15/05/2026
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bukaci Shugaba Bola Tinubu da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, su gaggauta sakin tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kafin bikin babbar Sallah.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa, Atiku ya bayyana ci gaba da tsare El-Rufai a matsayin abin takaici, rashin adalci da kuma cin zarafin ‘yancin dan Adam, musamman a lokacin da Musulmai ke shirin gudanar da bukukuwan Sallah.
A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya fitar a ranar Juma’a, Atiku ya ce gwamnati bai kamata ta yi amfani da karfin iko wajen tsoratar da abokan hamayyar siyasa ba.
Ya ce duk da bambancin siyasa, El-Rufai dan Najeriya ne da kundin tsarin mulki ya ba shi ‘yancin walwala, adalci da bin ka’ida kafin hukunci.
Atiku ya kuma bukaci gwamnatin tarayya da gwamnatin Kaduna su fito su bayyana dalilin tsare El-Rufai idan har akwai sahihin shari’a a kansa, yana mai gargadin cewa ci gaba da tsare shi ba tare da cikakken bayani ba na kara jefa damuwa kan makomar dimokuradiyya a kasar.
Ya kara da cewa lokacin Sallah lokaci ne na tausayi, yafiya da hadin kai, don haka babu dalilin hana mutum kasancewa tare da iyalansa ba tare da an bi ka’ida ba.