Halim Tv Hausa

Halim Tv Hausa Halim Media and Broadcasting Service.

Kungiyar manoman asali  ta Arewa, ta koka da yadda ake fifita kayan hatsi na Kasashen ketare a maimakon na gida tare da ...
29/09/2025

Kungiyar manoman asali ta Arewa, ta koka da yadda ake fifita kayan hatsi na Kasashen ketare a maimakon na gida tare da yin Kiran yi wa tubkar hanci don maido da martabar noma a Najeriya.

Kungiyar manoman asali ta Arewa (Arewa Grassroots Famers Alliance of Nigeria) ta bukaci gwamnatin tarayya da ta fifita sayen hatsi na gida a maimakon wadanda ake shigowa da su daga kasashen waje.

Kantoman riko na kungiyar, Comrade Dauda Musa Namadi, ya yi wannan Kiran a lokacin wani taron da kungiyar ta shirya a karamar hukumar Makarfi ta jihar Kaduna.

Comrade Dauda, ya ce, kamata ya yi Gwamnati ta fifita sayen hatsi na gida don kara inganta samarwa da bunkasa tattalin arziki manoma.

" Gwamnati za ta tabbatar da wadatar abinci ga jama'a ne muddin ta bunkasa amfani da hatsin cikin gida da rage yawan dogaro da kayayyakin da ake shigowa da su daga waje" ---- a cewar shugaban kungiyar manoman.

Kwamrade Dauda ya jaddada cewar Gwamnati, ya kyautatu ta rika sayen amfanin gona da manoman ainihi na gida ke Samarwa ta karyar dasu a farashi mai sauki don saidawa jama'a ko kamfanoni, in kuma ba ta iya sayen kayayyakin amfanin gona da manoman asali Ke nomawa don tallafawa manoman da suke kashe makudan kudade wajen harkokin noman, to ta daina barin ana shigo dana Kasashen ketare, don kayayyakin cikin gida su yi gogayya da sauran kayan hatsi na Kasashen waje.

Shugaban kungiyar manoman Comrade Dauda, ya Kara da cewa duk da muhimmancin Noma ga cigaban Kasa, manoman kasarnan da dama na fuskantar ƙalubale tun daga Kan rashin tsaro da rashin fifita abun da suke nomawa, wanda hakan ya Zama barazana ga harkokin noman manoman dake taimakawa wajen samar da abinci mai tarin yawa ga alummar Najeriya don haka ba za su lamunci wannan lamarin ba, sai ya yi Kira ga gwamnatin ta dauki kwararan matakan dakile haka Ko su Shiga yajin aiki.

Wasu daga cikin manoman kungiyar Ashiru Tanko Makarfi da Alhaji Shehu Ibrahim da sauran manoman da s**a halarci taron da s**a tofa albarkacin bakinsu, sun nuna rashin jindadinsu da Yadda ba a la'akari da wahalhalun da suke fuskanta na noma sai rika tsallakewa ana shigowa da wasu Kayan hatsi daga waje, daga nan sai s**a bukaci masu ruwa da tsaki su yi wa tubkar hanci.

Kungiyar manoman ta ce za ta cigaba da yin irin wadannan kiraye kirayen har sai gwamnati ta shawo Kan lamarin dake Neman fin karfin kundila.

ATLETICO TA YIWA REAL MADRID BUGUN BARAWON AGWAGWA DA CI 5-2..Kungiyar Kwallon Kafa ta Atletico Madrid ta yiwa Abokiyar ...
27/09/2025

ATLETICO TA YIWA REAL MADRID BUGUN BARAWON AGWAGWA DA CI 5-2..

Kungiyar Kwallon Kafa ta Atletico Madrid ta yiwa Abokiyar derby dinta ta Real Madrid Bugun Barawon Agwagwa da ci Biyar da biyu a Karawarsu a Gasar Laliga na wannan Makon da ya gudana a Gidan Atletico dake Spain.

Wannan Mummunar Dukkan da Atletico ta yiwa Real Madrid ta sanya Kulob din Madrid ya rikito daga matsayi na daya a gasar ta laliga.

Mai Za ku ce akan wannan Wasan?

DA DUMI-DUMINSA: An Wulakanta Netanyawu a Majalisar Dinkin Duniya..A wani Abu da ake ganin Tozarcine ga Shugaban Kasar I...
26/09/2025

DA DUMI-DUMINSA: An Wulakanta Netanyawu a Majalisar Dinkin Duniya..

A wani Abu da ake ganin Tozarcine ga Shugaban Kasar Isra'ila Benjamin Netanyawu,Shugabanni Kasashen duniya da wasu daga cikin Wakilan Kasashen Duniya sun Fice daga Dakin Taron Majalisar Dinkin Duniyar a daidai Lokacin da Shugaban Kasar Isra'ila Netanyawu zai fara Jawabi.

Wannan Matakin na matsayin nuna Fushi da bacin Rai ga Netanyawu da Kasarsa ta Isra'ila bisa Kisan Kiyashi da Cin Zarafin da suke yi a yankin Gaza ta kasar Falasɗinu.

Me za ku ce..

Yan Izala basu damu da Manzon Allah S.A.W ba...In Ji Sheikh Aliyu Dahiru Aliyu Ku ne Annabi (saw) ya dameku da har idan ...
26/09/2025

Yan Izala basu damu da Manzon Allah S.A.W ba...In Ji Sheikh Aliyu Dahiru Aliyu

Ku ne Annabi (saw) ya dameku da har idan an gaya masa magana hankalinku yake tashi. Wallahi ko ashariya aka durawa Annabi sai mutanen nan sun kareta matukar nasu ne ya yi. Hasalima a lokacin ne za a dinga kai masa mubayi'a ana cewa dodon bidi'a ne.

Idan kana son ka ga fushinsu ka ce akwai sahabbai yan wuta ko ka ce Bukhari ya yi karya. Su ma sahabban kada ka dauka damunsu s**a yi, kawai saboda wasunsu sun kashe jikokin Annabi (saw) ne. Su duk abin da zai batawa Annabi rai shi ne cikar sunnah a gurinsu, kuma Muawiyah ne ya koya haka.

Innalillahi wa inna Ilaihin Rajiun..Mun Samu Labarin Rasuwar Alaramma Abubakar Garba Surumbai. Matashin Mahaddacin Alkur...
25/09/2025

Innalillahi wa inna Ilaihin Rajiun..

Mun Samu Labarin Rasuwar Alaramma Abubakar Garba Surumbai. Matashin Mahaddacin Alkur'ani sannan Mashahurin Masoyin Manzon Allah S.A.W, Sannan ɗa ga Fitaccen Malamin Addinin Musuluncin nan dake Tudun Wada Zaria Marigayi Sheikh Abubakar Umar Inyass.

Ya Rasu bayan wata Gajeruwar Rashin Lafiya. Kanine ga Fitaccen Matashin dan Siyasar nan dake Zaria wato Mal Ibrahim Garba Umar (Inyass).

A madadin Ma'aikatan Gidan Jaridar Halim Tv Hausa muna mika dakon ta'aziyya ga Yan uwa da Abokan Arziki da Makusantan Mamacin. Allah ya karbi Bakuncinsa,ya Sada shi da Masoyinsa Manzon Allah S.A.W.

Jami'an Tsaron DSS sun yiwa Sheikh Lawal Triump Tabarma a Kano...
25/09/2025

Jami'an Tsaron DSS sun yiwa Sheikh Lawal Triump Tabarma a Kano...

CIKIN HOTUNA; Yanda Kanawa s**a Gudanar da Jana'izar Kare Wizzy a Karamar Hukumar Kabo dake Jihar Kano.Mai Za ku ce?.
25/09/2025

CIKIN HOTUNA; Yanda Kanawa s**a Gudanar da Jana'izar Kare Wizzy a Karamar Hukumar Kabo dake Jihar Kano.

Mai Za ku ce?.

ELON MUSK; Sai ka yi Shekaru Dubu Biyar kafin ka iya Tara Adadin Dukiyarsa.. Adadin dukiyar Fitaccen Attajirin nan na du...
24/09/2025

ELON MUSK; Sai ka yi Shekaru Dubu Biyar kafin ka iya Tara Adadin Dukiyarsa..

Adadin dukiyar Fitaccen Attajirin nan na duniya ya kai kimanin Dala 463 Billion(Dala Biliyon Dari Hudu da Sittin da Uku). Daidai da zunzurutun kuɗi Kimamin Naira Triliyon 689.(Triliyon Dari Shida da Tamanin da Tara)

A kiyasi sai Ka yi Shekaru Dubu Biyar kullum kana samun Naira Miliyan 377 kafin ka kamo Elon Musk kudi.

Allah kai mana Arziki.

Majalisar Mahaddata Alkur'ani Ta Karyata Nada Ganduje A Matsayin Khadimul Qur’an.Cibiyar Karatun Alkur’ani ta Najeriya (...
24/09/2025

Majalisar Mahaddata Alkur'ani Ta Karyata Nada Ganduje A Matsayin Khadimul Qur’an.

Cibiyar Karatun Alkur’ani ta Najeriya (CQRN) ta yi kakkausar s**a ga wani nadi da aka ce an yi da sunan majalisar inda ta ba tsohon gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje lakabin Khadimul Qur’an.

A wata sanarwa da ya fitar daga hedikwatarta ta kasa da ke Kano, shugaban majalisar na kasa, Goni Sunusi Abubakar, ya ce shugabanni da mambobin kungiyar ba su da masaniya kan wannan Shirme , kuma ba su taba bayar da izinin yin wannan nadin ba.

A cewarsa, kungiyar da ta gabatar da kanta a matsayin gamayyar masu karatun Alkur’ani ta hanyar damfara tayi amfani da hatimin wasikun cibiyar wajen sanar da nadin Ganduje.

Ya bayyana hakan a matsayin sabawa doka da kuma yaudara, yana mai jaddada cewa kungiyar ba ta da wata masaniya a matsayinta na ingantacciyar kungiyar masu karatun kur’ani ta kasa.

“Mun nesanta kanmu a wannan aiki, ni matsayina na Shugaba,ko kwamitin amintattu,bamu da wata alaka da wannan nadin, karya ce aka yi ba tare da yardarmu ba,”

Jami’an cibiyar sun yi gargadin cewa ayyukan kungiyar an tsara su ne domin haifar da hadin kai a tsakanin masu karatun kur’ani da malaman addinin musulunci a fadin kasar.

Sanarwar ta bukaci musulmi, masu karatun kur’ani, malaman addinin Islama, da kuma masoyan kur’ani da su yi watsi da wannan da’awar, kuma kada su danganta wannan haramtaccen aiki da cibiyar da aka sani na masu karatun kur’ani ta Najeriya.

Daga
Saifullahi Lawal Imam.

Wata Daliba daga Jami'ar A.B.U Dauke da maciji akanta,a yayin Bikin Nuna Al'adun gargajiya da aka gudanar a Jami'ar ciki...
20/08/2025

Wata Daliba daga Jami'ar A.B.U Dauke da maciji akanta,a yayin Bikin Nuna Al'adun gargajiya da aka gudanar a Jami'ar cikin Makon Nan.

wane Fata za ku mata?.

Innalillahi wa inna Ilaihin Rajiun.A Ceto Gaza😭😭🤲🤲
20/07/2025

Innalillahi wa inna Ilaihin Rajiun.

A Ceto Gaza😭😭🤲🤲

Nayi Karatun dayakai Matakin Degree amma Hakan Bai Hanani nayi Dakoba don neman Nakaina nasayar da shayi don neman nakai...
19/07/2025

Nayi Karatun dayakai Matakin Degree amma Hakan Bai Hanani nayi
Dakoba don neman Nakaina
nasayar da shayi don neman nakaina
Inayin Noma sabida nakare mutuncina
Ayanzu Haka Gurasa nake Soyawa Nadauka Natafi Tallenta Ahakan Nake Kare Mutumcin Kaina
Dan Uwa Kazama Jarumi ka kula da kanka sai ka Tunkari Adawa

In ji Itas.

Address

Zaria

Telephone

+2349034804338

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Halim Tv Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share