AlMizan

AlMizan A Hausa Newspaper for the Hausa speaking people in Nigeria and diaspora. An organ of the Islamic Mov
(1)

Ya yi arba da wanda ya yi kidinafin din su a harin jirgin kasa na Kaduna, amma ya kyale shiIn kai ne yaya za ka yi?Daya ...
01/05/2025

Ya yi arba da wanda ya yi kidinafin din su a harin jirgin kasa na Kaduna, amma ya kyale shi

In kai ne yaya za ka yi?

Daya daga cikin wadanda aka sace daga jirgin kasa a shekarar 2022, ya bayyana yadda ya yi magana da daya daga cikin 'yan bindigar da s**a sace shi a wani masallaci a jihar Kaduna.

A cikin wata hira da ya yi da Daily Trust, Comrade M. Muhammad, wanda ya ci karo da daya daga cikin wadanda s**a sace shi a masallaci, ya ba da labarin abin da ya faru a tsawon sa’ar da s**a yi suna magana.

“Da gaske ne cewa na ga mutumin nan Abubakar a Masallaci k**ar yadda na buga a shafina na sada zumunta. A gaskiya ya yi mamakin gani na, amma na yi masa murmushi, wanda hakan ya sa ya samu kwanciyar hankali.”

“Muka fita waje, ya gaya mani cewa ya tuba yanzu, kuma yana yin hayan mashin acaba ne. Ya kuma gaya mani cewa sojoji sun kashe daya daga cikin shugabanninsu, sanannen dan ta’addan nan, Baba Adamu, kuma na yi farin cikin jin labarin kisan,” in ji shi.

Kwamared din ya kara da cewa, ya gafarta wa dan bindigar da aka fi sani da Abubakar domin akwai wadanda ba su tsira daga harin ba, amma shi ya tsira.

“Wasu na iya yin mamakin cewa na gafarta masa, na bar shi ya tafi, domin tun kafin in gan shi a ranar, na riga na gafarta musu,” in ji shi.

Muhammad, duk da haka, ya ce ba zai gafarta wa gwamnati ba saboda abin da ya faru da shi a daren 28 ga Maris, 2022, “domin an kai wa jirgin harin ne saboda sakaci na gwamnati.”

Ya ce, gwamnati ta sami gargadin cewa za a iya kai wa jirgin harin, amma ba ta yi wani abu don hana aukuwar harin ba.

Wanda aka azabtar a kidinafin din, ya kuma zargi gwamnati da yin watsi da su bayan sun samu ‘yanci, inda ya ce su ne s**a biya kuɗin jinyar da s**a yi a bayan da s**a kubuta.

“Mun kwana 196, wato watanni 7, a zaman talala, bayan an sake mu, gwamnati ba ta yi mana komai ba face maganin drip da rigakafin zazzabin cizon sauro da ta ba mu.”

“Da yawa daga cikin mu, ciki har da ni, mun sha fama da tashin hankalin firgici, kuma dole ni sai da na je asibitin Neo Psychiatric tsawon watanni don neman magani ba tare da tallafin gwamnati ba.”

In za a iya tunawa a ranar 28 ga Maris, 2022, an kai wa wani jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna hari a Katari, Kaduna, kusan minti 15 kafin ya isa wurin da zai tsaya.

‘Yan bindiga sun sace daruruwan fasinjoji yayin da s**a kashe wasu ko kuma s**a jikkata su, bayan sun tayar da bam a jirgin.

Jirgin ya taso daga tashar Idu ta Abuja da karfe 6 na yamma, kuma ya k**ata ya isa tashar jirgin kasa ta Rigasa a Kaduna da karfe 8 na yamma, amma bai kai inda aka tsara ba.

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da sabon shafin intanet don inganta sayayya a ma’aikatun gwamnatiGwamnatin Tarayya ta sha ...
30/04/2025

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da sabon shafin intanet don inganta sayayya a ma’aikatun gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta sha alwashin magance matsalolin da s**a dabaibaye harkar sayayya a hukumomin gwamnati tare da ƙara inganta ayyuka a ma’aikatun gwamnati.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana haka a Abuja ranar Laraba yayin ƙaddamar da Gidan Yanar Takardun Shaidar Sayen Kaya na Nijeriya da Hukumar Sayen Kaya ta Ƙasa (BPP) ta ƙirƙiro tare da haɗin gwiwar Bankin Duniya.

Idris ya ce: "Wannan taron wata babbar alama ce ta ci gaba a ƙoƙarin da ake yi na sauya tsarin sayen kaya na gwamnati a Nijeriya, wanda ke da cikakken daidaito da Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, musamman wajen ƙarfafa tsarin shugabanci domin isar da ayyukan gwamnati cikin inganci, gaskiya da riƙon amana."

Ministan ya ce sabon gidan yanar na intanet zai taimaka wajen shawo kan matsalolin da s**a daɗe suna dagula harkokin sayayya a gwamnati, k**ar yadda ake fama da rashin ingantattun tsare-tsare, ƙarancin ƙwararru da rashin tsarin horaswa na dindindin.

Ya ce: “Ƙaddamar da wannan sabon shafin ba kawai cigaba ba ne a fannin fasaha; wata babbar hanya ce ta sauya fasalin aiki gaba ɗaya wadda ke magance manyan ƙalubale a tsarin sayen kaya na gwamnati, irin su cikas da ke yawan faruwa, rashin ingantattun hanyoyin sayayya, ƙarancin ma’aikatan da s**a dace, da kuma rashin ingantaccen tsarin gina ƙwarewa.

"Waɗannan matsaloli sun daɗe suna hana a yi amfani da dukiyoyin gwamnati yadda ya k**ata tare da kawo cikas ga cigaban tattalin arziki gaba ɗaya a ƙasar nan."

Ya ce wannan sabon tsari zai bai wa jami’an sayayya damar samun horo, takardun shaida, da kuma damar yin aiki da ƙwarewa, daidai da matakin duniya.

Idris ya ce: “Za a tabbatar da cewa mu jami’an gwamnati muna sayen kaya ba kawai bisa doka ba, har ma ƙwararru ne kuma masu iya gogayya a matakin duniya."

Idris ya yaba wa Darakta-Janar na BPP, Dakta Adebowale Adedokun, bisa jajircewa da hangen nesan sa wajen inganta tsarin sayayya a Nijeriya.

Ya ce wannan gidan yana hujja ce ta jajircewar sa wajen ganin an sabunta tsarin sayayya a ƙasar nan.

Ministan ya kuma buƙaci ‘yan ƙasa da su fahimci cewa sabon gidan yanar ba kawai don gwamnati ba ne, har ma wata hanya ce da za su iya amfani da ita wajen neman ingantattun ayyuka da gaskiya.

“Don haka ina kira ga dukkan hukumomi da jami’an gwamnati da su rungumi wannan shiri gaba ɗaya, kuma ina kira ga kafafen yaɗa labarai, musamman, da su taimaka wajen yaɗa amfanin sa da kuma sa ido kan yadda ake aiwatar da shi,” inji shi.

Cikin waɗanda s**a halarci taron akwai Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya, Misis Didi Esther Walson-Jack; Ministan Kuɗi kuma Ministan Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Mista Wale Edun; Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa; Ministar Harkokin Mata, Hajiya Imaan Sulaiman-Ibrahim; Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa (rtd); da Darakta-Janar na FRCN da NTA, Dakta Mohammed Bulama da Kwamared Abdulhamid Dembos.

Kafin ka fara abu, ka nemi ilimi a kansaA cikin Kano, an yi wani saurayi mai suna Bala, wanda ya yanke shawarar fara san...
29/04/2025

Kafin ka fara abu, ka nemi ilimi a kansa

A cikin Kano, an yi wani saurayi mai suna Bala, wanda ya yanke shawarar fara sana’ar POS, domin ya ga kowa yana yi, kuma ana samun kuɗi sosai. Bai D
Da ilimin Lissafi sosai, amma sai ya ce, “A Birni, kowa yana iya zama Boss.”

Ranar farko, sai ya samu tebur da kujera, ya zauna a G
gefen t**i, ya fesa turare, ya dora POS. Sai wata Budurwa kyakkawa ta zo tana sheƙi da kamshi.

“Yaya, zan cire dubu goma,” in ji ta.

Bala ya shigar da katin ATM din ta ya cire Naira dubu goma daga account din ta, Amma maimakon ya ba ta N10,000, sai ya ba ta N100,000, saboda hannunsa yana rawa saboda ya tsaya kallon kyakkawar Yarinyar.

Budurwar ta karbi kuɗi, ta wuce cikin girmamawa. Sai Bala ya duba Account ya ga Naira dubu goma ya cire, amma ya ba ta Naira dubu Ɗari. Sai ya fara ihu ya ce, “Wayyo POS!”

Ya bi ta da gudu yana ihu, amma budurwar ta shige rububin jama'a ta bace. Mutane s**a taru suna masa dariya. Wasu s**a ce masa: “Ka fara neman ilimi, kafin ka fara kasuwanci, in ba haka ba za ka yi ta asara.😃

EFCC ta yi wawan kamun Dala miliyan 98 a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano Hukumar EFFC mai yaƙi da cin hanci da ras...
29/04/2025

EFCC ta yi wawan kamun Dala miliyan 98 a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano

Hukumar EFFC mai yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ta ce ta fara bincike kan wasu dubun dubatar kuɗaɗen ƙasar waje da aka k**a a filin jirgin sama na Kano.

EFCC ta ce an ga dala 86,500,305 da kuma riyal 305,150 ne cikin wata jaka lokacin da aka ga wani ma'aikacin filin jirgin mai suna Sale Bala ya yi yunƙurin ɗaukar ta ranar Lahadi.

"Bayan bincike, jami'an kwastam sun gano kuɗaɗen ne da aka ɓoye cikin zannunwan gado," in ji EFCC cikin wata sanarwa.

"An k**a Sale Bala da wani Abdullahi Tahir da ake zargin shi ne aka tsara zai karɓi jakar bayan kammala tantance ta."

Ta ƙara da cewa kuɗin da kuma waɗanda ake zargi na tsare a hannunta, kuma za ta kai su kotu da zarar an kammala bincike.

Yqdda kotu ta yanke wa wani Sojan Sama na Najeriya Hukuncin Kisa Saboda Kisan BudurwarsaWata Kotun Soji ta Sojojin Sama ...
29/04/2025

Yqdda kotu ta yanke wa wani Sojan Sama na Najeriya Hukuncin Kisa Saboda Kisan Budurwarsa

Wata Kotun Soji ta Sojojin Sama ta Najeriya (NAF) a ranar Talata 29 ga Afrilun 2025 ta yanke wa Air Craftman Benard Kalu hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda kashe abokiyar aikinsa, Corporal Oladipupo S. A.

Kalu ya harbe Oladipupo a gidanta da ke Compound 9 na Barikin Sojojin Sama a Makurdi, bisa zargin cewa tana yin soyayya da wani mutum.

Kalu, mai shekaru 21, bayan ya kutsa cikin gidan Oladipupo da sanyin safiyar ranar wata Lahadi, ya harbe ta a makogwaro yayin da yake kusa da ita, sannan ya yi ƙoƙarin kashe mutumin da ya same shi a gidan.

Amma bindigarsa ta ki ta k**a, wanda ya sa mutumin ya yi ƙoƙari ya kokawa da Kalu har ya samu nasarar kwace masa bindiga.

Mai shari’a, Flight Lieutenant MA Umoh, ya lissafta tuhume-tuhumen da aka yi wa Kalu guda takwas, ciki har da kisan kai, kutse cikin gida ba bisa ka’ida ba, yunkurin kisan kai, rashin yi aikin soja, asarar kayan aikin soja, rashin bin umarnin soja, da kuma lalata tsarin soja.

Umoh ya ce wanda ake tuhuma ya ki amincewa da dukkan tuhume-tuhumen, kuma masu gabatar da kara sun kawo shaidu 13, yayin da lauyan kariya ya kawo shaidu uku, ciki har da wanda ake tuhuma.

Ya kara da cewa, kodayake masu gabatar da kara sun same shi da laifi a kan dukkan tuhume-tuhumen, lauyan kariya a karshen shari’ar ya ce masu gabatar da kara ba su tabbatar da laifin ba.

Lauyan kariya, Abimiku Ewuga, ya roki kotu da ta yi wa wanda ake tuhuma jinkirin hukunci, musamman saboda shi ba a taba samun laifinsa ba kuma shi ne mai tallafa wa iyalinsa.

A yanke hukunci, Shugaban kotun, Group Captain Elisha Bindul, wanda ya same shi da laifi a kan tuhume-tuhume shida daga cikin takwas, ya yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya, wanda zai dogara ne ga amincewar babban kwamandan sojojin sama.

29/04/2025

An tone kabarin tsohon Shugaban Siriya, an sace gawar

Wasu da ba a san ko su waye ba sun tone kabarin Hafez al-Assad, mahaifin tsohon shugaban Syria Bashar al-Assad, a Qardaha kuma sun kwashe gawarsa zuwa wani wurin da ba a san ko ina ba, a cewar rahotanni.

29/04/2025

Ya k**ata Minista ya duba sansanin inda ake bautar da yan Nijeriya a Jamhuriyar Benin.

29/04/2025

Har Indiyawa sun soma sauka a Madinah don fara aikin Hajji. Akalla za su kwashe kwanaki 45 kenan a Saudiyya

Shin da gaske ne Mataimakin Gwamnan Neja, Yakubu Garba, Zai yi murabus?Mataimakin Gwamnan jihar Neja, Yakubu Garba, zai ...
28/04/2025

Shin da gaske ne Mataimakin Gwamnan Neja, Yakubu Garba, Zai yi murabus?

Mataimakin Gwamnan jihar Neja, Yakubu Garba, zai yi murabus daga mukaminsa "kowane lokaci daga yanzu", majiyoyi da dama sun shaida wa wasu manema labarai.

A shirye-shiryen murabus din, majiyoyin sun ce mataimakin gwamnan da ke cikin rikici da Gwamnan jihar, Umar Bago, ya fara kwashe wasu kayansa daga Gidan gwamnati a karshen mako.

Wasu majiyoyi sun tabbatar wa manema labarai cewa sun ga yadda aka yi ta komowar kadarorin mataimakin gwamnan daga gidan gwamnati tsakanin Asabar da Lahadi.

Majiyar ta kara da cewa "Kamar yadda nake magana da ku, ya kwashe kayansa da yawa daga gidan gwamnati zuwa gidansa na kashin kansa.

Mun tattaro cewa wasu sarakunan gargajiya a jihar sun ziyarce shi a daren ranar Lahadin da ta gabata domin lallashin sa ya ajiye shirin murabus ɗin.

Sai dai babu tabbas ko Mista Garba ya sauya shawara bayan ziyarar sarakunan.

Masu lura da al’amura sun ce watakila matakin da mataimakin gwamnan ya dauka na yin murabus ba zai rasa nasaba da tabarbarewar dangantaka tsakanin sa da Gwamna Umaru Bago ba.

Hoto: Mataimakin Gwamnan Neja: Mista Yakubu Garba

Me ya sa Sarki Sunusi Lamido Sunusi bai halarci taron Sarakunan Arewa a Kaduna ba?An hangi Sarkin Kano Aminu Ado Bayero,...
26/04/2025

Me ya sa Sarki Sunusi Lamido Sunusi bai halarci taron Sarakunan Arewa a Kaduna ba?

An hangi Sarkin Kano Aminu Ado Bayero, a taron Sarakunan Arewa da ake gudanarwa a Gidan Gwamnatin Jahar Kaduna.

Rahotanni daga Birnin Kaduna na cewa Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ne ya halarci taron sarakunan Arewa da ke gudana a yau.

Ko me ya hana Sunusi Lamido Sunusi halartar taron?

Shin wanene halastaccen Sarkin Kano tsakanin Sunusi Lamido da Aminu Ado Bayero?

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AlMizan posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AlMizan:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share