TRT Afrika Hausa

TRT Afrika Hausa Afirka, tsantsarta

A ranar Laraba, Ma'aikatar Lafiya a Gaza ta ba da rahoton cewa rundunar sojin Isra'ila ta kashe Falasɗinawa 25 kuma ta r...
20/11/2025

A ranar Laraba, Ma'aikatar Lafiya a Gaza ta ba da rahoton cewa rundunar sojin Isra'ila ta kashe Falasɗinawa 25 kuma ta raunata 77 a jerin hare-hare kan wasu yankuna da Isra'ila ta riga ta janye daga cikinsu, abin da hukumomin Falasɗinawa s**a ce keta yarjejeniyar tsagaita wuta ce.

Hukumar Tsaron Al'umma ta Falasɗinu a Gaza ta ce an zaƙulo mutum 3 daga iyalai biyu a cikin ɓaraguzai, sannan an jikkata aƙalla wasu mutane 15 a Khan Younis, a kudancin Gaza.

20/11/2025

Maroko ta mamaye kyautukan Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka ta Gwarazan CAF 2025, inda aka bayyana Achraf Hakimi a matsayin Gwarzon Dan Wasan Afirka na Bana, wanda ya zama ɗan baya na farko da ya lashe kyautar a cikin shekaru 52.

Ghizlane Chebbak, ita ma 'yar Maroko, ita ce aka bayyana a matsayin Taurauwar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka ta Mata ta Bana, kuma ita ma ta kafa tarihin kasancewa mace ta farko da ta lashe kyautar tun 2001.

Maroko ta lashe kyautuka shida, abin da sa ta zama mafi yawan da wata ƙasa ta lashe a nahiyar.

Jirgin yana kan hanyarsa ta zuwa babban birnin kasar, Kinshasa, daga tashar Bena Dibele, da ke da nisan fiye da kilomita...
20/11/2025

Jirgin yana kan hanyarsa ta zuwa babban birnin kasar, Kinshasa, daga tashar Bena Dibele, da ke da nisan fiye da kilomita 800 lokacin da ya nutse a ranar Litinin a kogin Sankuru, sak**akon guguwa, a cewar gidan rediyon Majalisar Dinkin Duniya.

Kafofin watsa labarai na cikin gida sun ce jirgin yana ɗauke da kimanin mutum 120, kuma daga cikinsu kimanin 50 kawai aka iya cetowa kawo yanzu.

Wata Babbar Kotun Tarayya a Abuja babban birnin Nijeriya ta yanke hukuncin ɗaurin shekara 20 ga mutumin da ya tsara hare...
20/11/2025

Wata Babbar Kotun Tarayya a Abuja babban birnin Nijeriya ta yanke hukuncin ɗaurin shekara 20 ga mutumin da ya tsara hare-haren ta’addanci da aka kai a Kano a watan Janairun 2012.

Mai shari’a Justice Emeka Nwite ya yanke wa Hussaini Isma’ila da aka fi sani da Mai Tangaran hukuncin ne bayan ya amasa tuhume-tuhumen da Hukumar Tsaron Farin kaya ta DSS ta gabatar a kansa.

Mai shari’ar ya bayyana cewa hukuncin zai fara aiki ne tun daga lokacin da aka k**a shi a 2017.
https://www.trtafrika.com/hausa/article/f2e504a5fef6

20/11/2025

Wata gagarumar gobara ta tashi a wata masana'atar sarrafa auduga a yankin Beni Suef na Masar, wacce ta haifar da mummunar asara.

Jami'an tsaron al'umma da jama'ar gari sun samu nasarar kashe gobarar.

Yayin da aka tuna da ranar da Kwazarin Victoria Falls ya cika shekaru 170 bayan Livingstone ya gano wurin, 'yan Zimbabwe...
19/11/2025

Yayin da aka tuna da ranar da Kwazarin Victoria Falls ya cika shekaru 170 bayan Livingstone ya gano wurin, 'yan Zimbabwe na dasa ayar tambaya kan wanda ke da ikon bayyana ganowar wurin.

Yayin da aka yi tuni da ranar da kwazarin Victoria Falls ya cika shekaru 170 bayan Livingstone gano wurin, 'yan Zimbabwe aza ayar tambaya kan wanda ke da ikon bayyana ganowar wurin da kuma dalilin da yasa yake ɗauke da sunan sarauniyar Birtaniya

Masu sharhi na cewa ganin yadda a koyaushe Turkiyya ke goyon bayan abokanta da 'yan'uwanta na Sudan kuma ta yi kokari so...
19/11/2025

Masu sharhi na cewa ganin yadda a koyaushe Turkiyya ke goyon bayan abokanta da 'yan'uwanta na Sudan kuma ta yi kokari sosai don kawo karshen rikice-rikicen da ke faruwa a kasar, to ya zama wajibi a maye gurbin UAE da Turkiyya a cikin kungiyar kasashen "Quartet" don samar da zaman lafiya a Sudan.

Dole ne kasashen duniya su dauki matakan da s**a dace don kubutar da Sudan da jama’arta daga RSF da masu goya musu baya na kasashen waje.

Kungiyar agaji ta kasar Switzerland, Public Eye ta zargi kamfanin Nestle da yin munafunci inda ta ce kamfanin na sayar d...
19/11/2025

Kungiyar agaji ta kasar Switzerland, Public Eye ta zargi kamfanin Nestle da yin munafunci inda ta ce kamfanin na sayar da abincin jarirai a Afirka da ke dauke da s**ari mai yawa fiye da wanda ke cikin kasuwannin ƙasashen da s**a fi ci gaba, ikirarin da Nestle ta bayyana zargin a matsayin mai ruɗani kuma marar tushe.
👉🏻 https://www.trtafrika.com/hausa/article/4f4ed4daf869

19/11/2025

Wani mutum ya yi ƙoƙarin ƙona kwafin Alƙur'ani a yayin da yake zanga-zangar nuna ƙiyayya ga Musulunci a Dearborn, Michigan - birni da ke ɗaya daga cikin mafi yawan al'ummar Musulmi a Amurka. 'Yan sanda sun shiga tsakani cikin gaggawa, kuma wani da ke wajen ya shiga tsakani kafin lamarin ya ƙara ta'azzara.
Lamarin ya jawo s**a mai ƙarfi daga jami'an yankin.

Matashin ɗanwasan Real Madrid, Franco Mastantuono ya bayyana yadda yake fama da cutar matsematsi ta Pubalgia, irin wadda...
19/11/2025

Matashin ɗanwasan Real Madrid, Franco Mastantuono ya bayyana yadda yake fama da cutar matsematsi ta Pubalgia, irin wadda Lamine Yamal ke fama da ita, inda ya yi bayani kan yadda cutar take kawo masa cikas tun makonnin baya bayan nan. 👇🏻
https://www.trtafrika.com/hausa/article/88ea5901b5ba

Majalisar Dattawan Nijeriya ta yi kira ga rundunar sojin ƙasar da ta ɗauki ƙarin sojoji 100,000 domin magance matsalar r...
19/11/2025

Majalisar Dattawan Nijeriya ta yi kira ga rundunar sojin ƙasar da ta ɗauki ƙarin sojoji 100,000 domin magance matsalar rashin tsaro a sassan ƙasar, sannan ta kafa wani kwamiti na wucin gadi don yin bincike kan warewa da kashe kuɗi don shirin kare makarantu. 👇🏻
https://www.trtafrika.com/hausa/article/168357e1e5cf

Address

Ahmet Adnan Saygun Cd
Istanbul
34347

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TRT Afrika Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share