ZAGE- ZAGI A YAU.

ZAGE- ZAGI A YAU. Press Historical

06/09/2019

WAKAR DA MARIGAYI IBRAHIM NARAMBADA YA REREMA MARIGAYI SARKIN ZAZZAU MALAM JA'AFARU DAN'ISYAKU.

Jigo: Ai tafi Jekadiya
fado mashi bakonka ya zaka

Amshi: Ba taura bana Narambada Malamin kiddini, In ya ce maraba mun yi kidi Za mu Kwan bakwai, Dan Isyaku makaye Ja'afaru mai halin mazan jiya Zamna da lahiya.

Jgo: Ja'afaru Sarkin rikon amana ne baya walwalewa

Amshi: Sai ka walwale da kanka Yakan walwalewa Dan Isiyaku makaye, Ja'afaru mai halin mazan jiya Zamna da lahiya.

Jigo: Sarkin Gobir na Isa Ahmadu shi yak Kira ni, naji jawabin da yai mani, Ban zauna ba na shigo jirgi, sai fadin nikai jirgi Kai ni Zariya kai dai kai mu Zariya, Kai dai Kai mu lahiya Bisa yardan ubangiji,

Amshi: In mun shida mun ga Ja'afaru mun debe alkawal, Dan Isyaku makaye, Ja'afaru mai halin mazan jiya, Zamna da lahiya.

Jigo: Baban Jekadiya

Amshi: Ruwa da yawa maganin fari

Jigo: Tun ban zo nan ba naji labarin Abdu ya yi Sarki

Amshi: Ya kyauta duniya ×2

Jigo: Har Yero na ji yai Sarauta

Amshi: Ya kyauta duniya,

Jigo: Sarkin Yaki yai Sarauta

Amshi: Ya kyauta duniya

Jigo: Ibrahimu yai Sarauta

Amshi: Ya kyauta duniya,

Jigo: Ja'afaru Kai ag-gidanga, Kai ab babbansu kafi kowa,

Amshi: Wadda nit-taho kamar dai Yamusa ni ishe,
Dan Isiyaku makaye, Ja'afaru mai halin mazan jiya Zamna da lahiya

Jigo Baban Jekadiya

Amshi Ruwa da yawa maganin fari
Dan Isiyaku makaye, Ja'afaru mai halin mazan jiya Zamna da lahiya.

Jigo: Ai wata rana a sha Zuma wata rana a sha madaci, haka duniya take, yau in an ga an ci riba

Amshi Gaba faduwa akai Dan Isiyaku makaye Ja'afaru mai halin mazan jiya Zamna da lahiya

Jigo: Baban Jekadiya,

Amshi: Ruwa da yawa maganin fari ×2

Jigo: Kowai ce ya gane mu Zariya dominka yag-gamu

Amshi: In ba kai ba babu mai iya kawo mu Zariya ×2 Dan Isiyaku makaye Ja'afaru mai halin mazan jiya Zamna lahiya.

Jigo: Baban Jekadiya,

Amshi: Ruwa da yawa maganin fari ×2 Dan Isiyaku makaye Ja'afaru mai halin mazan jiya Zamna da lahiya

Kawowa Abdullahi Musa Badayi.

04/09/2019
02/09/2019

MALLAM ABBAS MUHAMMAD FAGACHI SARKIN AYYUKAN ZAZZAU:

Fagachi ya na cikin 'ya'yayen da Lardin Zazzau yake alfàhari dasu, kasancewarshi marubuci Kuma mai hazaka ya ba Lardin Zazzau gagarumar gudunmuwa a fagen tsare mutuncin tarihinta dana shugabaninta.

Fagachi ya dauki tsawon lokaci ya na nazari akan tarihin Mai martaba Sarkin Zazzau Alhaji Dr. Shehu Idris. Fagachi ya wallafa wani kasaitaccen litafi akan tarihin mai martaba Sarkin Zazzau. Wannan kasaitaccen littafin ya kunshi shafuka har (267).

A cikin wannan gagarumin aikin da Fagachi ya yi har ya yi kokarin rubutu manyan unguwan dake cikin birnin Zaria.

Garemu marubuta Fagachi ba karamin mutun bane kuma ba karamar gudunmuwa yaba wannan Lardin namu na Zazzau ba.

Dan hakanema nayi kokarin kawo kadan daga cikin tarihin yaruwan wannan jigo a fagen rubuce-rubuce.

An haifi Fagachi a garin Makarfi a shekarar 1966, a dai-dai lokacin Mahaifinsa Alhaji Muhammadu Fagachi Kuma Fagachin Zazzau, shi ke rike da sarautar hakimin Makarfi.

Fagachi ya fara karatunsa na Islama a makarantar Malam Abdu Mahaddaci da ke Makarfi.

Bayan ya yi nisa da karatu sai aka sanya shi a makarantar firamari a can garin Makarfi cikin shekarar 1973-1978. A shekarar ne Mahaifinsa ya yi ritaya daga aikin hakimci, ya dawo gida Zaria, inda aka sanya Fagachi a makarantar firamari ta Anguwar Kahu, a shekarar 1979.

Kuma a shekarar ya kare karatunsa na firamari daga nan ya sami shiga Makarantar Sakandare ta Dutsenma (GSS Dutsenma).

Daga nan Kuma ya koma makarantar Sakandare ta Alhudahuda, dake Zaria cikin shekarar 1979-1984, daga nan ya wuce jami'ar Ahmadu Bello, cibiyan nazarin koyon aikin mulki dake Congo (Department of Local Studies), daga shekarar 1984-1986.

Ya fara aiki da kamfanin sayar da kayan gona na (FASCOM) a matsayin mataimakin akawun ciniki (Commercial Assistance), daga shekarar 1986-1991.

Daga nan ya canza aiki zuwa kotun Daukaka Kara ta tarayya (federal Court of Appeal), reahen Jihar Kaduna daga shekarar 1990-1996 in da daga nan ya ajiye aiki don kashen kansa.

Fagachi ya halarci kos a kan kasuwanci a makarantar kimiya da fasaha ta Nuhu Bamalli da ke Zaria a shekarar 1991-1992. Ya Kuma yi Kos akan harshen larabci a FCE Zaria daga shekarar 2001-2002.

Ya sake Kos akan harshen larabci Kashi na daya dana biyu a kwalejin Sheik Abubakar Gumi dake Zaria a shekarar 2004.

Ya yi karatun lauya a jami'ar Ahmadu Bello, Fagachi nada iyalai da yara muna mushi fatan Alheri.

Rubutawa Abdullahi Musa Badayi

01/09/2019

JIYA BA YAU BA.

A hannun dama. Marigayi. FAGACHIN ZAZZAU. Alh Nuhu Muhammad.
A kusada dashi. MAKAMAN ZAZZAU.
Alh. Umaru Mijinyawa.
Na ukunsu. GALADIMAN ZAZZAU
Alh. Nuhu Aliyu Magaji.
Na hudunsu. Marigayi MADAKIN ZAZZAU. Alh. Aliyu Shehu Idris.

A dauki wannan photon ne a fadan mai martaba SARKIN ZAZZAU.

Ranar #26/08/1998.
Allah kajikan bayin Allah da rahama.

Address

No. 15 Anguwan Katuka, Kwarbai Zaria City
Zaria
YUSUF3461

Telephone

09038232070

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ZAGE- ZAGI A YAU. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category