13/06/2026
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana matuƙar alhini da kaɗuwa kan rasuwar tsohon Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, wanda ya rasu yayin da yake tsare a hannun masu garkuwa da mutane.
Tinubu ya yi Allah-wadai da wannan mummunan lamari, yana mai cewa mutuwar tsohon hafsan sojin babban rashi ne ba ga iyalansa kaɗai ba, har ma ga rundunar sojin Najeriya da ƙasa baki ɗaya.
Shugaban ƙasar ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta nuna wa 'yan bindiga da masu garkuwa da mutane wani sassauci ba, yana mai tabbatar da cewa hukumomin tsaro za su ci gaba da bibiyar duk masu hannu a wannan aika-aika domin su fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.
Ya kuma miƙa saƙon ta'aziyyarsa ga iyalan marigayin, gwamnatin Jihar Katsina, rundunar sojin Najeriya da daukacin al'ummar ƙasar, tare da addu'ar Allah Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya jikansa da rahama, Ya ba iyalansa da waɗanda ya bari haƙurin jure wannan babban rashi.
Shigo shafin 👉 DOVE NEWS HAUSA don samun Ingantattun Labarai a koda yaushe.