17/11/2025
Bangaran Ramlat tunda ta shige bedroom d'inta tayi wanka ta canza kaya yanzu ma ba wani abun arziki ta sakaba rawa take ta Tika cikeda farin ciki sai karairaya take tana
" ai wlh yau da inada hanyar fita waje da na hada kwarkwarya liyafa na hada party anyi casu saboda my soja yana cikin wani hali dan nasan yau ba bacci kwashewa tayi da dariya ta fada saman bed tana maida numfashi, wayarta ta fara ringing kallonta takai wajen wayar murmushi dauke kan face dinta ta hannu tasa ta dauko wayar tayi picking Takara a a kunnata" wayyo allah my khaleel wlh yau nayi babban lefi ba hanyar fita. muyi hakuri sai wani lokacin I love u my khaleel bye ta kasha wayar baki daya ta lumshe idanta tana neman hanyar zuwa gidan hajiya Dada dan sanin kantane yanzu ya saka asamata ido akamo masa ita tsaki taja aikin banza ai kin hofi wlh yanzu ma na fara zuwa part d'inka mutikar baka gari allah sai naje yauma ranace ta baci ka k**ani dede lokacin ake buga kofarta ido ta zaro " ke Ramlat ki bude wai uwar me k**e aciki ajiyar xuciya ta safke amma bata yada da mummy taba dan tasan bakinsu daya da mugun soja " mummy nifa wlh bazan bodeba kida ta kunna takore sauti ta Shiga shaaninta
********** ********** *********
Asalinsu alhaji usman Mani buzun bagajyya haifafan agadez ne dake cikin Niger buzayen asaline, gaba da bata allah yayi musu kyau jajur dash tashi ko dama ba,acewa komai sabofa shi s**a gada shikadai ne agurin iyayansa gaba da baya tinda ga haihuwarsa Mani da hauwa allah bai kara basu haihuwaba ya taso cikin gata da kulawa yasamu karatun addini da na boko dede gwar gwado Mani kasuwancinsa shine saiyar da manyan dabobi babu inda abaa san saba daga niger zuwa Nigeria chadi Cameron Mali Ghana da dai sauransu sai de kaf acikin mutanansa ba Wanda jinunsu yafi haduwa k**ar alhaji hambali na allah Wanda ke zaune a Nigeria suna kaunar junansu sosai shi ya bashi shawara Akan ya komo Nigeria yaci gaba da kasuwan cinsa da ya so ya kiya amma da yayi shawara da yan uwansa sai s**a aminta ai duk karuwaca
To wanan shine mafarin komo, warsu Nigeria garin kaduna usman yaci gaba da karatunsa allah ya albarkaci dukiyar Mani tana bungasa har matarsa ta bashi shawara ya Kara aure ko allah yasa asami rabon haihuwa yace ai da dayama garine in allah ya rayashi, to haka raguwa tayi ta tafiya har usman ya gimar ya kammala karatunsa ya mama ai ki iyayan sa s**a matsa masa Akan aure yace to shi yar gidan kawunsa musa yake so ta niger farin ciki s**ayi sosai ba bata lokaci s**a rankaya niger,
Rashida da akazo mata da magana bata ki tayiba ta amince akasa ka rana biki, rashida itama buzuwa ce fir kyakyawa ce sosai diyar kanan Mani ce ranar biki tazo akasha biki aka dau amarya aka tafi da ita Nigeria zama suke mai, cike da kaunar junansu bayan shekara biyu da auransu allah ya basu haihuwa fa namiji Wanda yaci sunan mustapha
ya samu bata sosai gun iyaynsa da kakaninsa ashekaran Mani ya sai wani tafka tafkan filaye a abuja
Tinda ganan haihuwa ta budewa rashida takara haihuwar namiji mai sunan munnir sai saudat sai Ibrahim sai jafar sai hamza sai mansur
sai maimunatu sai zuwaira sai autansu maaruf daga kansane haihuwa ta tsaya shekaru sunyi ta tafiya tsufa ya cinma hauwa da Mani wanda suke rungume da jikukinsu cikin so da kauna
Har zuwa girman su mustapah shi ya fara aure inda shima yar uwashice buzuwa ya aura amma Ana Kaduna suke da zama ita da iyayanta najaatu macace mai karamci da sanin ya k**ata gata da son jama'a bayan shekara daya da auransu ta haifo santalelan danta namiji yaci sunan Naseer shakara munnir shima yayi aure ya auri asiya anan kaduna to ba laifi tanada kirki shekara na zagayowa ta haihu namiji aka samasa suna nuradin bayan shekara biyu najaatu ta Kara,
haihuwa namiji kyakyawa ajin farko kyaun yaron baya faduwa a baki ai kuwa gaba daya family k**ar acinyesa saboda kyansa ranar suna yaci sunan Abdullahi
To daga haihuwar Abdallah aure ya bude a gidan a bayan auran saudat da shekaru biyu akasa ka auran mutum hudu saboda kasancewar haihuwar su ba nisa tsakani
Ibrahim jafar hamza mansur gaba daya aka saka auransu,
lokacin Abdallah nada shekara biyu amma tindaga lokacin zaka gane yaron idan ya girma zaa zuba miskilanci saboda ko irin dariyar naman bayayi ta yara,
Lokacin biki da yazo angangaje ba laifi saide biki yayi lami saboda ranar daurin aure matar da, hamza zai aura ta rasu ai kuwa haukane bai yiba saboda yana mugun son Ramlat saida yayi jinya sosai Kafin ya dawo daide, saida aka hada da rokon allah ya dawo haiyacinsa saide fa yace shi bazai taba aureba darker aka shawo kansa amma yace sai mai sunan ramlat lallabashi s**ayi aka hadashi da rahma diyar abokin usman saboda tanada hankali da nutsuwa daker ya amince, da sharadin daga ya sami, ya mace zai saka mata sunan ramlat s**a ce eh sun aminta tikun ya amince akayi bikin,
Bayan, aure Kafin wani lokaci ta mantar, dashi Ramlat s**a Gina zamansu cikin so da kaunar junasu, bayan shekaru biyu ta haiho namiji har fara yake yaso ace macace, yasa sunan
Ramlat amma allah baiyiba
haka rayuwa, tayi ta tafi har rahma ta sake haihuwa mace amma batazo da raiba har kuka hamza yayi,
Tofa Abu k**ar wasa rahma haihu tayi tayi har suku duka mata amma babu rai hankalinsu yayi mutikar tashi kuma sahekarane allah yayiwa Mani rasuwa sun Shiga tashin hankali mutika amma ya zasuyi da ikon allah,
********* ********** **********
Bayan, shakaru biyar da mutuwar Mani hauwa ma tace ga garinku, nan allah ya amshi abunsa, sunyi kukan rashin kakarsu mai sonsu usman ko yayi kukan rashin mahaifiyarsa
Alokacin, kaf yayan usman buzun bagaiya babu wanda bashida aure duk matan auren wurine s**ayi idan ka ganshi bakace ya aura da yara hudu bama bare yara goma kowa na gidansa na aure
Alokacin, ne ya tatara kan iyallansa yace zasu komaa abuja da zama sunyi farin cikin hakan lokacin ne rahma ta kuma samun ciki. Sosai take bata wahala haka tayi ta fam, kullum cikin kuka dan tasan karshen zancan, cikin ikon allah ta haihu lafiya abinda ta Haifa sunzo a raye yarane mata, ta Haifa har biyu kyawawa sankowa ai abin nema yasamu hamza ya rasa yada zai sa kansa dan dadi yau gashi da yara mata tiwis family sunyi murna susai, saide Kafin sunah dayar tace ga garinku nan ta koma ga, allah
Hamza Kuka yarikayi k**ar yaro sai rahama ce ke lallashin, tikun ya hakura ranar sunan ya sak**a yarinya hassana amma kuma yace Ramlat wancan sunan na ta gwai takane amma sunanta Ramlat da Ramlat ko ta tashi tanada wata uku da haihuwa,
alokacin ne
Abdallah yanada 11years amma yana mutikar son zama da anty rahama idan har baya school to yana gidan antinsa rahama saboda jininsu tafi haduwa Akan sauran Matan saide Sam jininsa bai hadu da ramlat ba duk da tana jaririya amma yanajin tsanarta aransa wai yanzu haka ita ta kashe abukiyar. Haihuwarta dan kar su rayu tare shiyasa kwata kwata bayason jaririyar ko ya sata, gaba yana zaginta wanan, daga ganinta muguwace za,ayi kujifa tin yanzu idanunta kirikiri atsaye
Lokacine s**a tare a,
cikin narkeken ginin gidajan Family estate bagaiyya wanda ke uguwar maitama abuja babuce ba a sakaba agidan.......✍🏼
.....gidajan sun hadu iya haduwa estate ne guda family's, usman buzun bagaiyya, kowa da ban,garansa, haka s**a tare da iya linsu cikin farin ciki da kaunar junansu, sun hada Kansu da na yaransu,
***
Bayan tarewarsu Abuja da shekara biyu a abuja lokacin dukiyarsu ta bunkasa fiye da yada me karatu kake tunani, alhaji usman ya hada
Meeting family s**ayi shawara akan su bude makarantu da asibiti, sunyi na'am da hakan Mayan filaye ya siya abinka ga mai akwai ba ajima gashi susai suna dasawa da gwamanati duk yabar aikin gwamanati ya fada kasuwanci shida kanninsa
Kafin kacemai an kwankwatsa makaranta tagani ta fada wace akasa mata suna complete schools private bagaiyya
Sosai jama'a ke turuwar kai yaransu kankacemai makarantar tayi suna a fadin Nigeria da niger,
******
Bayan budeta da shekara biyu ya Gina makeken asibiti a cikin estate family bagaiyya wace hospital din ita taci sunan bagaiyya Family amma har daga waje jama'a suna zuwa allah yaba mutanan arziki
******
Ramlat tayi wayo sosai kyanta ya Karu ga surutu, hamza yana mugun son yarsa sosai duk inda zashi suna tare gun aikine kadai baya zuwa da ita sai de fa yarinya muguwace ta karshe dan ko barna tayi aka dan doketa to wlh ranar wanda ya tabata to ba lafiya zuwa lokacin Abdallah jiyake da yanada halin kasheta wlh zai iya kasheta dan kawta kwata yarinya bata masaba, haka de rayuwa tayi ta tafiya har zuwa wasu shekaru Family estate din bagaiyya cike tada zuria mustapha nada yara shida Naseer Abdallah abubakar jameela hadeeza da auta shaffah, munnir, yanada yara biyar nuradin Abdullateef saratu. Najaatu safna, sai Ibrahim yanada uku anwar zakiyyah haleema, jafar ma uku ne aminu Ahmad faridah, hamza nada biyar sulaiman Ramlat affan nusaiba nabeela mansur ne allah bai bashi haihuwa ba jafar nada yaransa biyu mujaheed safara'u bangaran matama masha allah kowace
nada
Nata yaran allah ya dauka zuri'ar wanan family masha allah kansu ahada idan sun hadu baka ce ga dan wane ba ramlat ce tayi daban acikinsu nabeela na hannun mansur hamza yace yabashi ita kyauta koda allah ya bashi haihuwa ya hada yarike,
---------------- -------------- ---------------
Haka rayuwa taci gaba da tafiya, Ramlat tin tana primary school hatsabi bancinta yayi over yara dayawa anciresu daga makarantar da take saboda basuda yada zasuyi tin makarantarsu ce daurin gidin da take dashi amakarantar mahaifinta baya ganin mutumcin kowa akanta Ramlat shiyasa take tsula tsiyarta, saida usman ya takawa hamza birki, duk shima yana son ramlat fiyeda duk sauran jikokinsa tindaga primary school har zuwa secondary school zuwa lokacin rashin ramlat ya baci ga masifar iya mugunta wanan abun yana damun families dinsu har sadakar kudi suke rabawa Akan amata adu'a allah ya ciremata muguntar ta bata daukan raini ga batada tsoro mutum daya take tsoro arayuwarta Abdallah to tunda ya tafi London karatu shikenan iskancinta ya karu yawun zuwa casu ba inda bata zuwa amma wanan bai hanata tsayawa tayi karatuba kullum ita ke zuwa tadaya tindaga primary school har zuwa secondary school, har ta gama
Lokacin kyanta na asali ya fito saboda allah yamata diri mai kyau doguwace fara amma ba farin nan bas ba akwaita gashi mai santsi da tsayi idanunta masu mutikar haske saide kanune basuda girma amma sunyi mutikar yimata kyau tanada dimple wanda ko magana take suna lobawa dika kuncinta hancita zuwat atsaye batada Rama sosai kuma batada jiki idan kanta so kajama Lanka jaraba to cemata mai kanan idanu to sai kayi nadamar fada ahakade har s**a kammala secondary school kawarta daya jawahir
Rigima ta tada ita akaita waje tayi karatun ta tunda ta gama secondary school agida s**a family dinta basu bada goyan bayaba mahaifita ne kadai ya amince usman yace Sam bai lamintaba inda ace yarinya tanada nutsuwa to da dama amma agidama ya take bare a kasar waje lallabata yayi tayi tacigaba da karatunta agida itako tace Sam wallahi baxataci gababa in dai agidane ta hakura bayanda basuyi da itaba tace allah tabar makarantar amma fa 😂😂😂 kaf dinsu ba wanda bai ci uwar jinyaba ta uban mamaki dan jafar ya kai wata ko bakin kofa baya fita daker da sa bakin dada tikun saboda tana masifar son tsofuwar to shine ta hakura amma tace ta haramta karatun batayi tayi xamanta agida sai tsiyar fit in a iri iri
********* *********** **********
Bayan shekaru. Hudu Abdallah ya kammala karatunsa ya dawo gida wanda ya fito a babban soja, ya k**a aiki gadan gadan baji ba gani to lokacin Ramlat tarage yawan fita da shigar kananun kaya duk ba haduwa soke sosai ba dan baya mata ta dadi kuma har lokacin tinda take magana bata taba shiga tsakanin suba dan baya kaunar ko ganinta horan da yake matama, na dolane don, mahaifinsa ya sakashi gashi kuma yanaji da mahaifiyarta rahama, Ashe idan baya gari batada gun zuwa sai part dinsa har kawayanta take kai wa suyita ita shege da raye raye ta saka kakinsa na soja da takalminsa tana iskanci iri iri ko tashige bedroom dinsa tayi kwanciyarta Abu buwa de iri iri ba wanda Ramlat bata iyaba akwi lokacin da takawo saurayinta khaleel part din Abdallah, wanda ko wata basuyi da haduwa amma fa taga irin kalatane take sauraransa dan shima har kala yake canzawa gashin kansa, karma yada take wa gashinta,
Tace masa ya Saki jikinsa part din kanitane soja bayanan s**a Kari raye rayensu sai dare ya tafi dan duk iskancinta kayi kadan ka k**a mata koda yatsar hannunta amma dayawa, jama'a suna mata kallon mai bin maza saboda yawan shigar banzar da take,
---
Bayan shekara daya Abdallah ya samu mukamin daban daban a soja ansha bikin Karin girman daya samu jama'a daban daban dake mahaifinsa wanine yasami kyaut**ika ba adadi a yanzu duk inda yake yana tare da securities fiyeda goma na biye dashi saboda ansha kawo masa hari so kusan uku Allah ke kareshi saboda wasunsa sun so ace sune saman mukamin,sa
mata ko s**ace dawa allah ya hadasu amma ina ko kallon arziki basa samu amma duk da haka har yanzu biye suke dashi yakan ce aturai ma sunyi sun barni nafisat daya naso a London Dana gano halinta nabarta har abada
Mummy ta tayi tayi ta bode kofar taki shaanita take tana tsaka da casunta zuciyarta fari kal dan duk lokacin da zatama wani mugunta irin haka to acikin farin ciki take
Bai farkaba sai wajan karfe ta kwas na dare a hankali yake bude shanyayin idanunsa har ya bude su tar bakowa shi kadaine tashi yayi ya fice a bakin kofa s**a hadu da Dr jinaidu " a soja an tashi ya fara yana danne dariya da tazomasa kai ya daga masa ya ficewarsa direct part d'insa ya nufa security biyu na biye dashi, daker ke magana tamkar bayaso" ina fatan kun kawo mun yar iskar yarinyar,nan cike da fargaba s**ace" yallabai wlh munbi duk wata hanya mai sauki amma ko Santa ba muganiba tsoki yaja yana ciza bakinsa ya shige bedroom, kayan jikinsa ya rage ya shige toilet shower ya sakanwa kansa yajima sosai Kafin ya fito daure da towel daure a qogunsa jikinsa ya tsane ya murza maiyuka masu sanyin dadi jallabiya ya saka ya tada sallah koda ya gama Yajima yana neman gafar agun allah fa adu'ar allah ya bashi nasarar kamo Ramlat a kusa mike'wa yayi ya fice part din yinma bakowa a parlon cikin nutsuwa ya fara magana" yinma kina ina shaffah ce ta karasu cikin rawar jiki " batanan ta tafi part din kawu hamza wai Ramlat ta ruke taki bude tsoki yaja yana hararata " uwar magana ficewa yayi daga parlon yanufi part din su ramlat da sallama ya shigo parlon Ramlat tayi daidaya jikin yinma sai zuba sangarta take hamza da mustapah suna tambayar ta ta fadi abinda yasa tarufe kanta adaki dan sun tsorata ta taba irin haka saida tayi kwana biyu kuma anyi anyi a banbare kofar dakin, taki banbaruwa abin yayi mutikar tada musu hankali amma tana fitowa s**aga babu abinda yasameta, a ranshi yake cewa" naga samu naga rashi amma yau da kince kaniyarki sallama ya karayi karf a kunan Ramlat wace tsabar kaduwa da tayi batasan lokacin da ta diro tatsaya gaban kawu mustapah ba kanta ya fara juyawa ko ina jikinta karkarwa yake cikeda tsoro ya rikota ke hassana lfy da hannu take musu nuni shiko da ya lura basu kula da ya shigo ba sai yayi baya ya tafiyarsa" zaki ubanki yar iska
itako jikinta ya fara Saki idanunta sun fara lumshewa tayi luuuu......✍🏼
゚viralシfypシ゚viralシalシ