07/01/2026
•Sheikh Jingir Ya Sake Taron Laraba, Ya Jagoranci Tsara Sabbin Ayyuka na Ci Gaban Kungiya
•A yau Laraba, kamar yadda aka saba a ko wane sati, Khalipha Ash-Sheikh Muhammadu Sani Yahaya Jingir ya sake tara jama'arsa a babban zauren tattaunawa domin ji daga gare su da kuma tsara sabbin ayyuka na ci gaban ƙungiyar.
•Taron, wanda ya gudana cike da natsuwa da nutsuwar malamai da almajirai, ya kasance wata dama ta musayar ra'ayi, nazari kan ayyukan da s**a gabata da kuma fitar da sabbin dabaru da zasu ƙara ƙarfafa tafiyar Ahlussunnah a faɗin ƙasa.
•Taron na yau ya kuma ƙunshi gabatar da bayanai daga manyan shugabanni da masu ruwa da tsaki, inda aka tattauna batutuwan da s**a shafi tsare-tsare, shirye-shiryen agaji, da kuma sabbin matakan wanzar da ilimi da tarbiyya tsakanin mambobi.
•Kamar yadda ya saba faruwa a kowace Laraba, taron ya kasance cike da albarka, fahimtar juna, da kuma kyakkyawar mu’amala tsakanin jagora da mabiyansa.
•A ƙarshe, Sheikh Jingir ya yi addu’ar Allah ya ƙara ɗaukaka aikin, ya sa alkhairi ya yawaita .
SURAJ JOURNALISt ✍️