Indararo Hausa

Indararo Hausa Jaridar Indararo, sabuwar kafar watsa labarai da ke kawo muku labarai cikin harshen Hausa kai tsaye daga tushen al'umma masu gaskiya,

• KARFIN SOJIN NIGERIA....• Nigeria Ba Kanwar Lasa Bace, Nigeria Tana Da Karfin Soji, Tun Wajejan 1960 Nigeria Ta Dade D...
03/11/2025

• KARFIN SOJIN NIGERIA....

• Nigeria Ba Kanwar Lasa Bace, Nigeria Tana Da Karfin Soji, Tun Wajejan 1960 Nigeria Ta Dade Da Samun Yabo Dakuma Kambamawa Daga UN (United Nations) Domin Sunyi Shura Wajan Tura Jami'an Soji Zuwa Wata Kasa Abinda Ake Kira (Peacekeeping Operations) Suyi Yaki Su Samar Da Zaman Lafiya Kuma Su Dawo Gida NIGERIA.

• Asalin Sojojin Najeriya Sun Samo Asali Tun Wajan Shekarar 1863, Lokacin Da Aka Kafa “Glover Hausas” Wani Rukuni Ne Na Mayaka Daga Yankin Arewa (Hausa Soldiers) Da Birtaniya Tayi Amfani Dasu A Yankin Lagos Colony.

• Daga Baya Aka Hadasu Cikin Royal West African Frontier Force (RWAFF) A Shekarar 1900, Wanda Ya Kunshi Sojoji Daga Najeriya, Ghana, Saliyo da Gambiya.

• Bayan Nigeria Ta Samu Yancin Kai A Shekarar 1960, Najeriya Ta Kafa (Nigerian Army) Amatsayin Rundunar Soja Ta Kasa Mai Cikakken Iko, Sojojin Najeriya Suna Daya Daga Cikin Mafi Karfi Da Kwarewa A Afirka Wajen Iya Yaki Dakuma Samar Da Zaman Lafiya.

• Tunda Na Fara Wannan Rubutun Abinda Yake Zuwa Raina Shine: Zaku Iya Tambaya Cewa Duda Wannan Karfin Nasu Da Kwarewa Mai Yasa Ake Ta'âddanci A Kasar? Shima Muna Da Rubutu Akansa... Kudai Kuyi Shear..

Engr jabir

Kuyi Following na Indararo Hausa



Munafukin mutumin nan fah har cewa yayiWai an zaɓi muslim-muslim ne domin a kawo ƙarshen kiristoci a Nigeria 🇳🇬Bayan cin...
03/11/2025

Munafukin mutumin nan fah har cewa yayi

Wai an zaɓi muslim-muslim ne domin a kawo ƙarshen kiristoci a Nigeria 🇳🇬

Bayan cin zaɓe kullum sai an kashe sama da kirista 200 a Nigeria 🇳🇬

Me Zaku Ce?

Indararo Hausa



TIRKASHI:Turawa sun fara kira Da a Raba NAJERIYA saboda ta kasa yiwa kowane bangare Adalciinda wasu daga cikin Kiristoci...
03/11/2025

TIRKASHI:Turawa sun fara kira Da a Raba NAJERIYA saboda ta kasa yiwa kowane bangare Adalci

inda wasu daga cikin Kiristoci masu murnar cewa Amurka zata kawo musu dauki s**a fara fadar cewa ba abinda suke nema ba kenan,

me za ku ce

Indararo Hausa





Martani: ashirye muke matukar s**a cillo mana zamu cilla masu ba'asan nigeria 🇳🇬 da tsoro.cewar Alhassan Mai lafiame za ...
03/11/2025

Martani: ashirye muke matukar s**a cillo mana zamu cilla masu ba'asan nigeria 🇳🇬 da tsoro.

cewar Alhassan Mai lafia

me za ku ce?

Indararo






MARTANI ZUWA GA TRUPM:Kai Trump....Kabi a hankali bafa tsoronka ake ji ba, yadda Amurka take kasa mai yanci haka Nigeria...
02/11/2025

MARTANI ZUWA GA TRUPM:Kai Trump....

Kabi a hankali bafa tsoronka ake ji ba, yadda Amurka take kasa mai yanci haka Nigeria take, yadda Ingila tayiwa Amurka mulkin mallaka haka tayiwa Nigeria, yadda kuke da yawan mutane haka ita ma Nigeria take da yawa....

Idan lokacin tattaunawa yayi, za mu zo cikin izza da alfaharin kasancewar mu shugabannin kasar bakar fata mafi girma a duniya....

Ba zamu lamunci yinkurin da kake na shiga sabgogin kasarmu ba...

Cewar: Rabiu Biyora

Indararo Hausa







Wasu na zargin matatar man Dangote ce data dauko hanyar Zama babu irinta a Duniya,shine yake  tsolewa Thurawa ido kusaan...
02/11/2025

Wasu na zargin matatar man Dangote ce data dauko hanyar Zama babu irinta a Duniya,
shine yake tsolewa Thurawa ido kusaan dalilin dayasa suke son ganin sun wargaza Najeriya kenan.

me za ku ce?

Indararo Hausa







BA MUSULMI BANE KE KASHE KIRISTOCI BA A NAJERIYA. Cewar Gorge Udom Kirista daga Arewacin Najeriya:Matsalar son addini (R...
02/11/2025

BA MUSULMI BANE KE KASHE KIRISTOCI BA A NAJERIYA. Cewar Gorge Udom Kirista daga Arewacin Najeriya:

Matsalar son addini (Religious Bigotry) ba daga Arewa ta fara ba.

Mu koma baya kadan zuwa shekara ta 1962, lokacin da Musulmin Arewa, Sir Abubakar Tafawa Balewa, ya saka Najeriya cikin Majalisar Ikklisiyoyi ta Duniya (World Council of Churches), sannan a 1963 ya kuma saka ta cikin International Bible Society, babu wani kuka daga Musulman Arewa.

Asabar tana daga cikin ranakun aiki a Najeriya har zuwa shekara ta 1973, lokacin da Gowon, wanda yake Kirista daga ƙananan kabilu na Arewa, ya ayyana ta a matsayin ranar hutu don bai wa Seventh Day Adventist Church damar yin ibada — babu wani kuka daga Musulman Arewa.

A watan Fabrairu na 1979, Olusegun Obasanjo ya hana shahararren mai wa’azin Musulunci, Ahmed Deedat, shiga Najeriya — babu kuka daga Musulman Arewa.

A shekara ta 1982, Pope John Paul II ya ziyarci Najeriya, kuma Musulmi ne, Alhaji Shehu Shagari, ya tarbe shi.

Reinhard Bonnke, malamin Kirista mai wa’azi, yana shigowa Najeriya yadda yake so — babu kuka daga Musulman Arewa.

Abacha ma ya tarbi Pope John Paul, ya kuma kafa Papal Square a kusa da hanyar Kubwa Expressway — babu kuka daga Musulmai.

Amma a 1986, lokacin da Babangida ya saka Najeriya cikin Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi (OIC), sai tarzoma ta tashi a Lagos, Port Harcourt da Enugu — wanda CAN (Christian Association of Nigeria) ta shirya.

Don Allah, wa ne ke nuna son addini a nan?

A ‘yan kwanakin nan, Majalisar Koli ta Harkokin Musulunci ta Najeriya (NSCIA) ta bayyana cewa ba ta da hannu cikin siyasa — amma ya ya da CAN?

A shekara ta 2013, an k**a jirgin sama mallakin shugaban CAN a Afirka ta Kudu cike da kuɗin waje — me da za a ce da jirgin nan idan mallakin Sarkin Musulmi ne?

Don haka mu tambayi kanmu: Su waye masu son addini a gaskiya? Kafin mu sake yin kuskure a matsayin al’umma.

Ku biyu shafin Indararo Hausa domin cigaba da samun labarai da al'amuran yau da gobe,



DA DUMi-DUMi II Sheikh Abubakar Mahmud Gumi Yayi Zazzafan Martani Akan Kalaman "Donald Trump"  Cewa, Ze Dauki Matakin So...
02/11/2025

DA DUMi-DUMi II Sheikh Abubakar Mahmud Gumi Yayi Zazzafan Martani Akan Kalaman "Donald Trump"

Cewa, Ze Dauki Matakin Sojoji Akan Nigeria Saboda K!san Da Ake Yiwa Kiristoci

Malamin (Dr Gumi) Yace " Donald Trump,Shine Gatan Kiristoci A Nigeria, Allah Kuma Gatan Musulmi, Daman Me Kuke Tunanin Fitowa Daga Bakin Makiy!n Musulunci Irin Trump?
Saboda Haka Yan Uwa Musulmi Ku Kwantar Da Hankalinku, Allah Zeyi Mana Maganin Duk Wasu Masu Neman Tana Fitina A Kasarmu Ta Nigeria"

DR Ahmad Gumi Yayi Wannan Furucin Ne A Karatun Daya Gabatar Jiya, Inda A Safiyyar Wannan Rana Ya Sake Tabbatarwa Da Kiristocin Nigeria Cewa
"Daman Mu Musulmi Allah Shine Gatanmu Bawai Donald Trump Ba, Kuma Shine Zeyi Mana Maganin Shi"

Allah Ya Karawa Malam Lpy, Yayi Mana Maganin Wannan Azzalum! Donald Trump

Indararo Hausa

YANZU YANZU: AN Tonaa Asiri, Wannan shi ne Babban Fàšťò daya kaiwa ƙasar Amurika labarin cewa Ana yiwa kiristoci kis$n g...
02/11/2025

YANZU YANZU: AN Tonaa Asiri, Wannan shi ne Babban Fàšťò daya kaiwa ƙasar Amurika labarin cewa Ana yiwa kiristoci kis$n gilla a Nigeria, .

Sunansa "Bishop Wilfred Anagbe" daga jahar Benue/Makurdi

Wannan shine wanda yakai labarin ƙarya cewa ana kashe kiristoci a Nigeria.

Alokacin tattaunarsa da wani shahararren ɗan siyasar ƙasar amerika kuma malamin coci "Tony Perkins"

Shi kuwa "Tony Perkins" shine yakai wannan labarin zuwaga majalissar dokokin ƙasar amerika

Daga nan majalissar amerika tayi kira zuwaga shugaban ƙasar "Donald Trump" domin ɗaukar matakin gaggawa

Yak**ata gwamnatin Nigeria ta k**a wannan mutumin tare da hukuntashi bisa laifin cin amanar ƙasa.

Daga: Alhassan Mai Lafia.

Indararo Hausa

Babu Yadda Źà A Yi Na Kaiwa Kasata Harì, Ko Kumà Nà Ķàshè Iyàyèna Kan Wani Zàŕgìn Karyà Na Kisàn Kirìstòcì, Cewar Sojan ...
02/11/2025

Babu Yadda Źà A Yi Na Kaiwa Kasata Harì, Ko Kumà Nà Ķàshè Iyàyèna Kan Wani Zàŕgìn Karyà Na Kisàn Kirìstòcì, Cewar Sojan Amurka Dan Asalin Jihar Kano, Suleiman Isah

- Rariya

Me za ku ce?


Mawallafin jaridar Sahara reporters kuma dan Gwagwarmaya, Omoyele Sowore ya bayyana cewa, Kiristoci su daina murna sabod...
02/11/2025

Mawallafin jaridar Sahara reporters kuma dan Gwagwarmaya, Omoyele Sowore ya bayyana cewa,

Kiristoci su daina murna saboda Shugaban kasar Amurka, Donald Trump yace zai kawo hari dan Khashye masu yiwa kiristoci Khisan Qare dangi.

Sowore yace abin zai shafi kowa ne.

Shugaban kasar Amurka Donald Trump yace ba zasu zuba ido suna ganin ana kashe Kiristoci ba, yacw idan Gwamnati bata dauki mataki akan lamarin ba zasu dauki mataki ta hanyar soji.

Indararo Hausa

KAJI RABO: Sabuwar jarumar Kannywood ta mallaki motar GLK daga shigowar ta masana'antar lamarin da yasa masoyan ta je ga...
02/11/2025

KAJI RABO: Sabuwar jarumar Kannywood ta mallaki motar GLK daga shigowar ta masana'antar lamarin da yasa masoyan ta je ganin ta shigo da kafar dama

Motar GLK dai mota ce mai tsada kuma wacce jaruman Kannywood mata suke burin mallaka

Wacce fata za kuyi mata ?

Daga Salisu Editor,

Indararo Hausa




Address

216 Angwn Karfe Zaria City
Zaria
8000014

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Indararo Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Indararo Hausa:

Share