Daily True Hausa

Daily True Hausa GAME DA MU:

A Daily True Hausa, mun fahimci cewa gaskiya ba ta jin tsoro — mu ma haka muka ɗauki aikinmu.

(MANUFA) – BISA TSORON ALLAH DA KISHIN KASA:

Kare hakkin talakawa da masu rauni ta hanyar watsa gaskiya, ba wai abin da masu iko ke so a ji ba.

Yadda Akai Kutsen Na’urorin Birnin Tehran Don Bibiyar Jagora Khamenei Kafin FarmakiRahoton wani bincike daga jaridar Fin...
03/03/2026

Yadda Akai Kutsen Na’urorin Birnin Tehran Don Bibiyar Jagora Khamenei Kafin Farmaki

Rahoton wani bincike daga jaridar Financial Times ya ce hukumomin leƙen asiri na Isra’ila sun shafe shekaru suna kutsa (hack) cikin kusan dukkanin k**arar zirga-zirga na birnin Tehran da kuma sadarwar wayar hannu don sanin lokaci da inda Khamenei ke kafin harin da ya kashe shi.

An ce k**ara-k**ara na zirga-zirga kusan gaba ɗaya an samu damar kallon hotunansu cikin sirri, an tura hoton zuwa sabobin sirri a Isra’ila don nazari.

Daga cikin waɗannan bidiyon, akwai na’ura (kamera) da ta nuna inda ma’aikatan tsaro ke ajiye motocinsu, wanda ya taimaka wajen sanin al’adar zirga-zirgar su.

Wannan ya ba da damar gina abin da ake kira “pattern of life” – wato cikakken bayanin yadda mutanen suke tafiyar da rayuwarsu da aikinsu

📱 Kutsen Sadarwa da Wayoyin Hannu

Baya ga k**ara, an ce an sami damar shiga sadarwar wayar hannu da sauran hanyoyin sadarwa don bibiyar motsi da sadarwar jami’an tsaro. Wannan ya taimaka wajen sanin rinjaye wurare da lokutan da Khamenei da tawagarsa ke amfani da su a dayansu na yau da kullum.

✈️ Dalilin Amfani da Wannan Bayanai

Rahoton ya bayyana cewa bayan tattara bayanai daga k**ara da wayoyi da sauran hanyoyi, hukumomin Isra’ila da na Amurka s**a sami tabbacin cewa Khamenei zai kasance a wani taron da aka shirya a wani lokaci da wurin da aka tantance, don haka s**a kammala shirye-shiryen harin da ya kashe shi.

Rahoton jaridar The Washington Post ya bayyana cewa shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi maganganu fiye da 30,000 da ba ...
28/02/2026

Rahoton jaridar The Washington Post ya bayyana cewa shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi maganganu fiye da 30,000 da ba su dace da gaskiya ba a lokacin da yake mulki daga shekarar 2017 zuwa 2021 zangon mulkinsa na farko

A cewar rahoton, hakan na nufin cewa a kowace rana Trump yana yin kusan magana 21 da ba su yi daidai da gaskiya ba.

Jaridar ta ce ta tattara wannan kididdiga ne bisa binciken da ta gudanar kan jawaban Trump a lokacin mulkinsa.

24/02/2026
Yadda Zaɓe Yake Wakana A Jihar Kano
21/02/2026

Yadda Zaɓe Yake Wakana A Jihar Kano

Kwaɗayi da Barazanar Rugujewar Yarjejeniyar 60/40Daga Ambasada Tijjani Habib YakawadaYanayin siyasar Jihar Kano ya shiga...
17/02/2026

Kwaɗayi da Barazanar Rugujewar Yarjejeniyar 60/40

Daga Ambasada Tijjani Habib Yakawada

Yanayin siyasar Jihar Kano ya shiga wani sabon mataki na rikice-rikice, yayin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ke fuskantar s**a da ƙalubale bayan sauya sheƙarsa zuwa All Progressives Congress (APC) tare da bullo da tsarin rabon iko na 60/40. Duk da bayanan da ke nuna cewa tsarin an kirkiro shi ne domin samar da daidaito da kwanciyar hankali a jam’iyya, rahotanni da alamu daga ƙasa na nuni da cewa tsarin na fuskantar zargin kwaɗayi da yunƙurin mamaye jam’iyya.

Masu ruwa da tsaki a APC, musamman ‘yan da aka fi sani da “Tsofaffin 'Yan Jam'iyya”, na zargin cewa bangaren Gwamnan na neman kashi 60% na dukkan tsarukan jam’iyya da muk**an gwamnati a matakan tarayya, jiha da ƙananan hukumomi. A cewarsu, hakan ya haifar da rashin yarda da rarrabuwar kai a cikin jam’iyyar.

Wannan rashin jituwa ta fito fili a taron tarba da aka gudanar a Sani Abacha Stadium a ranar 16 ga Fabrairu, 2026. Rahotanni sun nuna cewa yawancin mahalarta taron sun fito ne daga bangaren tsofaffin jiga-jigan APC, musamman magoya bayan Barau Jibrin, Engr. Abba Bichi da Baffa Babba Dan’Agundi. Masu sharhi na siyasa na ganin cewa gagarumar fitowar jama’a ta fi nuna ƙarfin Legacy APC fiye da tasirin sabon bangaren da ya shigo jam’iyyar.

A wani bangare kuma, ana zargin wasu masu rike da muk**ai a gwamnatin jihar da aiwatar da dabarar “zauna ka lalata”, wato ci gaba da rike mukami amma suna raunana tafiyar jam’iyya daga ciki. Wasu na danganta hakan da shawarwarin siyasa da tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bai wa magoya bayansa na ci gaba da zama a gwamnati domin rage tasirin tafiyar. Rahotanni sun nuna cewa hakan ya shafi mobilization da aka yi, inda aka kasa tara jama’a yadda aka tsara duk da ware kuɗaɗe masu yawa.

Bayanan da ke fitowa daga ƙananan hukumomi sun nuna cewa duk da shirin samar da bas-bas masu yawa domin ɗauko magoya baya, an kawo ƙasa da adadin da aka tanada. Wasu shugabannin ƙananan hukumomi sun danganta hakan da rashin biyayyar jama’a, inda ake cewa masu kaɗa ƙuri’a da dama sun ƙi bin su zuwa APC, s**a ci gaba da kasancewa tare da tafiyar Kwankwasiyya.

Sai dai wasu masu fafutukar jam’iyya sun ƙaryata hujjar da ake yadawa cewa jami’an tsaro ne s**a hana jama’a shiga filin taro, suna mai cewa tsarin ya tanadi shugabanni su raka mabiyansu kai tsaye. A cewarsu, matsalar ita ce rashin sahihin magoya baya daga sabon bangaren jam’iyyar.

Rikicin cikin gida ya ƙara bayyana bayan da Alhassan Ado Doguwa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Tudun Wada/Doguwa, ya nuna rashin amincewa da aiwatar da tsarin 60/40 a yankinsa. Masu sharhi na ganin wannan mataki a matsayin alama cewa ‘yan Legacy APC ba za su amince da duk wani tsari da zai tauye musu tasiri ba.

Bugu da ƙari, bayanan da s**a fito daga atisayen rajistar APC da aka kammala kwanan nan sun nuna cewa Gwamna Abba ya shigo jam’iyyar da ƙasa da kashi 20% na amintattun magoya bayan Kwankwasiyya. Rahotanni sun bayyana cewa yawancin wadanda s**a yi rajista a karkashinsa masu rike da muk**ai ne kawai, yayin da jama’ar ƙasa s**a nuna halin ko-in-kula.

Yayin da APC a Kano ke shirin tunkarar tarukan jam’iyya na Fabrairu da Maris, masana siyasa na gargadin cewa ci gaba da nuna kwaɗayi wajen neman rinjaye na kashi 60% na iya janyo rugujewar haɗin kai. A cewarsu, idan ba a gyara wannan tsari da wuri ba, akwai yiwuwar rikicin cikin gida ya ƙara tsananta, tare da barazanar lalata gindin jam’iyyar a jihar Kano.

Da ɗumi-ɗumi: Ribadu ya buƙaci El-Rufai ya gabatar da hujjar shigo da gubar thallium sulphate ga DSSOfishin Mai Bai Wa S...
15/02/2026

Da ɗumi-ɗumi: Ribadu ya buƙaci El-Rufai ya gabatar da hujjar shigo da gubar thallium sulphate ga DSS

Ofishin Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro (ONSA) ya umarci tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, da ya gabatar da hujjojin zargin da ya yi na shigo da sinadarin guba mai suna thallium sulphate ga Hukumar Tsaro ta DSS domin gudanar da cikakken bincike.

Majiyoyi sun shaida cewa wannan umarni na zuwa ne bayan El-Rufai ya yi zargin cewa an shigo da sinadarin gubar cikin ƙasar, lamarin da ya jawo damuwa a fannin tsaro da lafiyar al’umma.

Sinadarin thallium sulphate dai guba ce mai matuƙar haɗari wadda ba ta da launi ko ƙamshi, kuma ko da ƙananan ƙwayarta na iya haddasa mutuwa ga ɗan Adam idan aka yi amfani da ita ta hanyar da ba ta dace ba.
Ana sa ran matakin da ONSA ta ɗauka zai ba jami’an tsaro damar tantance sahihancin zargin, tare da ɗaukar matakan da s**a dace domin kare lafiyar jama’a da tsaron ƙasa.

Ganduje ya nemi a binciki ikirarin El-Rufai kan bacewar DadiyataTsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi...
14/02/2026

Ganduje ya nemi a binciki ikirarin El-Rufai kan bacewar Dadiyata

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi kakkausar s**a tare da yin watsi da zargin da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El‑Rufai, ya yi masa dangane da bacewar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.

A cikin wata sanarwa wadda tsohon Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Ciki na Jihar Kano, Kwamared Muhammad Garba, ya sanya wa hannu, tsohon Shugaban APC na kasa ya bayyana zargin a matsayin maras tushe, maras hujja, kuma sakaci ne da ke nufin karkatar da alhakin wani lamari da ya faru gaba ɗaya a Jihar Kaduna State.

Ya jaddada cewa Dadiyata ya rayu kuma ya gudanar da ayyukansa ne a Kaduna, inda aka san shi da yin s**a kai tsaye ga gwamnatin jihar a wancan lokaci. A cewarsa, babu wata shaida mai inganci da ke nuna cewa Dadiyata ya mayar da hankalinsa kan gwamnatin Jihar Kano State ko kuma kan Dr. Ganduje.

“Kowa a Kaduna ya san irin s**ar da yake yi da kuma inda yake nufi,” in ji shi, yana kara da cewa alhakin tsaro a wancan lokaci yana karkashin gwamnatin Jihar Kaduna tare da hukumomin tsaron tarayya da ke aiki a can.

Sanarwar ta bukaci a yi cikakken bincike da tantancewa kan kalaman El-Rufai na baya-bayan nan, tare da jaddada cewa irin wadannan manyan zarge-zarge dole ne su kasance bisa hujjoji masu tabbaci, ba maganganun siyasa kawai ba. Shigar da Ganduje cikin lamarin ba tare da shaida ba, a cewar Garba, yana siyasantar da wani lamari mai radadi da har yanzu bai warware ba, tare da kara rikitar da jama’a kan batun da tuni yake da sarkakiya.

Yana kwatanta yanayin siyasa a jihohin biyu a wancan lokaci, Garba ya bayyana cewa mulkin Ganduje na wa’adi biyu a Kano ya kasance bisa hakuri da karbar s**a, bude kofar kafafen yada labarai, da amincewa da ra’ayoyin adawa.

“Ba k**ar wasu shugabanni da ke da takaddama da kafafen yada labarai ba, a Kano mun yarda da bincike, mun karbi muryoyin masu s**a, har ma mun amfana da ra’ayoyin adawa,” in ji shi.

Tsohon Kwamishinan ya kara da cewa babu wani tarihi na k**a, tsoratarwa ko gallazawa ‘yan jarida ko masu s**ar gwamnati a Kano a lokacin mulkin Ganduje.

Ya kuma lura cewa tattaunawar jama’a kan bacewar Dadiyata tsawon shekaru ta fi karkata ne kan abubuwan da s**a faru a Jihar Kaduna. A wannan bangare, ya tunatar da cewa tsohon Sanata Shehu Sani ya taba bayyana cewa mutane da dama a jihar suna jin tsoron yin magana a bainar jama’a kan lamarin, yayin da mai sharhi Reno Omokri ya taba tayar da tambayoyi kan yadda aka tafiyar da batun a wancan lokaci.

Garba ya nuna damuwa kan ikirarin El-Rufai cewa wani dan sanda ya ce an turo shi daga Kano domin sace Dadiyata. Ya tambayi dalilin da ya sa, idan har bayanin yana da sahihanci, ba a gabatar da shi ga hukumomin bincike a hukumance ba ko kuma a bi hanyoyin tsaro na gaskiya a lokacin da abin ya faru.

“Yana da wahala a hada ikirarin rashin sanin mutumin da kuma yin cikakkun bayanai kan wanda ake zargi da daukar alhaki,” in ji shi.

Yayin da ya sake nuna tausayawa ga iyalan Dadiyata, Garba ya jaddada cewa abin da ya fi muhimmanci shi ne gano gaskiya ta hanyar doka, adalci da gaskiya.

“Iyalan suna bukatar samun kwanciyar hankali,” in ji shi. “Abin da ba su cancanta ba shi ne a maida wannan mummunan lamari kayan siyasar jifa da zargi.”

A karshe, ya yi kira ga duk wanda ke da sahihin bayani kan bacewar Dadiyata da ya gabatar da shi ga hukumomin da s**a dace, yana jaddada cewa alhaki da adalci dole ne su ginu ne bisa hujjoji da bin ka’ida, ba zato ko hasashe ba.

13/02/2026

Zaben 2027 zai k**a ne ana tsaka da azumin watan Ramadan - lokaci na ibada

11/02/2026

"Gombe ta Malam ce," in ji ɗan Sheikh Pantami

Wasu masu sharhi da masu ruwa da tsaki sun shawarci magoya bayan Malam Isa Ali Pantami da su fahimci cewa adawa wani ban...
11/02/2026

Wasu masu sharhi da masu ruwa da tsaki sun shawarci magoya bayan Malam Isa Ali Pantami da su fahimci cewa adawa wani bangare ne na siyasa, tare da jaddada cewa wanda ba zai iya jure s**ar ra’ayi ba, bai k**ata ya tsunduma cikin harkar siyasa ba.

Wannan martani ya biyo bayan kalaman wasu daliban Sheikh Pantami da s**a bayyana cewa “wakilan yahudawa ne ke adawa da Malam,” wani furuci da ya haifar da ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta.

Masu adawa da wannan magana sun bayyana cewa irin wadannan kalamai ba su taimaka wa tattaunawa mai ma’ana ba, kuma suna iya ƙara rarrabuwar kai a tsakanin al’umma. A cewarsu, siyasa fage ne na ra’ayoyi mabambanta, inda hujja da gaskiya ke rinjayar komai, ba zargi ko lakabi ba.

Sai dai daliban Sheikh Pantami na ganin cewa adawar da ake yi wa Malaminsu ba ta da tushe, kuma ana yin ta ne da wata manufa ta musamman, suna mai jaddada goyon bayansu gare shi a kowane hali.

Lamarin dai na ci gaba da janyo muhawara, inda jama’a ke kira da a fifita hujja, mutunci da fahimtar juna a cikin duk wata tattaunawa ta siyasa.

10/02/2026

‘Kafin Ya Zama Minista, Ya Yi Kuka Sosai’ - Sule Lamido Ga Pantami

Adresse

Dakar

Site Web

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Daily True Hausa publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Partager