TRT Afrika Hausa

  • Home
  • TRT Afrika Hausa

TRT Afrika Hausa Afirka, tsantsarta

A cewar Mataimakin Sakataren Ƙungiyar Marubuta Labarin Wasanni reshen jihar Kano, Muzzammil Dalha Yola, har yanzu a lig ...
13/08/2025

A cewar Mataimakin Sakataren Ƙungiyar Marubuta Labarin Wasanni reshen jihar Kano, Muzzammil Dalha Yola, har yanzu a lig ɗin Nijeriya babu zaƙaƙuran ’yan wasa da za su iya gogayya da takwarorinsu na sauran ƙasashen Afirka.

Masana harkokin wasanni a Nijeriya suna ganin Sudan ta cancanci jinjina saboda duk da yakin da ƙasar ke ciki, hakan bai sa ’yan wasanta sun karaya ba, inda s**a lallasa Super Eagles ta Nijeriya da ci 4 da nema a gasar CHAN.

Sabon tsarin Visa na Amurka na kallon duk wani dan kasashen Malawi da Zambia a matsayin ma hatsarin karya ka’idar kwanak...
13/08/2025

Sabon tsarin Visa na Amurka na kallon duk wani dan kasashen Malawi da Zambia a matsayin ma hatsarin karya ka’idar kwanakin zama, wanda daga yanzu za su dinga ajje dala 15,000 kafin su tafi kasar.

13/08/2025

Nijeriya ta fita daga Gasar CHAN 2024 ne saboda bayan ƙasar ta buga wasanni biyu da ta yi a rukunin D, ba ta zura ƙwallo a raga ba kuma ba ta da maki ko guda.

Duk da cewa Nijeriya tana da sauran wasa ɗaya da ya rage wanda za ta buga da Congo a ranar Talata mai zuwa, kusan za a iya cewa duk abin da ya faru a wasan ba zai sauya makomar ƙasar ba a gasar.

Fiye da yara 100 sun mutu saboda rashin abinci da tsananin yunwa a Gaza yayin da Isra'ila ta tsananta ƙawanyar da take y...
13/08/2025

Fiye da yara 100 sun mutu saboda rashin abinci da tsananin yunwa a Gaza yayin da Isra'ila ta tsananta ƙawanyar da take yi yankin, in ji shugaban hukumar Majalisar Dinkin Duniya mai kula da 'yan gudun hijirar Falasdinu (UNRWA).

Shugaban UNRWA, Philippe Lazzarini, ya ce an kashe dubban yara a hare-haren da Isra'ila ke kaiwa Gaza, sannan an mayar da yawansu marayu ko an firgita su.

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan ya soki rawar da Isra'ila ke takawa a rikicin baya-bayan nan a garin Sweida...
13/08/2025

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan ya soki rawar da Isra'ila ke takawa a rikicin baya-bayan nan a garin Sweida na Syria, inda ya bayyana damuwar Turkiyya game da tsoma bakin kasashen waje kan harkokin Syria.

Al shaibani, tare da Fidan, sun jaddada muhimmancin hadin kai kan tsaro da batutuwan soji don tsare iyakoki da yaki da ta’addanci.

Falasdinawa biyar, da s**a hada da yara biyu, sun mutu sak**akon yunwa a Gaza cikin sa'o'i 24 da s**a gabata, lamarin da...
13/08/2025

Falasdinawa biyar, da s**a hada da yara biyu, sun mutu sak**akon yunwa a Gaza cikin sa'o'i 24 da s**a gabata, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutum 227 da s**a hada da yara 103 daga yunwar da Isra'ila ta ƙaƙaba wa yankin tun daga watan Oktoban 2023.

Isra’ila tana tattaunawa da Sudan Ta Kudu game da yiwuwar mayar da Falasɗinawa masu yawa daga Gaza can, a wani ɓangare n...
13/08/2025

Isra’ila tana tattaunawa da Sudan Ta Kudu game da yiwuwar mayar da Falasɗinawa masu yawa daga Gaza can, a wani ɓangare na ƙoƙarin Isra’ila na tilasta musu ficewa daga yankinsu.
Babu tabbacin irin nisan da aka yi wajen tattaunawar, amma idan hakan ya tabbata, to zai kasance tamkar sauya wa mutane wajen zama daga waje mai hatsari da ke fama da yunwa zuwa wani wajen mai irin wannan matsalar.
👉https://trt.global/afrika-hausa/article/71b1865a94c7

Rundunar Sojin Saman Nijeriya ta ce hare-haren, waɗanda s**a ƙunshi tashin jiragen yaƙi sau 798, sun yi nasarar rage ƙar...
13/08/2025

Rundunar Sojin Saman Nijeriya ta ce hare-haren, waɗanda s**a ƙunshi tashin jiragen yaƙi sau 798, sun yi nasarar rage ƙarfin mayaƙan ISWAP da Boko Haram sosai a arewa maso gabashin Nijeriya.
👉🏿 https://trt.global/afrika-hausa/article/c241eb71bcf6

Address

Ahmet Adnan Saygun Cd

34347

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TRT Afrika Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share