๐…๐ƒ๐€ ๐€๐ฉ๐ฉ๐ซ๐จ๐ฏ๐ž๐ ๐–๐ž๐ข๐ ๐ก๐ญ ๐‹๐จ๐ฌ๐ฌ

  • Home
  • United States
  • New York, NY
  • ๐…๐ƒ๐€ ๐€๐ฉ๐ฉ๐ซ๐จ๐ฏ๐ž๐ ๐–๐ž๐ข๐ ๐ก๐ญ ๐‹๐จ๐ฌ๐ฌ

๐…๐ƒ๐€ ๐€๐ฉ๐ฉ๐ซ๐จ๐ฏ๐ž๐ ๐–๐ž๐ข๐ ๐ก๐ญ ๐‹๐จ๐ฌ๐ฌ Your dream body, crafted together. Break free, embrace your true self with a professional weight loss plan tailored just for you.

Join us in saying no to the impossible and turn the page to a new chapter of captivating curves!

01/07/2025
INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIL RAJI'UN. Allah yayi rasuwa ma Babban Malamin Addinin Musulunci, a jihar Kano Sarkin Malaman...
11/06/2023

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIL RAJI'UN.

Allah yayi rasuwa ma Babban Malamin Addinin Musulunci, a jihar Kano Sarkin Malaman Gaya, kuma babban Shehi a Darikar Tijjaniyya Sheikh Dr. Yusuf Ali.

An kuma wallafa a shafin da yake yaษ—a karatukansa na facebook cewa za'ayi jana'izarsa da karfe 1:30 na ranar yau litinin, a masallacin Murtala dake Kano.

Allah ya jikanshi, yasa Aljanna fiddausi ce makomar sa Ameen.

ANYI WA ALKALI DA LAUYA DUKA A GOMBE.An bayyana zargin cewa, wasu โ€˜yan kauye sun kai farmaki kan alkali a yankin Degri d...
11/06/2023

ANYI WA ALKALI DA LAUYA DUKA A GOMBE.

An bayyana zargin cewa, wasu โ€˜yan kauye sun kai farmaki kan alkali a yankin Degri da ke karamar hukumar Balanga a jihar Gombe.

Jaridar hausa.legit.ng tace wadanda ake zargin an ce sun farmaki alkalin Babban Kotun Yanki na III, Ayuba Buba-Dalas, Barr Usman Yahaya da wani maโ€™aikacin kotun.

Majiyar jaridar Punch ta tattaro cewa, akan samu sabani kan gonaki a yankin, inda ake warwarewa a gaban kotun da ke garin.
An ruwaito cewa, a wannan karon, mai shariโ€™a Buba-Dalas ya yi kokarin zuwa da kansa don gwada fadi da tsawon wata don raba rikicin da aka kawo gabansa.

Wani ganau ya bayyana cewa, an farmaki maโ€™aikatan kotun ne a daidai lokacin da โ€˜yan kauyen s**a hango suna zuwa yankin.
Kungiyar lauyoyi ta Najeriya reshen jihar Gombe ta tabbatar da faruwar lamarin ta bakin sakatarenta na yada labarai, Bashir Abdullahi a ranar lahadi.

Source: Legit.ng Hausa

Da 'Yan Hisbah Su Rungumi Mace Su Saka Ta Cikin Mota, Da A Bar Matan Suna Fasikanci Wanne Ya Fi Muni?, Tambayar Sheik Be...
11/06/2023

Da 'Yan Hisbah Su Rungumi Mace Su Saka Ta Cikin Mota, Da A Bar Matan Suna Fasikanci Wanne Ya Fi Muni?, Tambayar Sheik Bello Yabo

Shehin Malamin ya kara da cewa "don haka 'Yan Hisbah kar ku damu da surutan mutanen banza, ku ci gaba da rungumarsu kuna saka wa cikin Hilux.

Me za ku ce?

1. Bread N600 2. Madara N100 3. Sugar N100 4. Kwai N300 5. Oil N150 6. Boun vita N180     Total N1,1301,130 ร— 30 = 33,90...
11/06/2023

1. Bread N600
2. Madara N100
3. Sugar N100
4. Kwai N300
5. Oil N150
6. Boun vita N180
Total N1,130
1,130 ร— 30 = 33,900
A albashin malamin primary saura nawa ko kuma nawa zai cika?

Sakon Aleeyu...Wannan Hasashe ne Nan da shekaru 30 masu zuwa;1.  Kashi 70 na maza bazasu iya biya wa mata buฦ™atan kwanci...
11/06/2023

Sakon Aleeyu...

Wannan Hasashe ne Nan da shekaru 30 masu zuwa;

1. Kashi 70 na maza bazasu iya biya wa mata buฦ™atan kwanciyar aure ba. Idan kana san tabbatar da haka, kaje Islamic Chemist da kuma inda ake sayarwa Man-power anan zaka ga yara ฦดan 25 to 30 years ke amfani da shi, duk da karancin shekarun su.

2. Za a samu yawaitar mata masu neman mata ฦดan-uwan su (Le****ns) da kuma masu amfani da sauran artificial in*******se wajen biya wa kan su bukata, kasancewar basa samun gamsuwar ta ษ—aya ษ“angaren wato maza.

3. Za a wayi gari, adadin mazan dake neman maza (homosexual) zai yawaita, ya ฦ™aru akan yadda yake a yanzu, saboda sauฦ™in gamsu da kuma sauฦ™in samun yin haka.

4. Masu cutar suga (Diabetes) zasu karu da adadin mai yawan gaske, saboda yadda mutane ke amfani da abincin da baya kawo sinadirin "insulin" da kuma yawaitar cin abinda, ke bukatar insulin ษ—in, wato abinci nau'in Carbohydrates.

5. Kasar mu Nigeria zata nin ka sau kusan sama da 15% zuwa 20% daga matakin da take na tattalin arziki a duniya, wanda hakan zai bata daman gogayya da manyan kasashen duniya waenda sune "Super-power" a Yanzu.

6. Mutane zasu waye, ta yadda za a dinga zaษ“en wanda ya dace wanda kuwa bai dace ba, zaษ“en sa bazai yiwu ba, haka zalika yan siyasar mu zasuji shakkar kin yin abinda ya dace su yi wa talakawan su.

7. Cutar ฦ˜anjamau (HIV AIDS) zai zama Tarihi da shi da Corona virus ta yadda baza a ji shakkar mai shi ba, sannan masu shi zasu ฦ™aranta acikin al'umma.

8. Waenda ake haihuwar su da lalurar shan inna da ciwon ido da kuma sauran matsalolin da ake haifar mutum da shi zai zama tarihin da sai dai adinga tunawa da shi.

9. Karancin Maza zai yawaita akan wanda ake da shi a yanzu ta yadda cikin sauki kowa zai iya fahimtar haka a duk inda yake a fadin kasar Nan.

10. Adadin mata dake mutuwa sanadiyyar haihuwa da kuma yara ฦ™anana zai ragu ba kamar yadda muke a yanzu da mu ka zama lamba daya a duniya na wannan matsalan ba.

11. Za a karbi kudin yanar Gizo -gizo hannu bibbiyu (Criptocur

Tambaya..?Bayan Bauchi Inane Kuma Ake Zabga Ruwan Sama Yanzu..
11/05/2023

Tambaya..?
Bayan Bauchi Inane Kuma Ake Zabga Ruwan Sama Yanzu..

Da dumi'dumi: Mun Gamsu da bukatun Al'ummarmu 'Yan Arewa ba za muyi Yaki ba tsakaninmu da Kasar Niger ~Cewar Shugaba Bol...
11/04/2023

Da dumi'dumi: Mun Gamsu da bukatun Al'ummarmu 'Yan Arewa ba za muyi Yaki ba tsakaninmu da Kasar Niger ~Cewar Shugaba Bola Tinubu.

Shugaban Bola Tinubu ya bayyana hakan a lokacin da ya karbi bakoncin Jakadan Kasar Faransa Emmanuelle Blatmann a fadar Shugaban Kasan Dake Abuja Yana Mai cewa Dangane da halin da jamhuriyar Nijar ke ciki, shugaba Tinubu, wanda shi ne shugaban kungiyar ECOWAS, ya ce Najeriya na sanya ido kan al'amuran da ke faruwa a makwabciyar kasar, tare da binciko hanyoyin diflomasiyya don kaucewa zubar da jini.

โ€œShugabanci ya shafi biyan bukatun jamaโ€™a kukan su da Jin bacin ran su. Najeriya na da iyaka da Nijar a fadin jihohin Najeriya bakwai, kuma galibin wadannan jahohin na da yawan jama'a. Don haka ina bukatar in yi wa ECOWAS jagoranci cikin tsanaki da tsayuwa domin mu sarrafa fushinmu a hankali.

โ€œMuna da abokin aiki kuma shugaban da aka zaba bisa tsarin dimokradiyya, Shugaba Bazoum, ana amfani da shi Amatsayin garkuwar dan adam. Idan ba mu mai da hankali ba, shi da iyalinsa za su iya fuskantar haษ—ari.

โ€œIna amfani da duk dabarun da s**a dace na baya-bayan nan don guje wa zubar da jini a Jamhuriyar Nijar. Mun amince da muradin mutanenmu, ba sa son yaki, amma hakan ba yana nufin ba za mu iya daukar kwakkwaran mataki ba,โ€ in ji shugaban.

Shugaba Tinubu, a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ajuri Ngelale, ya fitar, ya ce Najeriya za ta ci gaba da jan hankalin abokan huldar kasa da kasa, a yunkurin da ake na ganin an sasanta alโ€™amura a Jamhuriyar Nijar cikin lumana.

Ministan harkokin wajen Faransa na Turai da harkokin wajen ya bayyana shirin Faransa na fadada hadin gwiwa domin cin moriyar juna da Najeriya a bangarori da dama.

Babu Wanda Za Mu Baiwa Haฦ™uri Don Mun Gayyaci Malami Daga Wata Kasar Ya Yi Wa'azi, Martanin Sarkin Musulmi Ga Masu Sukar...
11/03/2023

Babu Wanda Za Mu Baiwa Haฦ™uri Don Mun Gayyaci Malami Daga Wata Kasar Ya Yi Wa'azi, Martanin Sarkin Musulmi Ga Masu Sukarsa Akan Gayyatar Zakir Naik

Ko Za Ku Iya Sanin Wane Garin Ne Nan?
11/03/2023

Ko Za Ku Iya Sanin Wane Garin Ne Nan?

Hasashe!!!Akwai yuyuwar za'a biya kusan naira miliyan 6 a matsayin kudin aikin hajjin bana a Nijeriya inji.AHUONฦ˜ungiyar...
11/03/2023

Hasashe!!!

Akwai yuyuwar za'a biya kusan naira miliyan 6 a matsayin kudin aikin hajjin bana a Nijeriya inji.AHUON

ฦ˜ungiyar AHUON ta bayyana cewa mahajjata masu niyyar zuwa aikin Hajji na iya biyan kusan N6m saษ“anin N3m da aka biya a lokacin aikin Hajjin 2023.

Wannan tsokacin ya fito ne daga bakin shugaban ฦ™ungiyar AHUON na ฦ™asa Alhaji Yahya Nasidi, lokacin da yake jawabi a birnin Kano yayin taron wayar da kai kan aikin Hajjin 2024 a ranar Laraba, 1 ga watan Nuwamban 2023.

Nasidi ya nuna damuwarsa kan yadda kuษ—in zuwa aikin hajjin 2024 zai ninka na shekarar 2023 saboda tashin gwauron zaษ“i da Dalar Amurka ke yi, rahoton New Telegraph ya tabbata.

Ya buฦ™aci gwamnatin da hukumar NAHCON su taimaka musu wajen ajiye kuษ—aษ—ensu a ฦ™asar Saudiyya. Alhaji Nasidi ya bayyana cewa: "Muna fargabar abin da zai faru idan gwamnati ba ta shiga cikin lamarin ba.

" "A shekarar da ta wuce mun gudanar da aiki a kan N3m, yanzu zai iya wuce N6m domin haka ne muke kira ga masu son zuwa aikin Hajjin bana da su yi ฦ™oฦ™arin biyan kudin aikin Hajjinsu da cikin lokaci"
Daga shafin jaridar Labari Daga Bauchi

GWAURANTA: Na Gaji Da Zama Ni Kadai, Ina Son Zama Matar Wani Ko Budurwar Wani, Saboda Nima Na Cancanci Nayi Farin Ciki A...
11/03/2023

GWAURANTA: Na Gaji Da Zama Ni Kadai, Ina Son Zama Matar Wani Ko Budurwar Wani, Saboda Nima Na Cancanci Nayi Farin Ciki A Rayuwata Kamar Sauran Mata, Tsohuwa Ta Koka Da Zaman Kaษ—aici

Wanne fata zaku yi mata ?

Address

New York, NY

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ๐…๐ƒ๐€ ๐€๐ฉ๐ฉ๐ซ๐จ๐ฏ๐ž๐ ๐–๐ž๐ข๐ ๐ก๐ญ ๐‹๐จ๐ฌ๐ฌ posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share