Albarka tv and radio

Albarka tv and radio Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Albarka tv and radio, Media/News Company, Kano.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci manyan jami’an tattalin arziki na Nijeriya da su gaggauta fito da matakan rage...
11/04/2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci manyan jami’an tattalin arziki na Nijeriya da su gaggauta fito da matakan rage radadin da rikicin Gabas ta Tsakiya ke jefa wa ‘yan ƙasa.

Shugaban ya bayar da umarnin ne a ranar Juma’a yayin wata liyafa da aka shirya masa a Yenagoa bayan kaddamar da wasu ayyuka da Gwamnan Bayelsa, Douye Diri ya aiwatar.

Ya ɗora wa Ma’aikatar Kuɗi da Tsare-tsare tare da shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya, Didi Esther Walson-Jack, alhakin nemo hanyoyin sauƙaƙa wa talakawa matsin tattalin arziki.

A cikin sanarwar da kakakin shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya amince cewa rikicin duniya ya ƙara tsananta tsadar rayuwa, musamman ta fuskar farashin man fetur.

“Ina jin koke-kokenku… farashin mai na matsawa, amma dole mu yi la’akari da abubuwan da ke faruwa a duniya,” in ji shi.

Ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta yi aiki tare da masana domin samar da hanyoyin rage wannan nauyi da ke kan al’umma.

Shugaban ya kuma jaddada aniyar APC na inganta rayuwar jama’a ta hanyar ayyukan raya ƙasa kamar hanyoyi, gadoji, wutar lantarki da samar da ayyukan yi.

A ziyarar tasa, Tinubu ya ƙaddamar da wasu manyan ayyuka ciki har da tashar wutar lantarki mai ƙarfin megawatt 60 a Elebele, gadar Angiama zuwa Oporoma, da kuma sabuwar hanyar shiga birnin Yenagoa.

Ya yaba wa Douye Diri kan haɗin gwiwa da gwamnatin tarayya, yana mai cewa wannan ne mabuɗin samun ci gaba cikin sauri.

Kafin kammalawa, shugaban ya buƙaci mahalarta taron su yi shiru na minti guda domin karrama sojojin da s**a rasu da kuma tsohon gwamnan Diepreye Alamieyeseigha.

A nasa jawabin, Gwamna Diri ya ce goyon bayan gwamnatin tarayya ya taimaka wajen kammala ayyukan wutar lantarki da za su bunƙasa tattalin arziki da rayuwar al’umma.

Me zaku ce. ?

Wata tawagar Gwamnatin Tarayya, bisa umarnin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ta kai ziyara ga Gwamnatin Borno domin jaj...
11/04/2026

Wata tawagar Gwamnatin Tarayya, bisa umarnin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ta kai ziyara ga Gwamnatin Borno domin jajanta wa harin da aka kai a Benisheikh wanda ya yi sanadiyyar mutuwar sojojin Nijeriya.

A yayin ziyarar, tawagar ta yi ta’aziyya ga iyalan sojojin da s**a rasu, inda ta bayyana su a matsayin jarumai masu kishin ƙasa da s**a sadaukar da rayuwarsu wajen kare ƙasa.

Jami’an sun jaddada cewa sojojin sun tsaya tsayin daka wajen kare al’umma, iyalai da makomar ƙasa, suna mai cewa irin wannan sadaukarwa na nuna muhimmancin tsaro da zaman lafiya.

Tawagar ta kuma tabbatar wa Gwamnatin Borno da rundunar sojin Nijeriya cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da ba da cikakken goyon baya.

Haka kuma ta yi alƙawarin cewa za a hukunta waɗanda s**a kai harin, tana mai cewa a ƙarƙashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu ba za a bar masu aikata laifi su tsira ba.

Me zaku ce. ?

HOTO: Taron Karrama Hajiya Mariya Galadanchi.An gudanar da taron karrama Hajiya Mariya Galadanchi a ɗakin taro na Mahmud...
11/04/2026

HOTO: Taron Karrama Hajiya Mariya Galadanchi.

An gudanar da taron karrama Hajiya Mariya Galadanchi a ɗakin taro na Mahmud Tukur Hall da ke cikin Jami'ar Bayero Kano a Kano.

Taron ya haɗa manyan baƙi, malamai da ɗalibai, inda ake yabawa da kuma girmama gudunmawar da ta bayar a fannoni daban-daban.

Hedikwatar rundunar Operation Hadin Kai ta bayyana damuwa kan yaɗuwar rahotanni na ƙarya, masu ruɗani da kuma ƙara gishi...
10/04/2026

Hedikwatar rundunar Operation Hadin Kai ta bayyana damuwa kan yaɗuwar rahotanni na ƙarya, masu ruɗani da kuma ƙara gishiri a kan harin ‘yan ta’adda da aka dakile a Benisheikh.

Rundunar ta ce wasu kafafen talabijin da shafukan sada zumunta na yaɗa labarai marasa tushe tare da hotuna da bidiyo da ba su da alaƙa da lamarin, wanda ke ƙoƙarin karkatar da gaskiya da kuma rage amincewar jama’a da aikin sojoji.

Ta karyata zargin cewa sojoji 17 ciki har da kwamandan Birged sun rasu a harin, inda ta ce sahihin bayani da Hedikwatar tsaron Nijeriya ta fitar ya nuna cewa jami’ai 2 da sojoji 2 ne kawai s**a rasu yayin artabun.

Har ila yau, rundunar ta musanta cewa motar kwamandan Birged ta samu matsala, tana mai cewa kwamandan yana cikin wata mota mai kariya ta musamman daga fashewar bama-bamai, wadda ta dan tsaya na ɗan lokaci ne a lokacin artabu yayin da yake jagorantar martanin da aka mayar.

Rundunar ta kuma bayyana cewa hotuna da bidiyoyin da ake yaɗawa ba su da alaƙa da harin Benisheikh, kuma ana amfani da su ne domin yaudarar jama’a da haifar da fargaba.

Ta yi Allah-wadai da yadda ake karkatar da gaskiya ko amfani da irin waɗannan abubuwa domin manufofin siyasa ko yaɗa farfaganda, tana mai cewa hakan na rage darajar sadaukarwar da sojoji ke yi wajen kare ƙasa.

Rundunar sojin Armed Forces of Nigeria ta jaddada cewa harin da aka kai an dakile shi cikin nasara, inda aka tilasta wa ‘yan ta’addan guduwa cikin ruɗani tare da ci gaba da riƙe sansanin.

Ta kuma ƙara da cewa rundunar ita ce tushen sahihan bayanai kan ayyukanta, tare da kira ga jama’a da su dogara da bayanan hukuma kawai, su guji yaɗa jita-jita.

Sanarwar ta fito ne daga bakin jami’in yaɗa labarai na rundunar, Sani Uba, a ranar 10 ga Afrilu 2026.

Allah ya kyauta.

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, Ya Karbi Bakuncin   Shugaban Babban Kamfanin Ayyukan Yada Labarai na ...
10/04/2026

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, Ya Karbi Bakuncin Shugaban Babban Kamfanin Ayyukan Yada Labarai na DAAR Communications Plc, Wanda Sune Masu Gidan Talabijin na AIT, Raymond Dokpesi Jenior, Yayin Ziyarar Girmamawa da kamfanin DAAR Communications Plc Ya Kai Wa Ministan, A Ofishin Sa A Abuja.

Cutar Lassa ta yi ajalin mutum 167 duk da raguwar yawan kamuwa da ita a Nijeriya
10/04/2026

Cutar Lassa ta yi ajalin mutum 167 duk da raguwar yawan kamuwa da ita a Nijeriya

Babu wani abin tayar da hankali da zai sa Amurka kwashe 'yan kasarta daga Nijeriya - Gwamnatin Tinubu.Me zaku ce.       ...
10/04/2026

Babu wani abin tayar da hankali da zai sa Amurka kwashe 'yan kasarta daga Nijeriya - Gwamnatin Tinubu.

Me zaku ce. ?

Ɗan Majalisar Tarayyar na Minjibir da Ungogo Hon. Sani Adamu Wakili ya kai wa Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ziyarar ban girma....
10/04/2026

Ɗan Majalisar Tarayyar na Minjibir da Ungogo Hon. Sani Adamu Wakili ya kai wa Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ziyarar ban girma.

Me za ku ce?

Hotuna daga Abubakar Musa DK.

Sojojin Amurka za su ci gaba da kasancewa a kusa da Iran - Trump.Sauran labarin Yana Nan Albarka tv and radio .
09/04/2026

Sojojin Amurka za su ci gaba da kasancewa a kusa da Iran - Trump.

Sauran labarin Yana Nan Albarka tv and radio .

Nijeriya ba ta daf da rugujewa, tana nuna juriya da samun cigaba – Ministan Yaɗa LabaraiMinistan Yaɗa Labarai da Wayar d...
09/04/2026

Nijeriya ba ta daf da rugujewa, tana nuna juriya da samun cigaba – Ministan Yaɗa Labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi watsi da iƙirarin da ake yi na cewa wai Nijeriya na daf da rugujewa, yana mai jaddada cewa ƙasar tana nan daram kuma tana samun cigaba mai ɗorewa.

Idris ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a Abuja, a lokacin Babban Taron Ƙasa na 81 da Taron Shekara-shekara na 23 na Ƙungiyar Masu Watsa Labarai ta Nijeriya (BON).

Ya ce: “Ba gaskiya ba ne cewa Nijeriya na daf da rugujewa. A maimakon haka, muna ci gaba da nuna juriya tare da ɗaukar matakai masu ƙarfi wajen tunkarar matsalolin tsaro da tattalin arziki.”

Dangane da tsaro, Ministan ya ce cigaba da kai samamen soji da kuma inganta haɗin gwiwa a ɓangaren bayanan sirri suna samar da sakamako mai kyau, inda ya buga misali da samamen baya-bayan nan a jihohin Zamfara da Neja, inda jami’an tsaro s**a ragargaji ‘yan bindiga tare da daƙile hare-haren da s**a shirya kaiwa.

Ya ƙara da cewa: “Haɗin gwiwar sojoji da sauran jami’an tsaro ya samar da gagarumar nasara a sassa daban-daban na ƙasar nan, kuma muna ƙara ƙarfafa tsarin tattara bayanan sirri da saurin kai ɗauki domin kare rayuka da dukiyoyi.”

Game da tattalin arziki, Idris ya ce alamu suna nuna farfaɗowa da ƙaruwar amincewar masu zuba jari, ya ƙara da cewa gyare-gyaren da ake yi a ɓangarorin man fetur da sauran fannoni suna taimakawa wajen faɗaɗa hanyoyin samun kuɗaɗen shiga da kuma daidaita asusun gwamnati.

Ya ce: “Ajiye kuɗaɗen ƙasashen waje yana ƙaruwa, amincewar masu zuba jari tana ƙaruwa, kuma gyare-gyaren da ake yi a ɓangarorin mai da waɗanda ba na mai ba suna faɗaɗa hanyoyin samun kuɗaɗen shiga.”

Ministan ya kuma ambaci dawo da Nijeriya matsayin "Frontier Market" da kamfanin FTSE Russell ya bayyana a matsayin wata alama ta ƙara amincewar duniya da tattalin arzikin ƙasar nan.

Bugu da ƙari ya buƙaci kafafen yaɗa labarai da su kiyaye ƙa’idojin aiki da kuma tabbatar da sahihancin rahotanni, musamman yayin da ƙasar nan take tunkarar wani sabon zagayen zaɓe, yana mai jaddada muhimmancin rawar da suke takawa wajen tsara fahimtar jama’a da kuma inganta haɗin kan ƙasa.

Ya ce: “Dole ne kafafen yaɗa labarai su ci gaba da sanarwa, ilimantarwa da haɗa kan jama’a, tare da bin ƙa’idojin ƙwarewa, adalci da sahihanci a aikin su.”

Idris ya jaddada ƙudirin Gwamnatin Tarayya na tallafa wa kafafen yaɗa labarai, yana mai kira da a ƙarfafa haɗin gwiwa domin yaƙar labaran ƙarya da kuma ƙarfafa haɗin kan ƙasa.

Ya yaba wa Ƙungiyar Masu Watsa Labarai ta Nijeriya bisa rawar da take takawa wajen inganta ƙwarewa a fannin, sannan ya ayyana buɗe babban taron BON karo na 81, yana mai bayyana fatan cewa za a samar da hanyoyin warware matsalolin da fannin ke fuskanta.

Daga cikin waɗanda s**a halarci taron akwai Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kan ta (INEC), Farfesa Joash Amupitan; Darakta-Janar na Hukumar Kula da Watsa Labarai ta Ƙasa (NBC), Dakta Charles Ebuebu; Darakta-Janar na Gidan Talbijin ta Nijeriya (NTA), Salihu Abdulhamid Dembos; Darakta-Janar na Hukumar Tace Tallace-Tallace ta Nijeriya (ARCON), Mista Olalekan Fadolapo; Darakta-Janar na gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON), Malam Jibrin Baba Ndace; Darakta-Janar na FRCN, Mohammed Bulama, da sauran su.

Me zaku ce. ?

Abin da INEC ta yi wa ADC ya kai mu nemi shugaba Trump ya ƙaƙaba mata takunkumi - Kamfanin Von Batten-Montague-York, L.C...
09/04/2026

Abin da INEC ta yi wa ADC ya kai mu nemi shugaba Trump ya ƙaƙaba mata takunkumi - Kamfanin Von Batten-Montague-York, L.C. na Amurka.

Sanata Kawu Sumaila ya gana da Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima a Abuja.
08/04/2026

Sanata Kawu Sumaila ya gana da Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima a Abuja.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Albarka tv and radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share