TRT Afrika Hausa

TRT Afrika Hausa Afirka, tsantsarta

Sojojin Isra'ila sun karɓe iko da wayoyin Falasdinawa a Gaza domin don tilasta musu sauraron jawabin Firaminista Benjami...
26/09/2025

Sojojin Isra'ila sun karɓe iko da wayoyin Falasdinawa a Gaza domin don tilasta musu sauraron jawabin Firaminista Benjamin Netanyahu da ya yi a gaban Babban Taron Majalisar Dinkin Duniya kai-tsaye.

Sanata Rabiu Kwankwaso ya yi kira ga 'yan Nijeriya su guji amincewa da duk wani bayani da ya shafi harkokin siyasarsu mu...
26/09/2025

Sanata Rabiu Kwankwaso ya yi kira ga 'yan Nijeriya su guji amincewa da duk wani bayani da ya shafi harkokin siyasarsu muddin ba ta hanyar da s**a saba sanar da jama'a ya fito ba.
Rahotanni dai sun daɗe suna cewa ɗan takarar na Jam'iyyar NNPP a zaɓen shugabancin Nijeriya 2023 yana shirin komawa Jam'iyyar APC mai mulki.

Hedkwatar tsaron Nijeriya ta ce dakarunta sun k**a masu aikata laifuka fiye da 120 ciki har da mutum 26 da ke taimaka wa...
26/09/2025

Hedkwatar tsaron Nijeriya ta ce dakarunta sun k**a masu aikata laifuka fiye da 120 ciki har da mutum 26 da ke taimaka wa ‘yan ta’adda, sannan sun kuɓutar da mutane 41 da aka yi garkuwa da su a faɗin ƙasar tsakanin 14 zuwa 22 ga watan Satumba.

A arewa maso gabashin Nijeriya, dakarun Operation Hadin Kai sun kuɓutar da mutum uku da aka yi garkuwa da su kuma s**a k**a masu taimaka wa ‘yan ta’adda 26 tare da kashe mayaƙan Boko Haram a Jihohin Borno da Yobe da kuma Adamawa.

Kun san irin zaluncin da Faransa ta kwashe shekaru aru-aru tana tafkawa a fannin hakar uranium na Jamhuriyar Nijar? Ku k...
26/09/2025

Kun san irin zaluncin da Faransa ta kwashe shekaru aru-aru tana tafkawa a fannin hakar uranium na Jamhuriyar Nijar?
Ku kalli bidiyon nan game da binciken da TRT ta gudanar kan wannan lamari👇🏾

Gabanin juyin mulkin da aka yi a Nijar ranar 27 ga Yulin 2023, Faransa ta mamaye arzikin uranium na kasar Nijar, ba ya ga mamayar da ta yi wa kasar a fannin ...

Trump ya jinjina wa Shugaban Turkiyya inda ya bayyana shi a matsayin “mutumin da ake matuƙar girmamawa”, inda ya ce ana ...
25/09/2025

Trump ya jinjina wa Shugaban Turkiyya inda ya bayyana shi a matsayin “mutumin da ake matuƙar girmamawa”, inda ya ce ana son Erdogan matuƙa a ƙasarsa da nahiyar Turai da duniya baki ɗaya”.

25/09/2025

Nijar ta zama mamba a kwamitin gudanarwa na hukumar kula da mak**ashin nukiliya ta duniya (IAEA), matakin da ake ganin wata babbar nasara ce ta diflomasiyya ga ƙasar da ke samar da sinadarin uranium. Matsayin ya biyo bayan zaɓen da aka gudanar a ranar Jumma’a 19 ga watan Satumba a ƙarshen taron hukumar IAEA karo na 69 a Vienna, k**ar yadda kafar watsa labarai ta ActuNiger ta ambato hukumomin ƙasar suna bayyanawa ranar Talata.

An yanke wa sojojin hukuncin laifuka da dama, da s**a hada da sata, da yin mu’amala da harsasai ba bisa ƙa’ida ba, da ku...
25/09/2025

An yanke wa sojojin hukuncin laifuka da dama, da s**a hada da sata, da yin mu’amala da harsasai ba bisa ƙa’ida ba, da kuma taimaka wa ‘yan ta’adda wadanda duk hukuncinsu ke karkashin dokar kotun.

An yanke wa sojojin hukuncin laifuka da dama, wadanda s**a hada da sata, da yin mu’amala da harsasai ba bisa ƙa’ida ba, da kuma taimaka wa ‘yan ta’adda wadanda duk hukuncinsu ke karkashin dokar kotun sojin Nijeriya

Wata kotu a birnin Paris ta yanke wa tsohon shugaban kasar Faransa, Nicolas Sarkozy hukuncin ɗaurin shekaru biyar a gida...
25/09/2025

Wata kotu a birnin Paris ta yanke wa tsohon shugaban kasar Faransa, Nicolas Sarkozy hukuncin ɗaurin shekaru biyar a gidan yari a ranar Alhamis.
Hakan na zuwa ne bayan da kotu ta same shi da laifi kan zargin da ake masa cewa tsohon shugaban Libiya, Muammar Gaddafi, ya taimaka wajen daukar nauyin yakin neman zabensa na 2007 wanda ya kai shi ga nasara.
🔗 https://www.trtafrika.com/hausa/article/06d15b647119

Ta bayyana haka ne a ranar Laraba a lokacin da take magana a wajen buɗe baje-kolin “Zero Waste Blue—Drop by Drop” a birn...
25/09/2025

Ta bayyana haka ne a ranar Laraba a lokacin da take magana a wajen buɗe baje-kolin “Zero Waste Blue—Drop by Drop” a birnin New York, inda ta ce ƙoƙarin da Turkiyya ke yi a kan muhalli ana yin sa ne don amfanin dukkan bil’adama.
🔗 https://www.trtafrika.com/hausa/article/6c334ced4482

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima ya yi magana kan batutuwan da s**a haɗa da bai wa Falasɗinu 'yanci da sama...
25/09/2025

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima ya yi magana kan batutuwan da s**a haɗa da bai wa Falasɗinu 'yanci da samar wa Nijeriya kiujerar dindindin a Kwamitin Tsaro na MDD da kuma neman a yafe wa ƙasashen Afirka basuss**a.

Ya ce MDD za ta sake samun ƙimarta ne kawai idan ta nuna yadda duniya take a halin yanzu, ba yadda take a da can ba.

Address

Ahmet Adnan Saygun Cd
Istanbul
34347

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TRT Afrika Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share