
19/09/2025
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya ɗauki nauyin karatun wasu ɗalibai daga jihar Yobe da s**a yi nasara a gasa turanci da aka gudanar a ƙasar Birtaniya. | Sarauniya Radio
Ɗaliban dai sun samu nasara a fagen gwaji na ƙwarewa da basira, lamarin da ya jawo yabo daga al’umma da hukumomin ilimi.
Atiku ya ce ɗaukar nauyin karatunsu wani ɓangare ne na goyon bayan da yake ba matasa masu basira domin su samu damar cika burinsu a fannin ilimi.
Masana harkokin ilimi sun yaba da wannan mataki, suna mai cewa hakan zai ƙarfafa sauran matasa su dage da neman ilimi tare da zama abin koyi ga sauran masu kuɗi a ƙasar.