Daily True Hausa

Daily True Hausa GAME DA MU:

A Daily True Hausa, mun fahimci cewa gaskiya ba ta jin tsoro — mu ma haka muka ɗauki aikinmu.

(MANUFA) – BISA TSORON ALLAH DA KISHIN KASA:

Kare hakkin talakawa da masu rauni ta hanyar watsa gaskiya, ba wai abin da masu iko ke so a ji ba.

Zaben 2027: Wike ya yi kaca-kaca da masu kira da Jonathan ya sake tsayawa takaraMinistan Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana ...
18/09/2025

Zaben 2027: Wike ya yi kaca-kaca da masu kira da Jonathan ya sake tsayawa takara

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana cewa kira da wasu ke yi na dawo da tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan domin yin wa’adi ɗaya kacal a zaben 2027, ba komai ba ne illa neman jefa ƙasar cikin rikici.

Wike ya yi wannan furuci ne yana mai tunatar da cewa mutanen da ke taƙama da sunan Jonathan a yau, su ne ainihin waɗanda s**a rusa masa lissafi a zaben 2015.

“Duk wanda yake cewa Jonathan ya dawo saboda zai yi wa’adi ɗaya ne kawai, wannan mutum na neman rikici. Waɗannan su ne mutanen da s**a rusa shi a 2015. Me ya sa yanzu? Jonathan ya riga ya kafa suna a duniya, amma suna son su jawo shi cikin rikici marar amfani,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa tsohon shugaban ƙasar ya riga ya kafa tarihi a duniya ta fuskar dimokuraɗiyya da zaman lafiya, don haka bai kamata a yi amfani da sunansa a matsayin abin wasa a siyasar cikin gida ba.

Amurka ta kashe dala miliyan 500 wajen maye gurbin makaman da ta yi amfani da su wajen kare Isra’ila a yaƙi da IranTakar...
18/09/2025

Amurka ta kashe dala miliyan 500 wajen maye gurbin makaman da ta yi amfani da su wajen kare Isra’ila a yaƙi da Iran

Takardun kasafin kuɗi da Ma’aikatar Tsaron Amurka (Pentagon) ta fitar sun nuna cewa an ware kusan dala miliyan 498.3 domin maye gurbin makaman Terminal High Altitude Area Defence (THAAD) da aka yi amfani da su a yayin yakin da Amurka ta gudanar da Iran don kare Isra’ila.

Takardun, waɗanda aka sanya wa kwanan wata ranar 1 ga watan Agusta, sun bayyana wannan sauya kuɗi a matsayin “abu na musamman da majalisar dokoki ta nuna sha’awa” da kuma “gaggawar bukatar kasafin kuɗi”.

Jaridar tsaron Amurka, The War Zone, ita ce ta fara bayyana wannan bayanin a ranar Talata.

A baya, rahoton CNN na watan Yuli ya ruwaito daga wasu majiyoyi cewa Amurka na iya yin amfani da makaman THAAD tsakanin 100 zuwa 150 a cikin kwanaki 12 na yaƙin – abin da ya kai kusan kashi 25% na jimillar makaman da kasar ke da su.

Shehi Mai Tajul’izzi ya amsa gayyatar Hukumar Tace Fina-finai, Usman Mai Dubun Isa ya ki zuwaMawaƙin yabo, Shehi Mai Taj...
18/09/2025

Shehi Mai Tajul’izzi ya amsa gayyatar Hukumar Tace Fina-finai, Usman Mai Dubun Isa ya ki zuwa

Mawaƙin yabo, Shehi Mai Tajul’izzi, tare da lauyansa Abba Hikima, sun amsa gayyatar da Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta aika musu, biyo bayan zargin shirya muqabala ba bisa ka’ida ba.

Sai dai abokin karawarsa, Usman Mai Dubun Isa, ya yi watsi da gayyatar hukumar, lamarin da ya janyo cece-kuce a tsakanin magoya baya.

A lokacin da aka isa gaban hukumar, lauyan Tajul’izzi, Barr. Abba Hikima, ya bayyana wa shugaban hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, cewa hukumar ba ta da hurumin gayyatar mawakan ko kuma tuhumar su da aikata wani laifi dangane da shirya muqabala.

Hukumar dai na ci gaba da nazari kan yadda za ta tunkari wannan al’amari, yayin da jama’a ke sa ran matakin da za a dauka a nan gaba.

2027: Abba Kabir Bichi a matsayin mai raba gardama a takarar gwamnan Kano a APCDaga Bashari Habib TarauniKano ba ta da s...
18/09/2025

2027: Abba Kabir Bichi a matsayin mai raba gardama a takarar gwamnan Kano a APC

Daga Bashari Habib Tarauni

Kano ba ta da sauƙin siyasa. Duk wanda ya bi tarihin zabubbukan jihar ya san cewa babu wanda ke samun nasara cikin sauƙi. Jiha ce mai nauyin siyasa a Najeriya, kuma duk jam’iyyar da ta ci a nan ta samu rinjaye ne a kasa baki ɗaya.

Jam’iyyar APC ta dade tana da rinjaye a Kano. Amma yayin da 2027 ke ƙaratowa, akwai barazanar rikici a cikin gida. Wannan barazana ba wai saboda rashin manyan shugabanni ba ce, illa dai rikicin da ka iya kunno kai tsakanin sansanonin Sanata Barau Jibrin da Dakta Nasiru Yusuf Gawuna.

A gaskiya, dukkansu biyun jagorori ne da s**a cancanci girmamawa. Barau ya ɗaga darajar Kano a majalisar dattawa a matsayin mataimakin shugaban majalisa, yayin da Gawuna ya nuna jajircewa da kishin jam’iyya lokacin da ya riƙe tutar APC a zaben gwamna na baya. Amma siyasa ba wai kawai game da mutum ɗaya ba ce — haɗin kan magoya baya shi ne ginshiƙi.

A halin yanzu, wannan haɗin kai yana tangal-tangal. Rikici tsakanin magoya bayan Barau da Gawuna na ƙara tsananta, kuma hakan na iya karya jam’iyyar kafin zabe. Jam’iyyar adawa na jiran irin wannan dama.

Saboda haka, wajibi ne a nemo hanyar tsaka-tsaki. A wurina, wannan hanya ita ce Hon. Inj. Kabir Abubakar Bichi — dan majalisar da ke wakiltar mazabar Bichi kuma shugaban kwamitin kasafin kuɗi na Majalisar Wakilai.

Hon. Bichi bai nuna sha’awar takara ba, amma wannan ma na iya zama hujja. Ya nisanci rikici, ya mayar da hankali kan aikinsa a majalisa da hidima ga al’ummarsa. Siyasarsa ta ginu ne kan sauƙin kai, shiga jama’a, da ayyukan ci gaba, ba rikici da gaba ba.

A ƙarƙashinsa, Bichi ta samu sauyi — hanyoyi an shimfiɗa, wutar lantarki ta shiga ƙauyuka, ruwan sha ya samu ci gaba. Ya saka hannun jari a ilimi ta hanyar bayar da guraben karatu ga ɗaruruwan dalibai a gida da ƙasashen waje. A baya-bayan nan kuma ya kaddamar da aikin hasken rana a Asibitin Aminu Kano, abin da ya amfanar da dukan jiha.

Alherinsa ya zarce iyakokin mazabarsa. Mutane daga sassa daban-daban na Kano suna da labarin yadda ya taɓa rayuwarsu. Wannan irin nagartar shugabanci ce da APC ke bukata yanzu — mai haɗa kai, ba mai raba kai ba.

A bayyane yake cewa ba ana maganar watsar da Barau ko Gawuna ba. A’a. Dukansu ginshiƙai ne da ba za a iya yi watsi da su ba. Amma shigar da Hon. Bichi a matsayin zabin haɗin kai zai iya kawar da rikici da kuma tabbatar da cewa jam’iyyar ta je zabe da cikakken ƙarfi.

Kano tana da nauyi mai girma a siyasar Najeriya. Jam’iyyar da ta ci a nan za ta sami babban tasiri a kasa baki ɗaya. Saboda haka, APC ba za ta iya shiga 2027 da gida mai rarrabuwa ba. Idan hadin kai shi ne mabuɗin nasara, to Kabir Abubakar Bichi shi ne madadin da ya dace.

Simeone ya nemi afuwa kan martaninsa ga magoya bayan LiverpoolKocin Atlético Madrid, Diego Simeone, ya nemi afuwa kan ma...
18/09/2025

Simeone ya nemi afuwa kan martaninsa ga magoya bayan Liverpool

Kocin Atlético Madrid, Diego Simeone, ya nemi afuwa kan martaninsa ga magoya bayan Liverpool bayan rashin nasara da ƙungiyarsa ta yi a gasar Champions League a filin Anfield.

Liverpool ta doke Atlético da ci 2-1, inda Virgil van Dijk ya zura ƙwallo a minti na 92, abin da ya tayar da hayaniya tsakanin magoya bayan gida da Simeone.

Rahotanni sun bayyana cewa tun farkon wasa magoya bayan Liverpool sun rika yi wa Simeone zagi, lamarin da ya sa kocin ɗin ya fusata kuma ya yi martani lokacin da aka kammala wasa. Hukuma ta tsaka da wasa ta tilasta masa barin fili kai tsaye.

A cikin jawabinsa bayan kammala wasan, Simeone ya bayyana nadama:

> “Na yi kuskure da yadda na nuna martani. Bai dace da ni ba, kuma ban kamata in bari wannan ya faru ba.”

Sai dai kocin ya jaddada cewa wannan ba shi ne karo na farko da yake fuskantar cin mutunci daga magoya baya ba, yana mai cewa hakan ya fi dacewa a hukunta su fiye da barin su da ‘yanci na zagi.

Ana sa ran hukumar UEFA za ta duba lamarin tare da yiwuwar ɗaukar matakin ladabtarwa.

🚄 Aikin Jirgin Kasa Kaduna–Kano Ya Kai Kashi 53% — MinistaGwamnatin Tarayya ta bayyana cewa aikin gina jirgin kasa daga ...
17/09/2025

🚄 Aikin Jirgin Kasa Kaduna–Kano Ya Kai Kashi 53% — Minista

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa aikin gina jirgin kasa daga Kaduna zuwa Kano ya kai kashi 53 cikin 100 na kammaluwa.

Ministan sufuri, Saidu Ahmed Alkali, ya bayyana hakan a lokacin da yake duba aikin. Ya ce lokacin da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta karɓi mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023, aikin yana kan kashi 15% ne kacal, amma yanzu an samu gagarumin ci gaba.

A cewar ministan, an tsara cewa za a kammala aikin a shekarar 2026, domin tabbatar da cewa al’umma za su fara amfana da shi.

Layin jirgin, wanda ya kai tsawon kilomita 203, na daga cikin manyan muhimman ayyuka da ake aiwatarwa a Arewa maso Yamma, kuma yana daga cikin tsarin Standard Gauge.

Haka kuma, gwamnatin ta bayyana cewa an samu tallafin kuɗi daga China Development Bank domin gaggauta aiwatar da aikin.

Sai dai masana sun yi kira da a tabbatar an kammala aikin cikin lokaci, tare da tabbatar da inganci, domin ya kawo sauƙi ga sufuri da kasuwanci tsakanin Kaduna, Kano da sauran jihohin ƙasar.

🚨 A cewar MARCA, Vini Jr. na fuskantar wani yanayi mai ban mamaki a Real Madrid…▪️ Tun bayan tafiyar Ancelotti, rawar da...
17/09/2025

🚨 A cewar MARCA, Vini Jr. na fuskantar wani yanayi mai ban mamaki a Real Madrid…

▪️ Tun bayan tafiyar Ancelotti, rawar da yake takawa ta sauya karkashin tsarin “Xabi Alonso method.”

▪️ An riga an ajiye shi a benci sau biyu a wannan kakar, ciki har da wasan bude gasar Champions League da Marseille.

▪️ Mbappé ya zama jagoran tawaga babu gardama – shi ne mai bugun fenariti, mai lamba 10, kuma tauraron Santiago Bernabéu.

🇧🇷⚪ Bambanci ya bayyana: Vini ya rasa tasiri, har da murmushinsa na al’ada. Yadda jikinsa yake nuna ya nuna takaici, kuma shugabancinsa na motsa zuciya ya fara dusashewa.

Yayin da batun sabunta kwantiraginsa har yanzu bai kammala ba, dan Brazil din na fuskantar babban kalubale: ya sake gina kansa, ya tabbatar zai iya yin rayuwa tare da Mbappé, tare da dawo da farin cikinsa da zama mai tasiri a filin wasa.

🚨🚨 Shugaban La Liga, Javier Tebas, ya caccaki Real MadridShugaban gasar La Liga, Javier Tebas, ya yi martani kan koke-ko...
15/09/2025

🚨🚨 Shugaban La Liga, Javier Tebas, ya caccaki Real Madrid

Shugaban gasar La Liga, Javier Tebas, ya yi martani kan koke-koken Real Madrid game da yadda alkalai ke gudanar da wasanninta.

A cewarsa: “Real Madrid na kuka kan rashin adalcin alkalanci? Ku yi hattara da abin da kuke aikatawa da abin da kuke faɗa. A ganina, Real Madrid kawai na ƙoƙarin lalata martabar La Liga ne.” ⚪️⚠️

🚨🚨 Real Madrid ta ƙuduri aniyar kai ƙarar alkalai FIFAKungiyar Real Madrid ta bayyana cewa za ta shigar da rahoto a gaba...
15/09/2025

🚨🚨 Real Madrid ta ƙuduri aniyar kai ƙarar alkalai FIFA

Kungiyar Real Madrid ta bayyana cewa za ta shigar da rahoto a gaban hukumar kwallon ƙafa ta duniya, FIFA, kan abin da ta kira kuskuren alkalanci da ya jawo mata rashin adalci a wasanni daban-daban.

Rahoton, wanda gidan rediyon Cope ya rawaito, zai ƙunshi kwatancen kididdiga tsakanin Madrid da abokiyar hamayyarta Barcelona. A cewar rahoton, Madrid ta fi fuskantar matsala a bangaren jan katuna, bugun daga kai sai mai tsaron raga, laifuka, da maki da ta rasa saboda kurakuran alkalai.

Kungiyar ta dage cewa za ta nemi a duba lamarin domin tabbatar da adalci a gasar. ⚠️‼️

15/09/2025

👀

🛑 Da Dumi-Dumi: Kotu ta wanke Abdullahi Rogo daga zargin badakalar Naira biliyan 6.5Wata babbar kotu a Kano ta wanke Abd...
15/09/2025

🛑 Da Dumi-Dumi: Kotu ta wanke Abdullahi Rogo daga zargin badakalar Naira biliyan 6.5

Wata babbar kotu a Kano ta wanke Abdullahi Rogo, Daraktan Tsare-tsare (DG Protocol) na Gwamnan Jihar Kano, daga zargin da ake masa na badakalar kudi har Naira biliyan 6.5.

Alkalin kotun ya bayyana cewa ba a samu hujjojin da s**a isa da za su tabbatar da laifin da ake zargin Rogo da shi ba.

Wannan hukunci ya kawo ƙarshen shari’ar da ta jawo ce-ce-ku-ce a jihar, inda mutane da dama ke tattaunawa kan batun kudaden gwamnati.

15/09/2025

Takutawa a Kano, Shehi Ahmad Tajulizzi

Adresse

Dakar

Site Web

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Daily True Hausa publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Partager