DOVE NEWS HAUSA

DOVE NEWS HAUSA Barka da zuwa shafin Jaridar DOVE NEWS HAUSA gidan jarida Mai Zaman Kanshi Dake Kawo Muku Ingantattun Labarai Cikin Harshen Hausa.
(1)

kana Son Bamu Labari Ko Faɗan Ra'ayin Ka Yi Mana Magana Ta Whatsapp 09131293900 Yanzu.

Jagoran ‘yan adawa kuma dan siyasa, Omoyele Sowore, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su fito a ranar Litinin domin bayyana...
13/06/2026

Jagoran ‘yan adawa kuma dan siyasa, Omoyele Sowore, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su fito a ranar Litinin domin bayyana matsayarsu a kan halin da kasar ke ciki.

Sowore ya ce ya kamata mutane su fito a dukkan birane, garuruwa, unguwanni da filayen jama’a domin isar da saƙonsu cikin karfi da bayyane.

Shigo shafin 👉 DOVE NEWS HAUSA don samun Ingantattun Labarai a koda yaushe.

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana matuƙar alhini da kaɗuwa kan rasuwar tsohon Manjo Janar Rabe Abubakar mai r...
13/06/2026

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana matuƙar alhini da kaɗuwa kan rasuwar tsohon Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, wanda ya rasu yayin da yake tsare a hannun masu garkuwa da mutane.

Tinubu ya yi Allah-wadai da wannan mummunan lamari, yana mai cewa mutuwar tsohon hafsan sojin babban rashi ne ba ga iyalansa kaɗai ba, har ma ga rundunar sojin Najeriya da ƙasa baki ɗaya.

Shugaban ƙasar ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta nuna wa 'yan bindiga da masu garkuwa da mutane wani sassauci ba, yana mai tabbatar da cewa hukumomin tsaro za su ci gaba da bibiyar duk masu hannu a wannan aika-aika domin su fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

Ya kuma miƙa saƙon ta'aziyyarsa ga iyalan marigayin, gwamnatin Jihar Katsina, rundunar sojin Najeriya da daukacin al'ummar ƙasar, tare da addu'ar Allah Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya jikansa da rahama, Ya ba iyalansa da waɗanda ya bari haƙurin jure wannan babban rashi.

Shigo shafin 👉 DOVE NEWS HAUSA don samun Ingantattun Labarai a koda yaushe.

13/06/2026

Saƙon jarumin Kannywood Sadiq Sani Sadiq ga al'ummar arewacin Najeriya.

Shigo shafin 👉 DOVE NEWS HAUSAdon samun Ingantattun Labarai a koda yaushe.

Matashin ɗan gwagwarmaya, Jafar Bala Afuwa, ya bayyana cewa mabiya Shi'a a Najeriya sun shafe sama da shekaru arba'in su...
13/06/2026

Matashin ɗan gwagwarmaya, Jafar Bala Afuwa, ya bayyana cewa mabiya Shi'a a Najeriya sun shafe sama da shekaru arba'in suna gudanar da zanga-zanga da fafutukar neman haƙƙoƙin talakawa kan batutuwa daban-daban da s**a shafi rayuwar al'umma.

A cewarsa, tun kafin zanga-zangar da ake gani a Abuja da sauran sassan ƙasar a yau, mabiya Shi'a sun kasance kan gaba wajen fito da muradun jama'a ta hanyar gudanar da zanga-zangar lumana a jihohi daban-daban na Najeriya.

Ya ce sun yi zanga-zanga kan kashe-kashen da ake yi a ƙasar, matsalar tsadar rayuwa, yarjejeniyoyin tsaro da ƙasashen waje, alaƙar Najeriya da Isra'ila, matsalar garkuwa da mutane, hare-haren Boko Haram da kuma matsalar Lakurawa, da sauran batutuwan da s**a shafi rayuwar al'umma.

Jafar Bala Afuwa ya yi iƙirarin cewa irin wannan fafutuka ne s**a buɗe hanya ga sauran masu rajin kare haƙƙin jama'a su samu damar gudanar da irin nasu zanga-zangar cikin lumana.

Ya kuma soki waɗanda ke tambayar irin gudunmawar da wasu ƙungiyoyi s**a bayar a wannan lokaci, yana mai cewa ya kamata kowa ya fara duba irin rawar da shi kansa yake takawa wajen neman gyaran al'umma.

Shigo shafin 👉 DOVE NEWS HAUSA don samun Ingantattun Labarai a koda yaushe.

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa Amurka za ta gano tare da lalata sinadarin uranium da Iran ta wadata idan...
13/06/2026

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa Amurka za ta gano tare da lalata sinadarin uranium da Iran ta wadata idan yanayin rikicin yankin ya lafa.

Trump ya yi wannan furuci ne yayin da yake sanar da cewa ana sa ran sanya hannu kan wata yarjejeniya da nufin kawo ƙarshen yaƙin a ranar Lahadi.

A cewarsa, Amurka za ta ɗauki matakin kawar da ajiyar uranium ɗin Iran domin tabbatar da cewa ba za a yi amfani da shi wajen ƙera makaman nukiliya ba.

Shigo shafin 👉 DOVE NEWS HAUSA don samun Ingantattun Labarai a koda yaushe.

Wasu Iraniyawa sun gudanar da gangami a harabar Ofishin Jakadancin ƙasashen waje da ke Tehran domin nuna adawarsu ga mat...
13/06/2026

Wasu Iraniyawa sun gudanar da gangami a harabar Ofishin Jakadancin ƙasashen waje da ke Tehran domin nuna adawarsu ga matakin gwamnatin Shugaba Masoud Pezeshkian na ƙoƙarin cimma yarjejeniya da Amurka.

Cikakken Rahoto Na Nan Tafe A Shafin👉 DOVE NEWS HAUSA

Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana cewa duk da cewa shahada babban abin alfahari ne a addinin Musulunci, bai k...
13/06/2026

Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana cewa duk da cewa shahada babban abin alfahari ne a addinin Musulunci, bai kamata a amince da yanayin da maƙiya ke samun damar kai hare-hare cikin sauƙi suna kashe manyan kwamandojin ƙasar ba.

Pezeshkian ya yi wannan furuci ne yayin wani taron tunawa da rasuwar jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Ayatollah Ali Khamene'i, a jawabin da aka watsa kai tsaye ta gidan talabijin.

Shigo shafin 👉 DOVE NEWS HAUSA don samun Ingantattun Labarai a koda yaushe.

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana matuƙar kaɗuwarsa da alhininsa kan rasuwar Manjo Janar Rabe A...
13/06/2026

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana matuƙar kaɗuwarsa da alhininsa kan rasuwar Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, wanda ya rasu bayan ya faɗa hannun 'yan bindiga.

Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da mutuwar tsohon jami'in sojin, inda Kwamishinan Harkokin Tsaro na jihar, Hon. Nasiru Mu'azu, ya fitar da sanarwar cikin jimami tare da miƙa ta'aziyya ga iyalan marigayin da daukacin al'ummar jihar.

Kwamishinan ya bayyana cewa gwamna Dikko Radda ya shiga cikin alhini da damuwa sakamakon wannan babban rashi, yana mai jajanta wa iyalai, abokai da duk waɗanda mutuwar marigayin ta shafa.

Shigo shafin 👉 DOVE NEWS HAUSA don samun Ingantattun Labarai a koda yaushe.

Rahoton CNN ya bayyana cewa Iran ta ƙara ƙarfafa matakan tsaro a wuraren da take adana sinadarin uranium da aka wadata, ...
13/06/2026

Rahoton CNN ya bayyana cewa Iran ta ƙara ƙarfafa matakan tsaro a wuraren da take adana sinadarin uranium da aka wadata, kamar yadda wasu majiyoyi masu masaniya kan bayanan sirrin leƙen asirin Amurka s**a shaida.

A cewar rahoton, a cikin makonnin da s**a gabata, Tehran ta ɗauki wasu matakai domin ɓoye wuraren da ake zargin suna ɗauke da ajiyar uranium da za a iya amfani da shi wajen ƙera makaman nukiliya.

Rahoton ya ƙara da cewa Iran ta yi amfani da fashe-fashe wajen rushe wasu ramuka da mashigai zuwa cikin rumbunan da ke ƙarƙashin ƙasa, a wani yunƙuri na hana gano ko isa ga wuraren ajiyar.

Shigo shafin 👉 DOVE NEWS HAUSA don samun Ingantattun Labarai a koda yaushe.

Ministan Tsaro na Najeriya, Bello Matawalle, ya bayyana cewa Allah ne kaɗai zai iya kawo ƙarshen matsalolin tsaro da s**...
13/06/2026

Ministan Tsaro na Najeriya, Bello Matawalle, ya bayyana cewa Allah ne kaɗai zai iya kawo ƙarshen matsalolin tsaro da s**a addabi ƙasar.

Matawalle ya yi wannan furuci ne yayin da yake jawabi kan ƙalubalen tsaro da Najeriya ke fuskanta, yana mai jaddada cewa duk da ƙoƙarin da hukumomin tsaro ke yi, akwai buƙatar neman taimakon Ubangiji domin samun mafita mai ɗorewa.

Shigo shafin 👉 DOVE NEWS HAUSA don samun Ingantattun Labarai a koda yaushe.

Address

Zaria

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DOVE NEWS HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share