Albarka Radio

  • Home
  • Albarka Radio

Albarka Radio 🎙️ Albarka Radio Online, Manufarmu Mu zama babbar tashar rediyo ta fasahar AI a Afrika da ke ilmantarwa, da yada gaskiya da cigaba.

Ayyukanmu
Mu wayar da kan al’umma ta hanyar sahihin labarai, ilimantarwa, da shirye-shiryen da ke gina tunani da kirkira.

An gudanar da jana’izar Kwamandan kwamitin yaƙi da ɓarayin waya na jihar Kano, Inuwa Salisu, a unguwar Sharada da ke cik...
30/10/2025

An gudanar da jana’izar Kwamandan kwamitin yaƙi da ɓarayin waya na jihar Kano, Inuwa Salisu, a unguwar Sharada da ke cikin birnin Kano.

Jana’izar ta samu halartar Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, jami’an gwamnati, ƴan sanda, da kuma ƴan uwa da abokan marigayin, waɗanda s**a bayyana rasuwar tasa a matsayin babban rashi ga jihar.

Marigayi Inuwa Salisu ya rasu ne a daren Talata, bayan da wasu ɓatagari s**a kai masa hari a gidansa da ke Sharada, inda s**a kashe shi.

An binne shi a makabartar Fadama da ke unguwar Sharada, bayan sallar la,asar a yau alhamis.

Hukumomi sun tabbatar da cewa an fara bincike don kamo wadanda s**a aikata wannan mummunan aiki.

Ƙungiyar Al Nassr ta fita daga gasar kofin sarki (King’s Cup) a zagaye na 16, bayan ta sha kaye a hannun Al Ittihad!Cris...
30/10/2025

Ƙungiyar Al Nassr ta fita daga gasar kofin sarki (King’s Cup) a zagaye na 16, bayan ta sha kaye a hannun Al Ittihad!

Cristiano Ronaldo da abokan wasansa sun kasa samun nasara, lamarin da ya jefa magoya bayansu cikin bakin ciki yayin da Al Ittihad ta tsallake zuwa mataki na gaba. ⚽🔥

Maryam Sanda na iya samun ‘yanci cikin shekara ɗaya da watanni huɗuBayan sabon matakin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinub...
30/10/2025

Maryam Sanda na iya samun ‘yanci cikin shekara ɗaya da watanni huɗu

Bayan sabon matakin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ɗauka na sauya wasu hukuncin kisa zuwa na daurin rai da rai, rahotanni na nuna cewa Maryam Sanda — wadda kotu ta same ta da laifin kashe mijinta — na iya samun ‘yanci cikin kusan shekara ɗaya da watanni huɗu.

A cewar wani bincike daga cikin hukumomin gidan yari, ana lissafin shekara ɗaya daidai da watanni takwas ne a tsarin zaman gidan yari, ma’ana wanda ya yi shekara shida da watanni takwas a zahiri, ya cika kimanin shekaru goma a lissafin gidan yari.

Tunda yanzu an sauya hukuncinta zuwa zaman shekaru 12, hakan na nufin cewa Maryam Sanda ta rigaya ta shafe kusan shekaru goma a cikin wannan sabon lissafi, kuma saura kimanin shekara ɗaya da watanni huɗu ta kammala cikakken lokacin zaman gidan yari.

Sai dai hukumomin gidan yari ba su tabbatar da takamaiman ranar da za ta fito ba, kasancewar dole a yi cikakken duba da tabbatar da sharuddan sakin kafin aiwatar da hakan.

Albarka Radio

Majalisar Wakilan Najeriya ta amince da bukatar Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ɗaukar sabon bashin waje na dala biliyan 2....
30/10/2025

Majalisar Wakilan Najeriya ta amince da bukatar Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ɗaukar sabon bashin waje na dala biliyan 2.35, domin cike gibi a kasafin kuɗin shekara ta 2025.

Shugaban Majalisar, Tajudeen Abbas, ne ya sanar da hakan yayin zaman majalisar a Abuja, inda ya ce kudaden za su taimaka wajen aiwatar da manyan ayyukan ci gaban ƙasa da kuma sake biyan wasu lamunin da s**a kai ƙarshen lokacin biyan su.

A cikin wasiƙar da shugaban ƙasa ya aika, ya bayyana cewa rance zai taimaka wajen fitowa daga kasuwannin Eurobond, bankunan waje, da kuma wasu cibiyoyin bashi na ƙasa da ƙasa.

Jimillar bashin Najeriya ya karu

Rahoton Hukumar Gudanar da Bashi ta Ƙasa (DMO) ya nuna cewa, jimillar bashin Najeriya ya kai naira tiriliyan 152.4 a tsakiyar shekarar 2025, wanda ya haɗa da lamunin cikin gida da na waje.

Wannan sabon rance na dala biliyan 2.35 zai ƙara nauyin bashin ƙasar, wanda a ƙarshen shekarar 2024 ya kai dala biliyan 94.2, kwatankwacin naira tiriliyan 70.3.

Dalilin karɓar sabon bashin

Gwamnati ta ce manufar sabon bashin ita ce cike gibin kasafin kuɗi na 2025, da kuma ƙarfafa fannonin tattalin arziki, tsaro, da aikin raya ƙasa.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya ce wannan mataki “yana da muhimmanci domin tabbatar da dorewar kasafin kuɗi da tallafa wa shirin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa.”

Sai dai wasu masana sun bayyana damuwarsu cewa ƙarin ciyo bashin zai iya ƙara nauyin bashin ƙasar, wanda ke iya shafar kudaden shiga da ake warewa ga ayyukan walwalar jama’a.
Masana sun bukaci gwamnati da ta tabbatar da cewa dukkan kuɗaɗen da aka aro an yi amfani da su ta hanya mai inganci da gaskiya.

TINUBU YA CIRE MASU MANYAN LAIFUKA DAGA JERIN WANDA YA YI WA AFUWAShugaban ƙasar Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya cire su...
29/10/2025

TINUBU YA CIRE MASU MANYAN LAIFUKA DAGA JERIN WANDA YA YI WA AFUWA

Shugaban ƙasar Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya cire sunayen masu manyan laifuka daga jerin mutanen da aka yi wa afuwa a farkon watan nan, bayan ce-ce-ku-ce da ta biyo bayan sanarwar farko.

A baya, Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa mutum 175 da kotuna s**a yanke wa hukunci ne s**a amfana da afuwar, ciki har da wasu da ake zargi da manyan laifuka irin su ta’ammali da miyagun ƙwayoyi, garkuwa da mutane, da kisan kai.

Sai dai wata sabuwar sanarwa daga fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa an sake nazarin jerin, kuma an cire sunayen masu irin waɗannan manyan laifuka.

A sabon jerin sunayen, mutum 34 kacal s**a rage daga cikin 175 na farko — inda 15 aka yafe musu gaba ɗaya, hudu aka mayar musu da hukuncin kisa zuwa daurin rai da rai, sai kuma 15 da aka sassauta musu hukunci.

Sanarwar da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan labarai, Bayo Onanuga, ya sanya wa hannu ta ce an ɗauki wannan mataki ne don kare tsaron ƙasa da tabbatar da adalci ga waɗanda abin ya shafa.

A cewar sanarwar, an tura sabon jerin zuwa Hukumar Gidajen Yari ta ƙasa don aiwatarwa, tare da umarnin sauya sakatariyar kwamitin jinƙai zuwa Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya domin inganta tsarin.

Shugaba Tinubu ya kuma jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da yin gyare-gyare a fannin shari’a don tabbatar da adalci da daidaito ga kowa

TANZANIA: SHUGABA SAMIA SULUHU TA KIRA ‘YAN KASA SU CI GABA DA FITOWA KURI’AShugabar ƙasar Tanzania, Samia Suluhu Hassan...
29/10/2025

TANZANIA: SHUGABA SAMIA SULUHU TA KIRA ‘YAN KASA SU CI GABA DA FITOWA KURI’A

Shugabar ƙasar Tanzania, Samia Suluhu Hassan, ta bayyana godiya ga Allah da kuma ‘yan ƙasa bayan ta kada ƙuri’arta a garin Chamwino, tana mai kira ga jama’a da su ci gaba da fitowa su kada ƙuri’a cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya.

Zaɓen na bana yana zuwa ne a lokacin da gwamnati ke fuskantar ƙalubale daga jam’iyyun adawa da s**a koka kan takunkumin da hukumar zaɓe ta sanya, wanda s**a ce ya tauye musu damar shiga zaɓen.

Sai dai duk da waɗannan ƙalubale, gwamnatin Shugaba Samia ta samu yabo wajen ci gaban da ta kawo a fannoni na gine-gine da sufuri, musamman gina sabon jirgin ƙasa mai dogon zango da nufin haɓaka tattalin arziƙin ƙasa.

29/10/2025

Barkan ku da safiya fatan Kun tashi lafiya Allah yasa.

AlbarkaRadio Muna tare daku.

Masarautar Rano ta amince da murabus ɗin limamin babban masallacin Juma’aMasarautar Rano ta tabbatar da amincewar ta da ...
28/10/2025

Masarautar Rano ta amince da murabus ɗin limamin babban masallacin Juma’a

Masarautar Rano ta tabbatar da amincewar ta da murabus ɗin limamin babban masallacin Juma’a na garin Rano, Alhaji Nasiru Hassan Imam Rano, saboda dalilan shekaru.

A cewar sakataren yada labaran masarautar, Nasiru Habu Faragai, limamin ya jagoranci sallar Juma’a tun shekarar 1963 ya zuwa wannan lokaci.

Mai Martaba Sarkin Rano, Ambasada Dr. Muhammad Isah Umaru, ya yaba da hidimar da limamin da Na’ibinsa Rabi’u Imam Rano s**a bayar kafin yin murabus saboda dalilan lafiya da shekaru.

Tinubu ya nemi Majalisar Dattawa ta tabbatar da sabbin hafsoshin tsaroShugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya tura wasika zuw...
28/10/2025

Tinubu ya nemi Majalisar Dattawa ta tabbatar da sabbin hafsoshin tsaro

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya tura wasika zuwa Majalisar Dattawa yana neman ta tabbatar da sabbin hafsoshin tsaro da ya nada bayan sauye-sauyen da aka yi a manyan mukaman rundunar sojin Najeriya.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ne ya karanta wasikar shugaban kasa yayin zaman majalisar a yau Talata, inda ya bayyana sunayen wadanda ake neman tabbatarwa da su:

Janar Olufemi Oluyede – Babban Hafsan Tsaro (CDS)

Manjo-Janar Waheedi Shaibu – Babban Hafsan Sojojin Kasa (COAS)

Rear Admiral Idi Abbas – Babban Hafsan Sojan Ruwa (CNS)

Air Vice Marshal Kennedy Aneke – Babban Hafsan Sojan Sama (CAS)

Manjo-Janar Emmanuel Undiendeye – Babban Daraktan Leken Asiri na Tsaro (CDI)

A cikin wasikar, Tinubu ya bukaci majalisar da ta gaggauta amincewa da nadin , yana mai cewa hakan na da matukar muhimmanci wajen karfafa tsarin tsaron kasa da inganta ayyukan soji.

Majalisar ta tura bukatar zuwa babban kwamitin (‘Committee of the Whole’) domin gudanar da tantancewa da tabbatarwa a mako mai zuwa.

Wannan sauyi na zuwa ne bayan sauya manyan hafsoshin soji, inda Janar Oluyede ya maye gurbin Janar Christopher Musa a matsayin Babban Hafsan Tsaro, yayin da Manjo-Janar Undiendeye ya ci gaba da rike mukaminsa na Babban Daraktan Leken Asiri.

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Sunday Dare, ya ce wannan mataki na cikin kokarin gwamnatin Tinubu na inganta tsaron kasa da kara kwarewar rundunonin sojin kasar.

28/10/2025

AlbarkaRadio Muna tare daku a Koda yaushe.

28/10/2025

Jama,a barkan ku da safiya a ya kuka wayi gari a yankunan ku

28/10/2025

Har Yanzu Tsohon gwamnan jahar jigawa Bai samu damar siyam fom din takarar kujerar Shugabancin jamm,iyyar PDP ba.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Albarka Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share