Jada Daily News

Jada Daily News Mutanen Jada nesa ta zo kusa..

An buɗe shafin jaridar Jada Daily News a fecbook, ranar 16 ga watan Afrilu 2026 domin wallafa muku labarai da Dumi-Duminsu, haɗa da bidiyoyi, cikin harshen Hausa.

DA DUMI-DUMI: INEC ta mayar da sunan David Mark a matsayin Shugaban ADC na ƙasa tare da mambobin NWC a cikin tsarin ta, ...
30/04/2026

DA DUMI-DUMI: INEC ta mayar da sunan David Mark a matsayin Shugaban ADC na ƙasa tare da mambobin NWC a cikin tsarin ta, bayan hukuncin Kotun Koli na yau.

Sanata Adolphus Wabara ya karɓi ragamar PDP bayan hukuncin Kotun ƘoliShugaban Kwamitin Amintattu (BoT) na jam’iyyar PDP ...
30/04/2026

Sanata Adolphus Wabara ya karɓi ragamar PDP bayan hukuncin Kotun Ƙoli

Shugaban Kwamitin Amintattu (BoT) na jam’iyyar PDP ya sanar da karɓar ragamar shugabancin jam’iyyar a matakin ƙasa, sakamakon hukuncin Kotun Ƙoli da ya soke shugabancin Tanimu Turaki da na Abdulrahman Muhammad.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban BoT na PDP, Sanata Adolphus Wabara, ya fitar ranar, inda ya ce matakin ya zama dole domin kauce wa gibin shugabanci a jam’iyyar.

YANZU-YANZU: Kotun Ƙoli ta fara sauraren shari’ar rikicin shugabancin jam’iyyar ADC tsakanin ɓangaren Nafi’u Bala da San...
30/04/2026

YANZU-YANZU: Kotun Ƙoli ta fara sauraren shari’ar rikicin shugabancin jam’iyyar ADC tsakanin ɓangaren Nafi’u Bala da Sanata David Mark.

DA DUMI-DUMI: Kotun koli ta soke babban taron jam’iyyar PDP na kasa da aka gudanar a Ibadan, inda aka zaɓi Tanimu Turaki...
30/04/2026

DA DUMI-DUMI: Kotun koli ta soke babban taron jam’iyyar PDP na kasa da aka gudanar a Ibadan, inda aka zaɓi Tanimu Turaki a matsayin shugaban jam’iyyar.

YANZU-YANZU: Kotun Ƙoli ta zauna domin fara sauraren ƙarar jam’iyyun PDP da ADC. Yayi da ake sa ran kotun za ta yanke hu...
30/04/2026

YANZU-YANZU: Kotun Ƙoli ta zauna domin fara sauraren ƙarar jam’iyyun PDP da ADC. Yayi da ake sa ran kotun za ta yanke hukunci a yau kan takaddamar da ke cikin jam’iyyun.

Wannan shari’a na daga cikin abubuwan da ke jan hankalin jama’a a faɗin ƙasar.

YANZU-YANZU: Jama’a sun yi cikar ƙwari a gaban Kotun Koli domin jin hukunci Kotun kan shari’o’in rikicin shugabanci na A...
30/04/2026

YANZU-YANZU: Jama’a sun yi cikar ƙwari a gaban Kotun Koli domin jin hukunci Kotun kan shari’o’in rikicin shugabanci na ADC da PDP da za a yanke hukunci ayau

Me kuke hasashe, Nafiu ko David Mark wa kuke wa fatan nasara a ADC?

Sannan Wike ko Su Tanimu Turaki wa ku ke wa fatan nasara a PDP?

ZABEN 2027: Matashi Dan gwogwarmaya kuma jakadan zaman lafiya ƙarƙashin Ƙungiyar Arewa Peace Ambassador Forum, Comr Isa ...
30/04/2026

ZABEN 2027: Matashi Dan gwogwarmaya kuma jakadan zaman lafiya ƙarƙashin Ƙungiyar Arewa Peace Ambassador Forum, Comr Isa Oga Abdulmumini ya nuna damuwa kan yadda ra'ayin Siyasa ke raba kan matasa wajen neman kawo sauyin Shugabanci a Najeriya.

Matashin ya ce dole matasa su hada kai, su rugumin mafitar kasar ta hanyar marawa 'yan takara na gari a lokacin zabukan 2027.

Jinanen Waɗanda S**a Rasu Ba Bisa Haƙki Ba Zai Tuhume KaTsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya soki Shugaba...
30/04/2026

Jinanen Waɗanda S**a Rasu Ba Bisa Haƙki Ba Zai Tuhume Ka

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya soki Shugaban Ƙasa Bola Tinubu kan kalaman da ya yi na neman tazara domin sake tsayawa takara, a daidai lokacin da ake fuskantar ƙalubalen tsaro a ƙasar.

Atiku ya ce kamata ya yi gwamnati ta fi mayar da hankali kan magance matsalar tsaro da ke ƙara ta’azzara maimakon maganar siyasar zaɓe.

'Strait of Trump', shi ne sabon sunan da shugaban Amurka Donald Trump ya wallafa a dandalinsa na truth social, bayan da ...
30/04/2026

'Strait of Trump', shi ne sabon sunan da shugaban Amurka Donald Trump ya wallafa a dandalinsa na truth social, bayan da wani ya wallafa neman a sauya sunan mashigin 'Strait of Hormuz'

DA DUMI-DUMI: Gomnatin Tarayya ta aiyana Ranar Jumma,a a matsayin Ranar Hutu Ranar ma,aikata
29/04/2026

DA DUMI-DUMI: Gomnatin Tarayya ta aiyana Ranar Jumma,a a matsayin Ranar Hutu Ranar ma,aikata

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa zai nemi wa’adi na biyu a mulki, yana mai cewa matsalar rashin tsa...
29/04/2026

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa zai nemi wa’adi na biyu a mulki, yana mai cewa matsalar rashin tsaro ba za ta tilasta masa barin mulki ba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, Tinubu ya faɗi hakan ne yayin karɓar Gwamnan Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, da wasu masu ruwa da tsaki daga jihar.

DA DUMI-DUMI: A yau Laraba matasan gidan Professor Isa Ali Pantami da s**a hada mishi fiye da Naira miliyan sittin (N60,...
29/04/2026

DA DUMI-DUMI: A yau Laraba matasan gidan Professor Isa Ali Pantami da s**a hada mishi fiye da Naira miliyan sittin (N60,000,000) kudin siyan form din tsayawa takara sun cika burinsu na siyan form din.

Idan baku manta ba a ranar Jumma'a da ta gabata Matasan da Professor Isa Ali Ibrahim (Pantami), CON, PhD, yayi silar taimakon rayuwarsu da masoyanshi s**a kudiri aniyar saya mishi form din tsayawa takarar Gwamnan jihar Gombe a kokarin matasan na maida halaccin taimakonsu da Professor Isa Ali Pantami yayi a rayuwarsu.

Wannan dalilin yasa matasan s**a kafa kwamitin gaggawa a tsakaninsu ba tare da wani ya saka su ba, inda a cikin kwanaki biyu kacal s**a hada fiye da Naira miliyan sittin (N60,000,000) kudin da ya zarce na iya siyan form din.

Dukkannin mutanen da s**a bada gudummuwarsu babu wanda aka saka ya bayar kowa radin kanshi

Wannan yake kara nunawa duniya cewa Majidadin Daular Usmaniyya ya kafa matasa da ayyukan yi a damar da ya samu.

A yau Laraba wakilan wasu daga cikin matasan s**a je inda ake saida form din, s**a cika burinsu na siyawa Malam Isa Ali Pantami form din kamar yadda s**a kudiri aniya.

Address

Jada Local Government
Yola
069600

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jada Daily News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share