gwamnati na tattalin arziƙi.

Dr Maiwada ya ce hukumar ta fara tattaunawa da Ma’aikatar Kudi domin tabbatar da cewa ba a samu cikas a ayyukan hukumar ba.

Hukumar ta kuma yi karin haske kan rahotannin da ke yaɗuwa a kafafen yaɗa labarai cewa harajin kashi 4% na FOB ƙirƙiro shi a kayi a ‘yan kwanakin nan. Ta ce wannan tanadi ne na doka da Majalisar Tarayya ta kafa a cikin Sashe na 18(1)(a) na Dokar Hukumar Kwastan ta 2023, wanda ya tanadi cewa “ba za a karɓi kasa da kashi 4% na FOB ba akan kayayyakin da ake shigo da su, bisa tsarin da duniya ke bi.”

Hukumar ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta yadda ya kamata ba tare da tangarda ba, tare da tabbatar da sauƙaƙe cinikayya da kuma ƙara samun kudaden shiga ga gwamnati.

“Muna da kwarin gwiwa cewa tattaunawa da Ma’aikatar Kudi da sauran masu ruwa da tsaki za su samar da mafita da za ta fi amfani ga Najeriya baki ɗaya, ta hanyar ƙara samun kudaden shiga da bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa,” in ji sanarwar.

Hukumar Kwastan ta ce za ta ci gaba da aiki da ‘yan kasuwa, masu fitar da kaya da hukumomin ƙasa da ƙasa wajen tabbatar da gudanar da ayyuka cikin bin ƙa’idoji.

Farashin kayan masarufi na ci gaba da sauka a Najeriya - Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS)Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ...
16/09/2025

Farashin kayan masarufi na ci gaba da sauka a Najeriya - Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS)

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin kaya a Najeriya ya sauka zuwa kashi 20.12 cikin ɗari a watan Agusta 2025.

A cikin rahoton da hukumar ta fitar kan Consumer Price Index (CPI) da hauhawar farashin kaya na watan Agusta, ta bayyana cewa adadin ya ragu da kashi 1.76 cikin ɗari idan aka kwatanta da na watan Yuli wanda ya kai kashi 21.88 cikin ɗari.

Hukumar ta ce idan aka yi la’akari da shekara ɗaya kacal, hauhawar farashin kaya ya yi ƙasa da kusan kashi 12.03 cikin ɗari, inda a watan Agusta 2024 aka samu kashi 32.15 cikin ɗari.

Rahoton ya kuma nuna cewa, hauhawar farashin abinci ya tsaya a kashi 21.87 cikin ɗari idan aka kwatanta da bara, inda ya kai kashi 37.52 cikin ɗari.

A matakin wata zuwa wata kuwa, farashin abinci ya tsaya a 1.65 cikin ɗari, bayan da a watan Yuli ya kai 3.12 cikin ɗari.

A cikin rahoton, an bayyana cewa hauhawar farashi a birane ya tsaya a 19.75 cikin ɗari, yayin da a karkara ya kai 20.28 cikin ɗari.

Rahoton ya kawo jerin jihohin da s**a fi samun hauhawar farashi a shekara wanda suma haɗa da:
• Ekiti (28.17%)
• Kano (27.27%)
• Oyo (26.58%)

Jihohin da s**a fi samun saukin hauhawar farashi kuwa sun haɗa da:
• Zamfara (11.82%)
• Anambra (14.16%)
• Enugu (14.20%)

A bangaren abinci kuwa, rahoton ya ce jihohin da s**a fi hauhawar farashi a shekara sun haɗa da:
• Borno (36.67%)
• Kano (30.44%)
• Akwa Ibom (29.85%)

Yayin da Zamfara (3.20%), Yobe (3.60%) da Sokoto (6.34%) s**a fi samun sauki.

16/09/2025

Wata Sabuwa PDP a karamar hukumar Girei sun fasa kwai mai wari kan zaben da akayi

16/09/2025

PCRC ta nada mambobinta domin dakile amfani da kayan kungiyar ba bisa ka’ida ba.

16/09/2025

An kashe wani matashi a gonansa dake garin Ngurore a jihar Adamawa.

16/09/2025

Halin da ake ciki a yanzu haka a anguwar Wuri Jabbe Sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya

16/09/2025

Gwamnatin Tarayya ta dakatar da kudin harajin kwastam na kashi 4% kan Kayan da ake shigo da su Najeriya

Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta dakatar da aiwatar da kudin harajin kashi 4% na Farashin kaya kafin ɗauko su daga ƙasar da aka samo su ( Free on Board [FOB]) da Hukumar Kwastam ta sanya a kan kayayyakin da ake shigo da su ƙasar.

Ma’aikatar Kuɗi ta ce an ɗauki wannan mataki ne bayan dogon nazari da shawarwari daga masana harkar kasuwanci, masana tattalin arziki da kuma jami’an gwamnati.

A cewar Ma’aikatar, an gano cewa harajin na iya jefa ƙasar cikin ƙarin matsaloli na hauhawar farashi, tsadar kayayyaki, da kuma rage gasa a harkokin kasuwanci.

Wata sanarwa da Babban Sakataren Ma’aikatar Kuɗi, R. O. Omachi ya fitar, ta ce yawancin ’yan kasuwa da masu shigo da kaya sun nuna damuwa kan wannan haraji saboda nauyin da zai dora musu.

Sanarwar ta ce dakatarwar za ta ba da damar tattaunawa da sake nazari kan tsarin, tare da shirin samar da wata hanya mafi daidaito da za ta taimaka wajen tara kuɗaɗen shiga da kuma tabbatar da ci gaban tattalin arzikin ƙasa.

Ma’aikatar ta kuma umurci hukumomin da abin ya shafa da su tabbatar da bin wannan umarni kai tsaye.

Address

YOLA AREWA MASO GABASHIN NIJERIYA ADAMAWA
Yola

Telephone

+2348067278515

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Voice of Arewa VOA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Voice of Arewa VOA:

Share