13/08/2026
Tsohon Na Hannun Daman Kwankwaso Ya Fice Daga NDC Zuwa APC, Ya Bayyana Goyon Bayansa Ga Tinubu
Kabiru Adamu Abdullahi, wanda ya shafe shekaru yana tare da jagoran tafiyar Kwankwasiyya kuma ɗan takarar Mataimakin Shugaban Ƙasa na jam'iyyar Nigerian Democratic Congress (NDC), Rabiu Musa Kwankwaso, ya sauya sheƙa zuwa jam'iyyar All Progressives Congress (APC).
Kamar yadda Daily True Hausa ta tattaro, Abdullahi ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar NDC ne ta cikin wasiƙar murabus da ya aike wa shugaban jam'iyyar na mazaɓar Kofar Ruwa da ke ƙaramar hukumar Dala a Jihar Kano.
Abdullahi, wanda a farkon wannan shekara ya rantse da Alƙur'ani cewa Kwankwaso bai tura Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa APC ba, ya ce ya yanke shawarar barin NDC ne saboda abin da ya bayyana a matsayin cikar alƙawura da bai taɓa gani ba tsawon shekarun da ya yi a tafiyar.
Ya ce ya kwashe shekaru 29 tare da Kwankwaso, amma abin da ya samu shi ne alƙawuran da ba su cika ba.
«"Na yi shekaru 29 tare da Kwankwaso, amma ban amfana da komai ba face alƙawuran da ba su cika ba. Zan koma inda za a fi girmama ni," in ji Abdullahi.»
Ya kuma bayyana cewa daga yanzu zai mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya a ƙoƙarinsa na sake neman wa'adi ƙarƙashin inuwar jam'iyyar APC.
A cikin wasiƙar murabus ɗinsa, Abdullahi ya gode wa jam'iyyar NDC bisa damar da ta ba shi na yin hidima, tare da sanar da cewa murabus ɗinsa ya fara aiki nan take.