12/08/2026
SAFNAH:
KUKAN DA BA A TAƁA MANTAWA BA
KASHI NA 16 – ZAƁIN DA YA FI MUTUWA ZAFI
Muryar mahaifin Safnah ta cika ɗakin.
"Safnah... ki yafe mini."
Safnah ta kasa motsi.
Shekaru goma sha shida tana mafarkin sake jin wannan murya.
Yanzu ta ji ta.
Amma maimakon farin ciki...
Sai tsoro ya mamaye zuciyarta.
Ta kalli mahaifiyarta tace:
"Umma... me ya sa Baba yake cewa in yafe masa?"
Safiyya ta share hawaye tace:
"Saboda ya san abin da zai faru idan abin wuyan na uku ya sake samun mai ɗauke da shi."
Malam Haruna ya ɗaga fitilar yace:
"Abin wuyan na uku ba laya ba ce kawai."
"Makulli ne."
"An yi shi ne domin ya kulle wani abu da bai k**ata ya sake dawowa duniya ba."
Safnah tayi tambaya:
"To me ya sa mutanen nan suke nemansa?"
Malam Haruna ya yi shiru.
Daga baya ya ce:
"Saboda suna tunanin idan s**a buɗe makullin..."
"za su sami iko da duk abin da ke ƙarƙashin wannan ƙasar."
Sai wani mutum daga bakin ƙofa ya yi magana:
"Ba iko kawai muke nema ba."
"Kuma ba mu zo domin mu cutar da ke ba."
Safnah ta kalle shi tace:
"To me kuke so?"
Mutumin ya cire abin da ya rufe fuskarsa da shi.
Safnah ta zaro ido tace:
Alhaji Suleiman ne.
Amma ba shi kaɗai ba.
A bayansa akwai wasu dattawan ƙauyen.
Alhaji Suleiman ya durƙusa yace:
"Na yi kuskure shekaru da s**a wuce."
"Na yi aiki tare da duhu saboda tsoro."
"Amma yanzu na san gaskiya."
Safnah ta yi shiru.
Ya ci gaba:
"Mutumin da k**e ganin mahaifinki..."
"...ba muryarsa ba ce kawai."
"An k**a wani ɓangare na ruhinsa ne tun daren da aka kashe shi."
Safnah ta ji zuciyarta ta karye tace:
"Don haka yana nan?"
Malam Haruna ya ce:
"Eh."
"Amma ba mu san ko za mu iya dawo da shi ba."
Safiyya ta riƙe hannun 'yarta tace:
"Shi ya sa na ɓoye ki."
"Na so ki girma ba tare da wannan la'anar ba."
"Amma duhun ya gano ki."
Sai abin wuyan da ke hannun mutumin ya fara haskawa.
Fuuush!
Ƙasa ta girgiza.
Wani dogon tsagewa ya bayyana a tsakiyar ɗakin.
Daga cikinsa aka fara jin ƙarar numfashi.
Malam Haruna ya yi iihu yace:
"Ku koma baya!"
Safnah ta riƙe mahaifiyarta tace:
"Me ke faruwa?"
Malam Haruna ya ce:
"Hatimin yana karyewa!"
Safnah ta kalli abin wuyan da ke wuyanta.
Ya fara haskawa sosai.
Sai ta ji wata murya a cikin zuciyarta.
"Ki zaɓa..."
"Mahaifiyarki..."
"ko ƙauyen."
Safnah ta rufe kunnuwanta tace:
"Ku daina!"
Amma muryar ta ƙara ƙarfi.
Ta ga hangen nesa.
A gefe guda...
Ta ga mahaifiyarta tana tsaye ita kaɗai.
A gefe guda...
Ta ga ƙauyen gaba ɗaya cike da mutane.
Idan ta zaɓi mahaifiyarta...
Ƙauyen zai faɗa cikin duhu.
Idan ta zaɓi ƙauyen...
Za ta rasa mahaifiyarta har abada.
Hawaye s**a cika idanunta.
Safiyya ta rungume ta tace:
"Ki saurare ni."
"Ba na son ki zaɓe ni saboda tsoro."
"Idan ceton mutane yana buƙatar ki bar ni..."
".ki bar ni."
Safnah ta girgiza kai tace:
"A'a!"
"Na riga na rasa ki sau ɗaya."
"Ba zan sake rasa ki ba."
Safiyya ta yi murmushi cikin hawaye tace:
"Ƙaunarki ta isa gare ni."
Sai ta sumbaci goshin Safnah.
Nan take...
Alamar baƙar wuta da ke hannun Safnah ta fara haskawa.
Amma wannan karon...
Baƙin hasken ya haɗu da hasken azurfa.
Malam Haruna ya tsaya cak yace:
"Abin mamaki..."
Safnah ta kalli hannunta tace:
"Me ya faru?"
Ya amsa:
"Kin haɗa haske da duhu."
"Ba tare da duhu ya mallake ki ba."
Safnah ta ɗaga kai.
A cikin idanunta akwai hawaye...
Amma kuma akwai sabon ƙarfin hali.
Sai ta ce:
"Ba zan zaɓi mahaifiyata ko ƙauyena ba."
"Zan nemi wata hanya."
Malam Haruna ya girgiza kai yace:
"Wata hanya?"
Safnah ta matse sandarta tace:
"Eh."
"Idan mahaifina ya iya ɓoye gaskiya tsawon shekaru..."
"...to dole ya bar mana wata hanya ta uku."
Nan take...
Wata ƙaramar murya ta fito daga cikin duhun ɗakin tace:
"Akwai..."
Kowa ya juya.
Ƙaramar Safnah ta sake bayyana.
Amma a wannan karon...
Tana riƙe da wani tsohon maɓalli.
Ta ce:
"Baba ya bar shi ne domin ke."
Safnah ta karɓi maɓallin.
A kansa akwai rubutu guda:
"KABARI NA ƘARSHE."
Safnah ta kalli mahaifiyarta.
Safiyya ta fara kuka tace:
"Na san wannan sunan..."
"Amma ban taɓa sanin inda yake ba."
Sai ƙaramar Safnah ta nuna bayan gidan tace:
"Yana ƙarƙashin itacen da aka binne gaskiya."
Kuma a wannan lokacin...
Ƙofar gidan ta rufe da kanta.
Daga waje aka ji wata murya mai sanyi tace:
"Ku je..."
"Domin can ne za ku ga wanda ya fara komai."
Zamu ci gaba...