DOVE NEWS HAUSA

DOVE NEWS HAUSA Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from DOVE NEWS HAUSA, Media/News Company, Zaria.

Barka da zuwa shafin Jaridar DOVE NEWS HAUSA gidan jarida Mai Zaman Kanshi Dake Kawo Muku Ingantattun Labarai Cikin Harshen Hausa

kana Son Bamu Labari Ko Faɗan Ra'ayin Ka Yi Mana Magana Ta Whatsapp 09131293900 Yanzu

Mataimakin shugaban ƙasar Venezuela ya bayyana cewa jami’an tsaron ƙasar sun cafke wasu ‘yan ta’adda da ake zargin suna ...
27/10/2025

Mataimakin shugaban ƙasar Venezuela ya bayyana cewa jami’an tsaron ƙasar sun cafke wasu ‘yan ta’adda da ake zargin suna samun goyon bayan hukumar leken asirin Amurka (CIA).

Dove News Hausa cewa an k**a ƴan ta'addan ne yayin da suke shirin kaddamar da hare-hare a cikin ƙasar, kafin barkewar rikicin da ake hasashen zai iya ɓarke tsakanin Amurka da Venezuela a yankin Caribbean Peninsula.

Gwamnatin Venezuela ta ce wannan mataki wani ɓangare ne na ƙoƙarinta na kare ƙasar daga duk wani yunkurin waje da ke nufin tayar da zaune tsaye ko kawo cikas ga tsaron ƙasa.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Sarkin Jordan, Abdullah II, ya gabatar da jawabi a ranar Lahadi yayin buɗe zama na biyu na majalisar dokoki ta 20 ta ƙas...
27/10/2025

Sarkin Jordan, Abdullah II, ya gabatar da jawabi a ranar Lahadi yayin buɗe zama na biyu na majalisar dokoki ta 20 ta ƙasar.

A cikin jawabin nasa, Sarkin ya jaddada matsayar Jordan na adawa da cin zarafin da Isra’ila ke yi a yankin Yammacin Kogin Jordan da ta mamaye, tare da tabbatar da cewa masarautar Jordan za ta ci gaba da mara baya ga al’ummar Falasɗinu wajen kare hakkokinsu da neman ‘yancin kai.

Sarauniya Rania, Yarima mai jiran gado Hussein, Sarauniya Rajwa da Sarauniya Salma duk sun halarci zaman majalisar.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Iran mai kula da Harkokin Shari’a da Ƙasashen Duniya, Kazem Gharibabad, ya bayyana ce...
27/10/2025

Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Iran mai kula da Harkokin Shari’a da Ƙasashen Duniya, Kazem Gharibabad, ya bayyana cewa ziyararsa zuwa ƙasar Afghanistan na da nufin tattauna muhimman batutuwa da s**a shafi hulɗar ƙasashen biyu.

Dove News Hausa ta ruwaito cewa Kazem Gharibabad ya ce tattaunawar ta shafi haɗin gwiwar tsaro a kan iyaka, rabon ruwa daga koguna da tafkuna da ke tsakanin ƙasashen biyu, da kuma lamuran shari’a da diflomasiyya.

Ya kuma bayyana cewa Iran tana fatan wannan ziyarar za ta zama wata hanya ta ƙarfafa zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin ƙasashen biyu, musamman ganin yadda rikice-rikicen siyasa da matsalolin tsaro ke da tasiri ga yankin.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Rundunar sojin Isra’ila ta tabbatar da cewa sojojinta goma sha biyu (12) sun ji rauni a haɗarin mota da ya faru a kan iy...
27/10/2025

Rundunar sojin Isra’ila ta tabbatar da cewa sojojinta goma sha biyu (12) sun ji rauni a haɗarin mota da ya faru a kan iyakar Gaza a jiya Lahadi.

An ce dukkansu an garzaya da su asibiti domin karɓar kulawa, kuma wasu daga cikinsu na cikin mummunan yanayi

Rundunar ba ta bayyana cikakkun bayanai kan yadda haɗarin ya faru ba, sai dai ta ce an fara bincike kan lamarin.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kebbe/Tambuwal ta jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki, ya bayyana cewa ba zai sak...
26/10/2025

Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kebbe/Tambuwal ta jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki, ya bayyana cewa ba zai sake neman takara a zaɓen 2027 ba, yana mai cewa lokaci ya yi da matasa za su karɓi ragamar shugabanci.

Dove News Hausa ta ruwaito cewa a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi,Abdussamad Dasuki ya ce matakin nasa wata sadaukarwa ce domin ƙarfafa dimokuraɗiyya da kuma buɗe ƙofa ga matasa su shiga siyasa cikin ƙwarin gwiwa.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉
DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Shugaban Hukumar Tsaron Cikin Gida ta Iran, Birgediya Janar Gholamreza Jalali, ya bayyana cewa gine-ginen mak**ai na ƙas...
26/10/2025

Shugaban Hukumar Tsaron Cikin Gida ta Iran, Birgediya Janar Gholamreza Jalali, ya bayyana cewa gine-ginen mak**ai na ƙasa da ƙasa (underground military facilities) da ƙasar ke da su, sun nuna irin nasarar da Iran ta samu wajen kare kanta daga barazanar abokan gaba.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Za a Bai wa Manyan Sojojin da Tinubu Ya Tsige Sabbin Motoci Masu Silke da masu Tsaron Lafiyar su Gwamnatin Tarayyar Naje...
26/10/2025

Za a Bai wa Manyan Sojojin da Tinubu Ya Tsige Sabbin Motoci Masu Silke da masu Tsaron Lafiyar su

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta amince da bai wa manyan hafsoshin tsaron da aka tsige kwanan nan sabbin motoci masu silke tare da ƙarin jami’an tsaro da masu yi musu hidima a gida.

Hafsoshin da abin ya shafa sun haɗa da tsohon Shugaban Hafsan Sojin Ƙasa, Janar Christopher Musa; tsohon Shugaban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Hasan Abubakar; da kuma tsohon Shugaban Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ogalla.

Wannan na cikin sabbin ƙa’idojin barin aikin soja da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya wa hannu a ranar 14 ga Disamba, 2024.

A ranar Juma’a da ta gabata ne gwamnatin tarayya ta sanar da tsige waɗannan hafsoshin tsaron, tare da maye gurbinsu da sabbin shugabanni nan take.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Farfesa Isa Ali Pantami ya bayyana cewa idan mutanen Gombe s**a ba shi dama ya zama gwamna, zai gudanar da mulki irin na...
26/10/2025

Farfesa Isa Ali Pantami ya bayyana cewa idan mutanen Gombe s**a ba shi dama ya zama gwamna, zai gudanar da mulki irin na tsohon shugaban ƙasa, marigayi Muhammadu Buhari.

Dove News Hausa ta ruwaito cewa Pantami ya ce zai yi amfani da salon mulki mai cike da gaskiya, adalci, amana, tausayi, kyautatawa da sadaukarwa, domin kawo cigaba ga jihar Gombe da al’ummarta.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Shahararren mawaki Soja Boy ya bayyana cewa yana da niyyar gina masallaci da makaranta daga kudaden da yake samu ta hany...
25/10/2025

Shahararren mawaki Soja Boy ya bayyana cewa yana da niyyar gina masallaci da makaranta daga kudaden da yake samu ta hanyar wakokinsa, ciki har da waɗanda ake kiran wakokin batsa.

A cewar Soja Boy, zunubin irin waɗannan wakoki daban yake, amma ladar gina masallaci ko makaranta daban take. Ya ce yana da tabbacin cewa mutane ba za su ƙi yin sallah a masallacin da ya gina ba, haka kuma ba za su ƙi yin karatu a makarantar da ya kafa ba.

Mawakin, wanda ya shahara da wakokin soyayya da kuma irin waɗanda ke jawo cece-kuce a shafukan sada zumunta, ya ce burinsa shi ne yin amfani da abin da yake samu wajen aikata alheri.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Manjo Janar Emmanuel Perkar, wanda ya bankado shirin juyin mulki a cikin rundunar sojin Najeriya, shi kaɗai ne daga ciki...
25/10/2025

Manjo Janar Emmanuel Perkar, wanda ya bankado shirin juyin mulki a cikin rundunar sojin Najeriya, shi kaɗai ne daga cikin manyan hafsoshin da kujerarsu ta tsira daga sauyin da aka yi kwanan nan.

Yanzu haka, Janar Perkar yana ci gaba da jagorantar Hukumar Leƙen Asirin Sojin Najeriya (Defence Intelligence Agency – DIA), inda yake kula da harkokin tsaro da tattara bayanai na musamman domin kare muradun ƙasa.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Ziyarar Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Shaida Ce Ta Samuwar Tsaro Da Zaman Lafiya — Ministan Tsaron NijeriyaMinistan Tsaro...
25/10/2025

Ziyarar Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Shaida Ce Ta Samuwar Tsaro Da Zaman Lafiya — Ministan Tsaron Nijeriya

Ministan Tsaron Nijeriya, Dr. Bello Muhammad Matawalle, ya bayyana ziyarar tsoffin ’yan wasan ƙungiyar kwallon ƙafa ta Barcelona zuwa Nijeriya a matsayin tabbacin dawowar zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali a ƙasar.

A wata sanarwa da mataimakinsa na musamman kan yaɗa labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya fitar a Abuja ranar Juma’a, Matawalle ya ce wannan ziyara ta nuna yadda ƙasashen duniya ke sake samun kwarin gwiwa kan ƙoƙarin da gwamnatin Nijeriya ke yi wajen magance matsalolin tsaro.

A cewarsa, zuwan tsoffin ’yan wasan Barcelona hujja ce ta ci gaban da ƙasar ke samu wajen farfaɗo da tsaro da zaman lafiya. Ya ƙara da cewa, hakan na nuna cewa Nijeriya ta zama ƙasa mai jan hankalin duniya sak**akon jajircewar jami’an tsaro da hukumomin gwamnati.

Matawalle ya bayyana wasan sada zumunci da tsoffin ’yan wasan Barcelona za su buga da tsoffin taurarin ’yan wasan Afirka a ranar Asabar, 25 ga Oktoba, 2025, a filin wasa na Moshood Abiola, Abuja, a matsayin nasara ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu wajen tabbatar da zaman lafiya da samar da yanayi mai kyau domin gudanar da wasannin kasa da kasa.

Daga ƙarshe, Ministan ya yi wa tawagar tsoffin ’yan wasan maraba a madadin gwamnatin Nijeriya da al’ummar ƙasa, tare da fatan natsuwa da nishadi a lokacin da za su shafe a Nijeriya.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Zan Kamo Bello Turji Nan Da Lokaci Kaɗan — Cewar Sabon Hafsan Sojin NajeriyaSabon Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftana...
25/10/2025

Zan Kamo Bello Turji Nan Da Lokaci Kaɗan — Cewar Sabon Hafsan Sojin Najeriya

Sabon Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya yi alkawarin dawo da zaman lafiya da kuma yaki da ayyukan ta’addanci a fadin ƙasar.

Janar Oluyede ya bayyana hakan ne yayin da yake magana game da barazanar da ƙungiyar Boko Haram ke yi a Jihar Yobe, inda ya kuma jaddada aniyar rundunar sojin wajen k**a manyan shugabannin ‘yan ta’adda irin su Bello Turji.

An haifi Oluyede a garin Ikere, Jihar Ekiti, a shekarar 1968. Ya fara aikin soja ne a shekarar 1987 a matsayin dalibi a Kwalejin Tsaro ta Najeriya (NDA).

Bayan kammala karatunsa, an ba shi muƙamin Laftanar na Biyu (Second Lieutenant) a shekarar 1992, inda daga nan ya ci gaba da hawa matakai har zuwa mukamin da yake kai a halin yanzu.

kana Son Kasancewa Cikin Sahun Farko Dake Samun Ingantattun Labarai Shigo Jaridar 👉 DOVE NEWS HAUSA 👈 Yanzu Kayi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Address

Zaria

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DOVE NEWS HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share