DOVE NEWS HAUSA

DOVE NEWS HAUSA Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from DOVE NEWS HAUSA, Media/News Company, Zaria.

Barka da zuwa shafin Jaridar DOVE NEWS HAUSA gidan jarida Mai Zaman Kanshi Dake Kawo Muku Ingantattun Labarai Cikin Harshen Hausa

kana Son Bamu Labari Ko Faɗan Ra'ayin Ka Yi Mana Magana Ta Whatsapp 09131293900 Yanzu

Sheikh Halliru Maraya ya bayyana cewa Annabi Muhammad (S.A.W) shi ne ya fara nuna murnar ranar haihuwarsa, don haka Maul...
03/09/2025

Sheikh Halliru Maraya ya bayyana cewa Annabi Muhammad (S.A.W) shi ne ya fara nuna murnar ranar haihuwarsa, don haka Maulidi ba bidi’a ba ce. Annabi ya yi nuni da cewa ranar Litinin ce aka haife shi, shi ya sa ake yin azumi a wannan rana.

A lokacin Maulidi, ya k**ata a gudanar da ayyuka masu amfani k**ar:

1. Taron yin koyi da halayen Annabi,

2. Yin azumi,

3. Ƙarfafa zumunci,

4. Ziyartar marasa lafiya,

5. Taimakon al’umma.

Sai dai kuma bai yarda da abubuwan da ba su da amfani ba irin su:

Cakuɗuwar maza da mata,

Yin ihuce-ihuce,

Sha da kuma shagulgulan banza.

Sheikh ya ƙara da cewa watan Rabi’ul Awwal wata ne mai muhimmanci ga Musulmi saboda shi ne watan da aka haifi Annabi Muhammad (S.A.W).

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Wani matashi mai suna Freeman Ishaku, wanda Kirista ne, ya shiga aikin gyaran makabartan Musulmi a garin Gombi na jihar ...
03/09/2025

Wani matashi mai suna Freeman Ishaku, wanda Kirista ne, ya shiga aikin gyaran makabartan Musulmi a garin Gombi na jihar Adamawa.

Wani mazaunin yankin Ya shaidawa wakilin Dove News Hausa cewa irin wannan haɗin kai ne ya dace a ƙara inganta shi domin bunƙasa zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban a Najeriya.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Juma’a, 5 ga watan Satumba, 2025 a matsayin ranar hutun aiki don bikin tunawa da haihu...
03/09/2025

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Juma’a, 5 ga watan Satumba, 2025 a matsayin ranar hutun aiki don bikin tunawa da haihuwar Annabi Muhammad (SAW).

Dove news Hausa ta ruwaito cewa Ministan Harkokin Cikin Gida, Tunji Ojo, ne ya sanar da hakan a wata takarda da ma’aikatarsa ta fitar a yau, inda ya ce hutun ya biyo bayan bukin Maulidin Annabi ﷺ da Musulmi ke gudanarwa a faɗin duniya.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Bauchi, Hon. Aliyu Aminu Garu, ya bayar da tallafin naira miliyan goma (₦10m)...
03/09/2025

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Bauchi, Hon. Aliyu Aminu Garu, ya bayar da tallafin naira miliyan goma (₦10m) tare da kayan abinci ga al’ummar da ke gudanar da bikin Maulidin Annabi ﷺ a jihar Bauchi.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Shugaban mulkin sojin Jamhuriyar Nijar, Janar Abdourahamane Tchiani, ya nuna ƙaunar sa ga masana’antar fina-finan Hausa ...
02/09/2025

Shugaban mulkin sojin Jamhuriyar Nijar, Janar Abdourahamane Tchiani, ya nuna ƙaunar sa ga masana’antar fina-finan Hausa ta Kannywood, inda ya tallafa wa ɗaya daga cikin fitattun jarumai, Malam Na Tala’ala, wanda yake kwance a gadon asibiti.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

A jiya Litinin, babban birnin ƙasar Ethiopia, Addis Ababa, ya cika da taron dubunnan al'ummar musulmi da s**a fito daga ...
02/09/2025

A jiya Litinin, babban birnin ƙasar Ethiopia, Addis Ababa, ya cika da taron dubunnan al'ummar musulmi da s**a fito daga sassa daban-daban domin murnar zagayowar haihuwar Manzon Allah, Annabi Muhammad ﷺ.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda, ya jagoranci wata tawaga ta manyan jami’an jihar zuwa fadar shugaban ƙasa domin...
02/09/2025

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda, ya jagoranci wata tawaga ta manyan jami’an jihar zuwa fadar shugaban ƙasa domin tattaunawa da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan matsalar tsaro da ta addabi jihar.

A yayin zaman, Shugaba Tinubu ya tabbatar da cewa gwamnatin sa za ta sauya salo a yaƙin da ake yi da ’yan bindiga, musamman ta hanyar amfani da jiragen sama marasa matuƙi (drones) domin kai farmaki a dukkanin yankunan jihar Katsina.

Kazalika, shugaban ƙasar ya umarci manyan hafsoshin tsaron ƙasa da su gyara damarar su tare da ƙirƙirar sabbin dabaru wajen yakar matsalar ’yan bindiga, domin tabbatar da cewa jihar Katsina ta samu zaman lafiya.

Shugaba Tinubu ya tabbatar wa Gwamna Radda da tawagarsa cewa, daga yanzu zuwa duk lokacin da ya dace, salon yaƙi da ’yan bindiga a Katsina zai canza domin tabbatar da nasara a fagen tsaro.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Fitaccen malamin addini, Sheikh Ishaq Adam Ishaq, ya bayyana adawarsa ga yadda wasu malamai ke ta kira da ake yi na haɗa...
02/09/2025

Fitaccen malamin addini, Sheikh Ishaq Adam Ishaq, ya bayyana adawarsa ga yadda wasu malamai ke ta kira da ake yi na haɗa kan malaman Musulunci, musamman a fagen da ya shafi akida.

A cewar Sheikh Ishaq, haɗa kai a lamuran da za su kawo sauyi da ci gaban al’umma abin so ne, amma bai k**ata a yi amfani da akida wajen matsa wa mutane lamba ba.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Hukumar tsaro ta Civil Defence reshen jihar Gombe ta k**a wani mutum mai suna Ibrahim Haruna, mai shekaru 48, tare da ɗa...
02/09/2025

Hukumar tsaro ta Civil Defence reshen jihar Gombe ta k**a wani mutum mai suna Ibrahim Haruna, mai shekaru 48, tare da ɗansa Abdullahi Ibrahim mai shekaru 15, bisa zargin yi wa wata yarinya ƴar shekara 13 fyade.

Wani jami’in NSCDC ya tabbatar da Dove News Hausa cewa an cafke su ne a unguwar Jekadafari da ke cikin karamar hukumar Gombe, inda ake zargin sun aikata laifin.

A cewar hukumar, an k**a su ne a ranar Litinin a hedikwatar rundunar, kuma tuni bincike ya fara kan lamarin.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Shahararren attajiri na Najeriya, Alhaji Aliko Dangote, ya bayyana cewa dukiyar da yake da ita a yau ba ta fito daga mah...
02/09/2025

Shahararren attajiri na Najeriya, Alhaji Aliko Dangote, ya bayyana cewa dukiyar da yake da ita a yau ba ta fito daga mahaifinsa ba, shi da kansa ya gina ta daga tushe.

Dangote ya ce abin da ya samu daga iyayensa bai yi amfani da shi wajen kafa kasuwancinsa ba, domin tun farko duk abin da aka bashi gudunmawa ce kawai.

Ya kuma ƙara da cewa ya fara harkar kasuwanci ne da saye da sayar da siminti, kafin daga baya ya faɗaɗa jarinsa har ya zama ɗaya daga cikin manyan attajirai a duniya.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

DA DUMI DUMI: Zamu hukunta Nasiru El-rufa'i. Domin ba zamu taɓa lamuntar ya lalata mana zaman lafiyar jihar Kaduna da ka...
02/09/2025

DA DUMI DUMI: Zamu hukunta Nasiru El-rufa'i. Domin ba zamu taɓa lamuntar ya lalata mana zaman lafiyar jihar Kaduna da kalaman karya ba -Gwamna Uba sani.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Gwamnatin Burkina Faso ta fitar da sabuwar doka da ta haramta aikata luwaɗi, tare da tanadar da hukuncin ɗaurin shekaru ...
02/09/2025

Gwamnatin Burkina Faso ta fitar da sabuwar doka da ta haramta aikata luwaɗi, tare da tanadar da hukuncin ɗaurin shekaru biyu zuwa biyar da kuma tara ga duk wanda aka k**a da laifin.

Majalisar dokokin gwamnatin riƙon ƙwarya ta ƙasar ce ta amince da wannan doka a zaman da ta gudanar, inda dukkan ’yan majalisar 71 s**a kada kuri’ar amincewa da sabuntawar dokar.

Ministan Shari’a na ƙasar, Edasso Rodrigue Bayala, ya bayyana matakin a cikin jawabi da ya yi a gidan talabijin na ƙasar, RTB, a ranar Litinin.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Address

Zaria

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DOVE NEWS HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share