Adamawa Press Team

Adamawa Press Team The Adamawa Press Team offers various services focused on promoting quality thought and freedom for human development.

ANA GAYYATAR AL'UMMAR MUSULMI MUZAHARAR MAULIDI A GOMBI.
04/09/2026

ANA GAYYATAR AL'UMMAR MUSULMI MUZAHARAR MAULIDI A GOMBI.

🌹 SANARWAR GAYYATA ZUWA MAULIDI 🌹Halkar Samunaka Welcome tana gayyatar daukacin ’yan uwa Musulmi da masoya Fiyayyen Hali...
04/09/2026

🌹 SANARWAR GAYYATA ZUWA MAULIDI 🌹

Halkar Samunaka Welcome tana gayyatar daukacin ’yan uwa Musulmi da masoya Fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad (S.A.W), zuwa taron Maulidi da ’yan uwa almajiran Shaikh Ibrahim Zakzaky (H) na unguwar s**a saba shiryawa duk shekara.

✨ Taron zai gudana In shaa Allahu kamar haka:

📅 Rana: Yau Jumu’a, 04/09/2026

📍 Wuri: SAMUNAKA KARSHEN KOLTA LAYIN JAJERI GALKU.

🕢 Lokaci: 07:30 na dare.

🌹 Kada a manta! Ku zo domin murnar zagayowar haihuwar Fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad (S.A.W).

🤲 Allah (S.W.T) Ya ba mu ikon halarta, Ya sanya albarka a cikin wannan taro. Amin.

✍️ Adamawa Press Team Services

03/09/2026

TAFSEER MAJLIS

| Tafsirin Alqur’ani mai girma Tare da Hujjatul Islam, Shaikh Muhammad Gidado Hamman Yola, Daga Masallacin Jumma'a Na Nassarawo, Jimeta Yola, Adamawa State.

Alhamis
(08/09/2026)



©️ Adamawa Press Team Services

GWAMNA FINTIRI YA JAGORANCI TARON MAJALISAR ZARTARWA TA JIHAR ADAMAWA KARO 13, YA AMINCE DA MUHIMMAN AIYUKA DA KUMA MANU...
02/09/2026

GWAMNA FINTIRI YA JAGORANCI TARON MAJALISAR ZARTARWA TA JIHAR ADAMAWA KARO 13, YA AMINCE DA MUHIMMAN AIYUKA DA KUMA MANUFOFI MASU KYAU.

Gwamnan Jihar Adamawa, Rt. Hon. Ahmadu Umaru Fintiri, a yau ya jagoranci taron Majalisar Zartarwa ta Jihar Adamawa (EXCO) karo na 13, inda aka tattauna tare da amincewa da muhimman ayyuka da manufofi da dama.

Daga cikin ababen da aka amince dasu akai Waɗannan:

An amince da kwangilar gina sabbin gine-ginen ofisoshi na Hukumar Kula da Makarantun Sakandare ta Jihar Adamawa (Post Primary Management Board) kan jimillar kuɗi Naira biliyan 1.752.

An amince da kwangilar gina hanyoyin cikin makaranta, magudanan ruwa, kwalbatoci da sauran ayyukan more rayuwa a Babbar Makarantar Kimiyya da Fasaha (Mega Science and Technical Secondary School) da ke Hong, a Ƙaramar Hukumar Hong, kan kuɗi Naira miliyan 627,695,000.

Domin bunƙasa noma da noman rani, Majalisar ta amince da sayen buhuna 36,300 na takin zamani iri-iri domin noman rani, kan jimillar kuɗi Naira biliyan 2.198.

Haka kuma, Majalisar ta amince da ɗaukar wani kamfanin bada shawara domin gudanar da ayyukan shawarwari kafin da bayan gina Sansanin Yaƙi da Ta’addanci (Counter-Terrorism Base) da ake shirin ginawa a Gulak, Ƙaramar Hukumar Madagali, kan kuɗi Naira 381,655,781.24.

An kuma amince da sayen magungunan kashe ciyawa da kwari domin tallafa wa ayyukan noma a faɗin jihar, kan kuɗi Naira miliyan 759,280,000.

Bugu da ƙari, Majalisar ta tattauna tare da amincewa da takardar Ma’aikatar Albarkatun Ma’adinai ta jihar game da lasisin haƙar ma’adinai.

Waɗannan amincewar suna nuna ci gaba da jajircewar gwamnatin Gwamna Fintiri wajen inganta ababen more rayuwa, ilimi, noma, tsaro da kuma ɓangaren albarkatun ma’adinai, domin tabbatar da ci gaba mai ɗorewa a Jihar Adamawa.

📸 Thomas Terry

📍 Vandi Yusuf Mai Ba Gwamna Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai.

Fassara: Muhammad Mahdi Hamisu

02/09/2026

Wasu Almajiran Shaikh Ibrahim Zakzaky (H) Sun Shirya Ranar (AL-QUR'ANI) Yayin Gabatar da Baƙin Auren su.
02/09/2026

Wasu Almajiran Shaikh Ibrahim Zakzaky (H) Sun Shirya Ranar (AL-QUR'ANI) Yayin Gabatar da Baƙin Auren su.

MUZAHARAR MAULIDIN FIYAYYEN HALITTA ANNABI MUHAMMAD (S.A.W) A GARIN MUBIA ranar talatar da ta gabata ne Ya’uwa musulmi A...
02/09/2026

MUZAHARAR MAULIDIN FIYAYYEN HALITTA ANNABI MUHAMMAD (S.A.W) A GARIN MUBI

A ranar talatar da ta gabata ne Ya’uwa musulmi Almajiran shaikh Ibrahim zakzaky (H) na garin Mubi dake jihar Adamawa, tare da Sauran al’ummar Musulmi masoya Fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad (S.A.W), s**a gudanar da gagarumar Muzaharar Maulidi a garin Mubi, dake Jihar Adamawa.

Muzaharar ta samu halartar dimbin masoya Manzon Allah (S.A.W), inda mahalarta s**a fito cikin farin ciki da nuna matuƙar ƙauna ga Fiyayyen Halitta Annabi Muhammad (S.A.W).

An gudanar da Muzaharar cikin tsari da lumana, yayin da mahalarta ke rera wakoki da taken yabon Manzon Allah (S.A.W), tare da ɗaga sakonni da ke nuna ƙauna, biyayya da kuma girmama matsayin Annabi Muhammad (S.A.W).

Haka kuma, Muzaharar ta kasance wata dama ta tunatar da al’umma muhimmancin koyarwar Manzon Allah (S.A.W), musamman wajen raya kyawawan ɗabi’u, zaman lafiya, haƙuri, tausayi, adalci da kuma ƙarfafa zumunci tsakanin al’umma.

Mahalarta Muzaharar sun bayyana cewa gudanar da irin wannan gagarumin taro wata hanya ce ta nuna farin ciki da murnar zagayowar ranar haihuwar Fiyayyen Halitta, tare da ƙara tunawa da rayuwarsa da kuma koyarwarsa.

An gudanar da taron cikin lumana da kwanciyar hankali, yayin da jama’a s**a gudanar da Muzaharar cikin tsari har zuwa ƙarshenta.

Muna roƙon Allah Madaukakin Sarki Ya ƙara tabbatar da ƙaunar Annabi Muhammad (S.A.W) a cikin zukatanmu, Ya kuma ba mu ikon koyi da kyawawan halayensa da bin koyarwarsa.

Allah Ya ƙara salati da aminci ga Fiyayyen Halitta Annabi Muhammad (S.A.W), da Alayensa Tsarkaka da Sahabbansa na gari.

01-09-2026
✍️ Adamawa Press Team services

Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gabatar da jawabin Mauludi tare da rufe taron Makon Haɗin Kai ga ɗimbin mahalarta ...
31/08/2026

Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gabatar da jawabin Mauludi tare da rufe taron Makon Haɗin Kai ga ɗimbin mahalarta daga sassa daban-daban na al’ummar Musulmi, a Abuja.

📷 Sayyid Ibraheem Zakzaky Office

Gwamna Fintiri ya gana da dukkan Sarakunan Adamawa da Hakimai a ɗakin taro na Majalisar Gwamnati dake Fadar Gwamnati.
31/08/2026

Gwamna Fintiri ya gana da dukkan Sarakunan Adamawa da Hakimai a ɗakin taro na Majalisar Gwamnati dake Fadar Gwamnati.

LABBAIKA YA RASULALLAH (S.A.W) GANGAMIN RANAR JUMA’A DAGA GARIN NUMANYan’uwa Musulmai Almajiran Sheikh Ibrahim al-Zakzak...
28/08/2026

LABBAIKA YA RASULALLAH (S.A.W)

GANGAMIN RANAR JUMA’A DAGA GARIN NUMAN

Yan’uwa Musulmai Almajiran Sheikh Ibrahim al-Zakzaky (H) na Garin Numan sun gudanar da gangamin ranar Juma'a wanda s**a saba gudanarwa duk ranar Juma'a domin nuna goyon bayansu ga al'ummar Palestine da kuma ƙasar Iran.

Kamar yadda s**a saba a kowane mako yau ma sun fito domin bayyana matsayinsu na goyon baya ga waɗanda suke fuskantar ƙalubale da zalunci tare da yin addu'a ga Allah Ya kawo zaman lafiya da nasara.

Allah Ya kare al'ummar Palestine da Iran Ya taimaki dukkan waɗanda ake zalunta a duniya. 🤲??



'a

.B NMN.✍️✓✓✓✓

©Adamawa press team

27/08/2026

TAFSEER MAJLIS

| Tafsirin Alqur’ani mai girma Tare da Hujjatul Islam, Shaikh Muhammad Gidado Hamman Yola, Daga Masallacin Jumma'a Na Nassarawo, Jimeta Yola, Adamawa State.

Alhamis
(27/08/2026)



©️ Adamawa Press Team Services

Address

Kaduna Street Nepa
Yola
6001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Adamawa Press Team posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Adamawa Press Team:

Shortcuts

Share