11/04/2026
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci manyan jami’an tattalin arziki na Nijeriya da su gaggauta fito da matakan rage radadin da rikicin Gabas ta Tsakiya ke jefa wa ‘yan ƙasa.
Shugaban ya bayar da umarnin ne a ranar Juma’a yayin wata liyafa da aka shirya masa a Yenagoa bayan kaddamar da wasu ayyuka da Gwamnan Bayelsa, Douye Diri ya aiwatar.
Ya ɗora wa Ma’aikatar Kuɗi da Tsare-tsare tare da shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya, Didi Esther Walson-Jack, alhakin nemo hanyoyin sauƙaƙa wa talakawa matsin tattalin arziki.
A cikin sanarwar da kakakin shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya amince cewa rikicin duniya ya ƙara tsananta tsadar rayuwa, musamman ta fuskar farashin man fetur.
“Ina jin koke-kokenku… farashin mai na matsawa, amma dole mu yi la’akari da abubuwan da ke faruwa a duniya,” in ji shi.
Ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta yi aiki tare da masana domin samar da hanyoyin rage wannan nauyi da ke kan al’umma.
Shugaban ya kuma jaddada aniyar APC na inganta rayuwar jama’a ta hanyar ayyukan raya ƙasa kamar hanyoyi, gadoji, wutar lantarki da samar da ayyukan yi.
A ziyarar tasa, Tinubu ya ƙaddamar da wasu manyan ayyuka ciki har da tashar wutar lantarki mai ƙarfin megawatt 60 a Elebele, gadar Angiama zuwa Oporoma, da kuma sabuwar hanyar shiga birnin Yenagoa.
Ya yaba wa Douye Diri kan haɗin gwiwa da gwamnatin tarayya, yana mai cewa wannan ne mabuɗin samun ci gaba cikin sauri.
Kafin kammalawa, shugaban ya buƙaci mahalarta taron su yi shiru na minti guda domin karrama sojojin da s**a rasu da kuma tsohon gwamnan Diepreye Alamieyeseigha.
A nasa jawabin, Gwamna Diri ya ce goyon bayan gwamnatin tarayya ya taimaka wajen kammala ayyukan wutar lantarki da za su bunƙasa tattalin arziki da rayuwar al’umma.
Me zaku ce. ?