Sarauniya Radio

Sarauniya Radio Your Voice | Your Story | Your Sarauniya Radio | Giving humanity a voice and also a provider of trusted information

19/09/2025

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya ɗauki nauyin karatun wasu ɗalibai daga jihar Yobe da s**a yi nasara a gasa turanci da aka gudanar a ƙasar Birtaniya. | Sarauniya Radio

Ɗaliban dai sun samu nasara a fagen gwaji na ƙwarewa da basira, lamarin da ya jawo yabo daga al’umma da hukumomin ilimi.

Atiku ya ce ɗaukar nauyin karatunsu wani ɓangare ne na goyon bayan da yake ba matasa masu basira domin su samu damar cika burinsu a fannin ilimi.

Masana harkokin ilimi sun yaba da wannan mataki, suna mai cewa hakan zai ƙarfafa sauran matasa su dage da neman ilimi tare da zama abin koyi ga sauran masu kuɗi a ƙasar.

19/09/2025

A daren jiya, an kai h@ri kan Bataliya ta 152 da ke garin Banki, a karamar hukumar Bama ta jihar Borno, lamarin da ya jawo as@rar rayuka da l@lacewar kayan s0joji.

Shaidu sun bayyana cewa motocin sojoji da dama sun ƙ0ne a cikin barikin sak**akon h@rin. Rahotanni sun tabbatar da cewa s0ja guda ɗaya da kuma farar hula ɗaya sun mu*tu, yayin da mutane shida s**a jikkata sak**akon harb!n b!ndiga.

Wadanda s**a jikkata an garzaya da su Asibitin Kiwon Lafiya na Farko (PHC) Banki domin samun kulawar gaggawa.

Har yanzu hukumomin tsaro ba su fitar da cikakken bayani kan lamarin ba, sai dai an ce jami’an tsaro na ci gaba da bincike kan yadda h@rin ya afku.

19/09/2025

Rundunar ’Yan sandan Jigawa ta yi nasarar cafke wani Sojan bogi tare da wasu mutum biyu da ake zargi da satar mota a ƙauyen Sabon Sara da ke ƙaramar hukumar Kafin Hausa.

‎Kakakin rundunar, SP Shiisu Lawan Adam, ya tabbatar da hakan a taron manema labarai da aka gudanar a Dutse. Ya ce an k**a sojan bogin mai suna Kabiru Musa tare da abokan aikinsa, Umar Ali da Sabi’u Bashir, dukkansu ’yan asalin jihar Kano.

‎Rundunar ta bayyana kayakin da ta samu a hannunsu da s**a haɗa da katunan ATM guda bakwai, lasisin tuki guda biyu, da kayan sojan da ake zargin Kabiru Musa ke amfani da su wajen aikata laifuka.

‎SP Shiisu ya ce rundunar za ta ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin, kafin daga bisani a gurfanar da su gaban kuliya.

‎Ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa ’yan sanda hadin kai da bayanai don taimakawa wajen magance aikata laifuka a fadin jihar.

‎Hukumar ta ce wannan matakin na daga cikin kokarin da rundunar ke yi na dakile matsalar satar motoci da yin amfani da sunan jami’an tsaro wajen aikata laifuka. | Sarauniya Radio

19/09/2025

An samu hatsaniya a Magama Gumau, da ke karamar hukumar Toro ta jihar Bauchi, bayan da wata mata ta shiga hannun ’yan sanda bisa zargin ƙ0na al’aurar ’yarta ’yar shekara 10, bisa zargin cewa yarinyar mayya ce.

Rahotanni sun bayyana cewa matar ta dumama cokali a cikin wuta, sannan ta umarci sauran ’ya’yanta biyu su riƙe ƙanwarsu, kafin ta yi amfani da shi ta ƙona ta.

Lamarin ya jefa yarinyar cikin mawuyacin hali na rashin iya yin fitsari da bayan gida cikin sauƙi. Maƙwabta da s**a ga abin da ya faru s**a garzaya da batun ga ’yan sanda.

An kai yarinyar zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH), Bauchi domin samun kulawa ta gaggawa.

Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Mohammed Ahmed Wakil, ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa an cafke matar tare da wasu ciki har da wata mai maganin gargajiya, Fatima Abdullahi, wadda ake zargi da karɓar kuɗi daga uwar kafin ta tabbatar mata cewa yarinyar mayya ce. | Sarauniya Radio

19/09/2025

Hukumar Sibil Difens (NSCDC) a jihar Gombe ta tabbatar da k**a mutum shida bisa zargin tono gawar wani a kabari domin cire wasu sassan jikin a yi tsafi da sh.i | Sarauniya Radio

Rahotanni sun nuna cewa mutanen da ake zargi sun shiga makabarta ne da daddare, inda s**a tono gawar sannan s**a cire wasu sassa na jikinta kafin a k**a su.

Mai magana da yawun NSCDC a jihar, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa bincike na ci gaba domin gano sauran wadanda ke da hannu a wannan aika-aika.

An ce za a gurfanar da wadanda ake zargi a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

19/09/2025

Manoma a Arewacin Najeriya na ci gaba da kokawa kan yadda Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta rage farashin kayan gona a kasuwa ba tare da rage farashin takin zamani ba. | Sarauniya Radio

A cewar manoman, wannan mataki k**ar wani zagon ƙasa ne ga harkar noma a Najeriya, musamman ganin cewa Arewacin ƙasar ne cibiyar samar da yawancin abinci da ake ci a ƙasar.

Sun kuma nuna takaici kan yadda Shugaba Tinubu ya kaddamar da tiraktoci 2,000 amma har yanzu ya ƙi amincewa a raba su ga manoma, alhali kuwa damina ta fara ja baya.

Wasu daga cikin manoman sun bayyana cewa:

“𝙄𝙙𝙖𝙣 𝙛𝙖𝙧𝙖𝙨𝙝𝙞𝙣 𝙠𝙖𝙮𝙖𝙣 𝙜𝙤𝙣𝙖 𝙮𝙖 𝙠𝙖𝙧𝙮𝙚, 𝙖𝙢𝙢𝙖 𝙛𝙖𝙧𝙖𝙨𝙝𝙞𝙣 𝙩𝙖𝙠𝙞 𝙮𝙖 𝙘𝙞 𝙜𝙖𝙗𝙖 𝙙𝙖 𝙝𝙖𝙬𝙖, 𝙗𝙖 𝙢𝙪 𝙙𝙖 𝙬𝙖𝙣𝙞 𝙧𝙞𝙗𝙖 𝙖 𝙘𝙞𝙠𝙞𝙣 𝙣𝙤𝙢𝙖. 𝙒𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 𝙝𝙖𝙣𝙮𝙖 𝙘𝙚 𝙩𝙖 𝙩𝙖𝙪𝙮𝙚 𝙘𝙞 𝙜𝙖𝙗𝙖𝙣 𝙣𝙤𝙢𝙖 𝙙𝙖 𝙠𝙪𝙢𝙖 ƙ𝙖𝙧𝙖 𝙟𝙚𝙛𝙖 𝙢𝙖𝙣𝙤𝙢𝙖 𝙘𝙞𝙠𝙞𝙣 𝙩𝙖𝙡𝙖𝙪𝙘𝙞.”

“𝘽𝙖 𝙢𝙪 𝙛𝙖𝙝𝙞𝙢𝙘𝙞 𝙢𝙚 𝙂𝙬𝙖𝙢𝙣𝙖𝙩𝙞𝙣 𝙏𝙖𝙧𝙖𝙮𝙮𝙖 𝙩𝙖𝙠𝙚 𝙣𝙪𝙛𝙞 𝙙𝙖 𝙢𝙖𝙣𝙤𝙢𝙖 𝙖 𝙬𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 ƙ𝙖𝙨𝙖 𝙗𝙖. 𝙏𝙞𝙧𝙖𝙠𝙩𝙤𝙘𝙞 𝙣𝙖 𝙣𝙖𝙣 𝙖𝙟𝙞𝙮𝙚, 𝙙𝙖𝙢𝙞𝙣𝙖 𝙠𝙪𝙢𝙖 𝙣𝙖 𝙬𝙪𝙘𝙚𝙬𝙖. 𝙈𝙚 𝙮𝙖𝙨𝙖 𝙜𝙬𝙖𝙢𝙣𝙖𝙩𝙞 𝙠𝙚 𝙬𝙖𝙨𝙖 𝙙𝙖 𝙧𝙖𝙮𝙪𝙬𝙖𝙧𝙢𝙪 𝙙𝙖 𝙠𝙪𝙢𝙖 𝙩𝙨𝙖𝙧𝙤𝙣 𝙖𝙗𝙞𝙣𝙘𝙞 𝙣𝙖 ƙ𝙖𝙨𝙖?”

Sun bukaci gwamnati ta sake duba tsarin, tare da ɗaukar matakan da za su baiwa manoma tallafi wajen samun taki a farashi mai rahusa domin ci gaba da samar da abinci a ƙasar.

19/09/2025
19/09/2025

Jama'a Assalamu alaikum Sarauniya Radio, ke muku sallama, daga nan birnin tarayya Abuja, tare da fatan kun tashi lafiya.

18/09/2025

‎Makarantar Sultan Bright Academy Bauchi (Nursery da Primary) ta bayyana aniyarta ta zama cibiyar ilimi ta zamani wacce ke haɗa kwarewar karatu da tarbiyya cikin yanayi mai cike da tsaro da kulawa.

‎Makarantar na sahun gaba a jahar Bauchi wajen samar da ilimi mai inganci, rungumar fasahar zamani da kuma koya wa yara kyawawan dabi’u.

‎Kuma suna da abubuwa k**ar haka:⤵️
‎• Malamai gogaggu da ke baiwa ɗalibai kulawa ta musamman

‎• Amfani da fasaha wajen koyarwa

‎• Kula da ladabi da tarbiyya

‎Makarantar na ba da muhimmanci ga ci gaban tunanin yara, ƙarfafa sha’awar karatu da kuma shirya su domin nasara a rayuwa.

Za ku iya ‎tuntuɓarsu k**ar haka:⤵️
‎📞 07036917288 | 08068582198
‎🏫 Karofin Madaki, new transformer, opposite Dr. Said Chemist, Bauchi.

Sarauniya Radio | Kafar Al'umma

A Kamaru, Brands Biya, ’yar shugaban ƙasar Paul Biya, ta yi kira ga ’yan ƙasa da kada su sake zaɓen mahaifinta a babban ...
18/09/2025

A Kamaru, Brands Biya, ’yar shugaban ƙasar Paul Biya, ta yi kira ga ’yan ƙasa da kada su sake zaɓen mahaifinta a babban zaɓen da za a gudanar ranar 12 ga Oktoba, 2025.

A cikin wani faifan bidiyo da ta wallafa a shafinta na TikTok, Brands ta ce Kamaru na cikin mummunan hali na siyasa da tattalin arziki, don haka lokaci ya yi da a ba ’yan adawa dama domin kawo sauyi.

Wannan kira daga ’yar shugaban ya haifar da ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta, inda mutane da dama ke bayyana mamaki da kuma yadda take s**ar mahaifinta a bainar jama’a.

Shugaba Paul Biya, wanda ke da shekaru sama da 90, ya shafe fiye da shekaru 40 yana mulkin Kamaru, lamarin da ke ci gaba da jawo muhawara kan tsawon lokacin shugabancinsa.

Al’ummomin jihohin Katsina da Zamfara na ci gaba da ɗanɗana kuɗansu a hannun ’yan b!ndiga duk da yarjejeniyar sulhu da a...
18/09/2025

Al’ummomin jihohin Katsina da Zamfara na ci gaba da ɗanɗana kuɗansu a hannun ’yan b!ndiga duk da yarjejeniyar sulhu da ake yi tsakaninsu da gwamnatin jihohin da kuma wasu shugabannin al’umma.

Masana harkokin tsaro a Najeriya sun dade suna gargaɗin cewa sulhu da ’yan b!ndiga ba mafita ba ce, domin a lokuta da dama m@haran kan bar yankin da aka yi sulhu da su, su koma wasu wurare su kai h@re-h@re, sannan daga baya su dawo inda aka yi sulhun domin neman mafaka.

H@re-h@ren ’yan b!ndiga dai na daga cikin manyan kalubalen tsaro da ke addabar jihahin Katsina da Zamfara da wasu sassan Arewacin Najeriya, duk da kokarin da gwamnati da jami’an tsaro ke cewa suna yi na kawo karshen matsalar.

©️ Sarauniya Radio

18/09/2025

Jama'a Assalamu alaikum Sarauniya Radio, ke muku sallama, daga nan birnin tarayya Abuja, tare da fatan kun wayi gari lafiya.

Address

Sunusi Dantata House, Plot 274, Central Business District
Zaria
563744

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sarauniya Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sarauniya Radio:

Share

Category