S jazuga na futuhi tv

S jazuga na futuhi tv Ahamadu yarwa abul futuhati wallahi kai nakeso soyayyar da baza ta iiguba shi ya sa nace da ga kai

LABARI MAI DAƊI: Gwamnatin Saudiyya ta Amince Ayi Zagayen Mauludin Murnar Ranar Zagayowar Haihuwar Fiyayyan Halitta Anna...
09/09/2025

LABARI MAI DAƊI: Gwamnatin Saudiyya ta Amince Ayi Zagayen Mauludin Murnar Ranar Zagayowar Haihuwar Fiyayyan Halitta Annabi Muhammadu SAW a duk faɗin ƙasar.

A karon farko, Gwamnatin Saudiyya ta amince a fara gudanar da zagayen murnan haihuwar MANZON ALLAH SAW a biranen Makka Madina da Riyad, duk da cewa ba'a kira taron zagayen, da sunan Mauludi ba amma an bayyana shi a matsayin murnar zagayowar watan da aka haifi ANNABI SAW, yau an yi a Madina, gobe za a gudanar da zagayen a birnin Riyad, a ƙarƙare a Makka.

Yin Mauludi Ta Hanyar Da Ya K**ata Abu Ne Mai Kyau K**ar A Masallatai Da Islamiyyu, Domin Cusawa Yara Kaunar Annabi SAW,...
08/28/2025

Yin Mauludi Ta Hanyar Da Ya K**ata Abu Ne Mai Kyau K**ar A Masallatai Da Islamiyyu, Domin Cusawa Yara Kaunar Annabi SAW, Inji Sheikh Kabir Gombe

"Tsakani da Allah babu wanda zai ce wannan manufar ba abu ne mai kyau ba, manufar tana da kyau", cewar Shehin Malamin.

ABUBUWA GUDA HUDU SUNA JANYO BUDEWAR KOFOFIN ARZIKI :1. TSAIWAR DARE (Qiyamul Layl) : Manzon Allah (saww) ya nuna mana M...
08/22/2025

ABUBUWA GUDA HUDU SUNA JANYO BUDEWAR KOFOFIN ARZIKI :

1. TSAIWAR DARE (Qiyamul Layl) : Manzon Allah (saww) ya nuna mana Muhimmancin Tsaiwar dare ya ce tana janyo ma mutum samun girman matsayi awajen Allah. Kuma duk wanda ya hana idonsa barci cikin dare don neman yardar Allah, Shi kuma Allah zai faranta zuciyarsa da rana.

2. ISTIGHFARI : Allah ya bamu labarin abinda Annabi Nuhu (as) yake gaya ma Mutanensa. Yace :

"NACE (MUSU) KU NEMI GAFARAR UBANGIJINKU DOMIN SHI MAI GAFARA NE. ZAI SAUKAR MUKU DA RUWA DAGA SAMA, KUMA QAREKU DA DUKIYA DA 'YA'YA, KUMA ZAI SANYA MUKU GONAKI KUMA ZAI SANYA MUKU QORAMU (Wato albarkacin Istighfarin nan Allah zai gafarta zunubanku, kuma zai yalwata arzikinku ta fuskar 'ya'ya da dukiya da gonakai da Qoramu da kuma ruwan sama mai albarka.

Manzon Allah (saww) yace duk wanda ya yawaita Istighfari Allah zai yaye masa damuwarsa kuma zai azurtashi ta inda ba ya tsammani.

3. SADAQAH : Sadaqah itama babbar hanyar budewar kofofin Arziki ne. Domin kuwa Allah yana cewa :

"IDAN KUKA BAMA ALLAH RANCHE, RANCHE MAI KYAWU, TO ZAI NINNINKASHI GAREKU KUMA ZAO GAFARTA MUKU.. ".

Kuma yace "DUK ABINDA KUKA CIYAR NA WANI ABU, TO (ALLAH) SHI ZAI NINKASHI KUMA SHINE MAFI ALKHAIRIN MASU AZURTAWA".

4. ZIKIRIN ALLAH : Zikirin Allah, Karatun Alqur'ani da Salatin Manzon Rahama (saww) su ke Sanya zuciya ta samu nutsuwa azahiri da badini. Kuma ta hanyar zikirin Allah mutum yana samun yayewar Talauci da Qunci. Kuma yana samun kusanci da Allah da jibintar lamarinsa aduniya da lahira.

Allah yasa mu dace da samun wadannan falaloli. Allah ya yaye mana Quncin rayuwa, ya Qara rufa asiranmu aduniya da lahira Ameeen.

IDAN KAJI DADI KATURA A GROUP 7 ZUWAGA MASOYA ANNAB ﷺ ALLAH YAKARA MANA SON ANNABI MUHAMMADU ﷺ
ALLAH.

SHEHU TIJJANI ABUL ABBAS RTA YAGA ANNABI SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAM QURU QURU YA BASHI SALATUL FATIH A duba Cikin SAHIH...
08/18/2025

SHEHU TIJJANI ABUL ABBAS RTA YAGA ANNABI SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAM QURU QURU YA BASHI SALATUL FATIH

A duba Cikin SAHIHU MUSLIM

acikin sahih Muslim manzan Allah صلى الله عليه وسلم yace

ﻣﻦ ﺭﺁﻧﻰ ﻓﻰ ﺍﻟﻤﻨﺎﻡ فسيراني ﻓﻰ ﺍﻟﻴﻘﻈﺔ »»

"Wanda ya ganin a Cikin bacci da sannu zai ganni kuru kuru"

Ashe ana ganin annabi Muhammad ﷺ a farke to dalilin da ya jawo Shehu tijjani RTA yaga annabi Muhammad صلى الله عليه وسلم
A farke kenan, manzan Allah ya bashi salatul fatih da falalarta yace ya riqe

alaji ko Jakine Kai karatun jiya ya fita fess wannan sashin bayanin imam ABULFATHI SANI ATTIJANY ne

Abinda Annabi Sayyidina Rasulullahi ﷺ ya ce game da muhimmancin kyawawan ɗabi'u shi ne:"Babu abin da yafi nauyi a kan mi...
08/17/2025

Abinda Annabi Sayyidina Rasulullahi ﷺ ya ce game da muhimmancin kyawawan ɗabi'u shi ne:

"Babu abin da yafi nauyi a kan mizani na ayyukan alheri a Ranar Alƙiyama fiye da kyawawan ɗabi'u."

(Sunan, 4781)

Ku biyo mu don ci gaba da kasancewa tare.

Wata Rana Abdullahi Bn Salaam('Daya Daga Cikin Yahudawan Madina) Ya Zo Wajen MA'AIKI(S.A.W) Ya Ce Da Shi:"Na Zo Ne Domin...
08/16/2025

Wata Rana Abdullahi Bn Salaam('Daya Daga Cikin Yahudawan Madina) Ya Zo Wajen MA'AIKI(S.A.W) Ya Ce Da Shi:"Na Zo Ne Domin Na Yi Maka Wasu Tambayoyi Guda Uku(3) Wadanda Babu Wanda Ya San Amsarsu Idan Shi Ba Annabi Bane:
;
1. Shin Menene Farkon Sharadin Tashin Alqiyamah???

2. Shin Menene Farkon Abincin Da 'Yan Aljannah Zasu Ci???

3. Shin Menene Yasa Wani Lokaci Idan Aka Haifi Yaro Ya Kan Yi K**a Da Ubanshi, Wani Lokacin Kuma Uwarshi???
:
Sai ANNABI(S.A.W) Ya Ce Da Shi:"Yanzun Nan Mala'ika Jibrilu(A.S) Ya Zo Ya Bani Labarin Amsoshin Tambayoyin Nan Naka".
;
Sai Bn Salaam Ya Ce:"Mala'ika Jibrilu???"
;
ANNABI(S.A.W) Ya Ce:"Eh"
;
Bn Salam Ya Ce:"Ai Mala'ika Jibrilu Shi Ne Makiyin Yahudawa".
;
Sai ANNABI(S.A.W) Ya Karanto Masa Wannan Ayar Da Take Cewa:"Man Kana Aduwan Lillahi Wa Mala'ikatihi Wa Jibrila Wa Minkala Fa'inallaha Aduwan Lilkafiriin".
;
Sannan Ya Bashi Amsoshin Tambayoyinsa K**ar Haka:
;
1. Farkon Sharadin Tashin Qiyama Wata Wuta Ce Wacce Zata Koro Mutane Tun Daga Inda Rana Take 'Bullowa Har Zuwa Inda Take Fad'uwa
2. Farkon Abincin Da 'Yan Aljannah Zasu Ci Shi Ne Hantar Wani Kifi,
3. Idan Maniyyin Namiji Ya Riga Na Mace Sauka, To Sai Yaron Ya Zama Yana K**a Da Shi(Uban), Idan Kuma Na Macen Ne Ya Riga Sauka, To Sai Yaron Yayi K**a Da Ita(Uwar).
;
Daga Wannan Lokacin Sai Abdullahi Bn Salam Wanda Ada Shi Ne Mafi Alkhairin Yahudawa Kuma 'Dan Shugaban Yahudawan Ya Ce:"Na Shaida Babu Abin Bautawa Da Gaskiya Sai ALLAH, Kuma Haqiqa Kai MANZON ALLAH Ne,
;
Ya RASULALLAHI! Haqiqa Yahudawa Mutane Ne Masu 'Kage Da Sharri Ne, Idan S**a San Cewa; Na Musulunta Tun Kafin Ka Tambaye Su Game Da Ni, To Tabbas Zasu Yi Min Sharri Da 'Kage",
:
Da Sauran Yahudawan S**a Zo Sai MANZON ALLAH(S.A.W) Ya Tambaye Su Cewa:"Shin Menene Matsayin Abdullahi Bn Salaam a Cikinku???"
;
Sai S**a Ce:"Shi Ne Mafi Alkhairin Cikinmu, Kuma 'Dan Gidan Mafi Alkhairin Cikinmu, Kuma Shi 'Dan Shugaba Ne",
;
ANNABI(S.A.W) Ya Ce:"Shin Yaya Kuke Gani Idan Shi Ya Musulunta???"
;
Sai S**a Ce:"ALLAH Ya Tsare Shi Ba Zai Ta6a Musulunta Ba".
;
Jin Hakan Ke Da Wuya Sai Abdullahi Bn Salaam(R.A) Ya Fito Daga Inda Yake 'Boye Ya Ce:"Ash-Hadu An La'Ilaha Illallahu Wa Anna Muhammadur Rasulullahi".
;
Daga Jin Hakan Sai Yahudawan S**a Ce:"Ai Wannan Shi Ne Mafi Sharrin Cikinmu Kuma 'Dan Gidan Mafi Sharrin Cikinmu".
;
Sai Bn Salaam(R.A) Ya Ce:"Ya RASULULLAHI! Ka Ga Abin Da Nake Tsoro Kenan Tun Farko; Sharrin Bakinsu".
;
Sayyiduna Abdullahi Bn Salaam(R.A) Ya Musulunta Kuma Musulunci Yayi Armashi Sosai Harma Ya Kasance 'Daya Daga Cikin Malaman Sahabban ANNABI(S.A.W).
:
Ya ALLAH! Ka Yi Dadin Tsira, Sallama Da Salati Ga Mijin Khadija Angon A'isha, Abul Qaseem Abban Fatima, Wanda Ka Aiko Shi Domin Ya Kasance Rahama Ga Dukkan Talikai.
:
ALLAH YA 'KARA MANA SOYAYYAR SHI(S.A.W) AMEEEEEN.

SHIN DA GASKE SHEHU IBRAHIM YA KIRA KANSA ALLAH?An tambayi Baba Lameen RTA  Shin Dagaske ne Shehu Ibrahim RTA  ya kira k...
08/16/2025

SHIN DA GASKE SHEHU IBRAHIM YA KIRA KANSA ALLAH?

An tambayi Baba Lameen RTA Shin Dagaske ne Shehu Ibrahim RTA ya kira kanshi Allah kamar yadda ake faɗi?

Shehu laminu Yace: Hakika duk me irin wannan maganar baisan wanene Shehu Ibrahim ba.

Duk Narkewar Shehu Ibrahim a Allah bai taɓa Shafe Allah ya tabbatar da Kansa ba, Saboda irin Tarbiyyarsa Sai dai ya shafe kanshi ya tabbatar da Allah, Domin daman shine tabbatacce K**ar yanda yazo cikin Al-Qur’ani.

Da yawan masu shafe Allah su tabbatar da Shehu ba suma San wanene Shehu ba, Domin a karatun da sukeyi a Tarbiyya lallai zasu iya sanin wanene Tabbatacce

Shin ko sun manta Shehu Ibrahim yazo cikin Kaunu yayi Rayuwa da Jasadinsu tsawon Shekara 75 kuma yayi Aure ya haifi ƴaƴa 75 Sannan Yayi Hajji da Umrah sau 75 haka kuma Ya Ziyarci Kasashe 75 kuma ya rubuta littafai 75, Shin kodai masu wanchan Shashancin Sheɗan suke nufi ba Shehu ba An tambayi wani Baƙo a Senegal mai irin wannan ɗabi’a ta cewa Shehu Ibrahim Allah ne. Lokacin da s**a shigo Senegal za’ayi Sallah Sai yayi ta mamaki daman anayin Sallah a gidan Shehu ?

Bayan an idar da Sallah Sai yaga Anyi Da’ira Ana Zikirin Juma’ah, Nanma mamaki ya kamashi Ashe anayin Zikirin Juma’a a gidan Shehu?

Ranar Litinin Bayan sun gama Wazifa sai yaga an kawo kayan shan Ruwa ga waɗanda s**ai Azumin Litinin Nanma ya cika da mamaki domin shi ko Ramadan ma ba yayi

Saida aka gama komai sai yaje ya samu Shehu Mahy Cisse yake gaya masa irin yadda Shehin sa ya tarbiyantar dashi akan Shafe Dukkan waɗannan Sharuɗɗa na Musulunci Sai Shehu Mahy yace masa Haƙiƙa Shehinka Wakilin Shaiɗan ne Ba Wakilin sheikh Ibrahim Niasse ba.

Domin duk Duniya babu Gidan da yakai Gidan Shehu koyar da dukkan Abinda musulunci yazo dashi Hasalima a gidan Shehu Sunnah takan zama Farillah Farillah Takan zama Rayuwa

❤️🄵🄾🄻🄻🄾🅆 🄼🄴 ❤️ 🌺∙──༅༎﷽༎༅──∙🌺              ❤️❤️❤️ The Ancient 4,500-Year-Old Tunic at the Egyptian Museum.               ...
08/14/2025

❤️🄵🄾🄻🄻🄾🅆 🄼🄴 ❤️
🌺∙──༅༎﷽༎༅──∙🌺
❤️❤️❤️

The Ancient 4,500-Year-Old Tunic at the Egyptian Museum.


Wahabiyawa ga Shawara kudaina Shiga Sabgar Malamin mu Domin Ina Son kusani Malamin mu ba Sa'ar k bane, eheZakin faidah d...
08/14/2025

Wahabiyawa ga Shawara kudaina Shiga Sabgar Malamin mu Domin Ina Son kusani Malamin mu ba Sa'ar k bane, ehe

Zakin faidah da kuke gani A kaf Cikin kafatanin wahabiya babu wanda Zai iya Saka sa baki a Harkar sa In dai Akan Magana ce ta Ilimi

Domin dukkanin ku daukakar biri ce gare ku kuna sama tsuliyar ku na waje🤣🤣🤣🫣

Saboda Haka ayi tattara wallahi a kiyaye Yakamata wahabiya kusan cewa bakin rijiya ba gurin wasan yaro D makaho bane yawa Allah Ta'aala yasa an gane Zancen

✍️Shuaeveesk

✨ ALMAJIRAN SHEHU TIJJANI (RTA) ✨🚫 Bama zuwa wajen wani Waliyyi 🌟🔍 Neman madadi — komai girman darajarsa.🤲 Ba don muna r...
08/13/2025

✨ ALMAJIRAN SHEHU TIJJANI (RTA) ✨

🚫 Bama zuwa wajen wani Waliyyi 🌟
🔍 Neman madadi — komai girman darajarsa.

🤲 Ba don muna raina shi ba…
💎 Sai don muna da Ubanmu 👑 — wanda ya ishe mu!

🌙 Ubanmu Shehu Ahmad Tijjani (RTA)
☁️ Yana Gaba da kowane Waliyyi a ƙasa 🌍 da sama ✨

⚖️ Komai girman Waliyyi…
📿 Yana ƙasa da Shehu Tijjani (RTA) a daraja.

🕋 Wannan tsarin Allah ne Haka yaga Dama.
🕌 Abi liman Imamu Shehu Tijjani RTA,
🔄 Ko ka canza masallaci…

📿 Ashiga Darika — Abi Shehu Tijjani (RTA)
🔥 Ko akasin haka — Abi Shaidan Warr.

DAKARUN SUNNAR KARE MARTABAN ANNABI (S.A.W) DA IYALANSA 🥰Wallahi Ina Kaunarku Sabida Yadda Kukewa Addinin Musulunci Hidi...
08/12/2025

DAKARUN SUNNAR KARE MARTABAN ANNABI (S.A.W) DA IYALANSA 🥰

Wallahi Ina Kaunarku Sabida Yadda Kukewa Addinin Musulunci Hidima Da Kuma Yadda Kuke Kare Martaban Ma'aiki (S.A.W) Da Janibin Iyayensa.

Wallahi Kaunar Da Nakewa Wayannan Bayin Allah ♥️ Bazai Misaltuba.🙏

Allah ya Kara ingantamana lafiyar ku albarkan Shugaba (SA.W) 🥰

✍️ Abubakar Gausu Attijjani

BAYE LA SOLUTION 🌹❣️"Unveiling History: The 4,500-Year-Old Tunic at the Egyptian Museum"😱🥰🇯🇴😊     Treasures
08/12/2025

BAYE LA SOLUTION 🌹❣️
"Unveiling History: The 4,500-Year-Old Tunic at the Egyptian Museum"😱🥰🇯🇴😊


Treasures

Address

Memphis, TN

Telephone

+19012504296

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when S jazuga na futuhi tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to S jazuga na futuhi tv:

Share

Category