Jigawa Online TV

  • Home
  • Jigawa Online TV

Jigawa Online TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jigawa Online TV, TV Channel, .

Ziyarar Mataimakiyar Sakataren Ƙungiyar Ƙasashen Duniya (UN), Hajiya Amina J. Mohammed, Zuwa Wajen Mai Girma Gwamnan Jih...
20/07/2025

Ziyarar Mataimakiyar Sakataren Ƙungiyar Ƙasashen Duniya (UN), Hajiya Amina J. Mohammed, Zuwa Wajen Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf

Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya karɓi baƙuncin Mataimakiyar Sakataren Ƙungiyar Ƙasashen Duniya (UN), Hajiya Amina J. Mohammed, wadda ta kai ziyarar aiki zuwa Kano.

Ziyarar na cikin yunƙurin ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin Gwamnatin Jihar Kano da Majalisar Ɗinkin Duniya wajen aiwatar da manyan manufofin cigaban duniya (SDGs), musamman a fannonin ilimi, ƙarfafa matasa da mata, da sauya fasalin muhalli.

Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna godiya bisa wannan ziyara tare da yabawa irin tallafi da goyon bayan da ƙungiyar ke baiwa jihar Kano. Ya kuma bayyana aniyar gwamnatinsa na ci gaba da aiki tukuru don cimma burin ci gaban al’umma da daidaito.

A nata jawabin, Hajiya Amina J. Mohammed ta bayyana jin daɗinta da kokarin da gwamnatin Kano ke yi wajen inganta rayuwar jama'a, tare da jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da ƙungiyoyi domin kawo ci gaba mai ɗorewa.

Ziyarar ta haɗa da ganawa da manyan jami’an gwamnati, wakilan ƙungiyoyin haɗin gwiwa, da wakilan al’umma, domin tattauna hanyoyin ƙarfafa haɗin kai.

© Shehu Saleesu Farawa ✍️

Matuƙar Ana, Buƙatar Samar Da Nagartattun Mutane Amatsayin Shuwagabanni Dole ne al-ummar Nigeriya mu kaucewa tsarin siya...
03/07/2025

Matuƙar Ana, Buƙatar Samar Da Nagartattun Mutane Amatsayin Shuwagabanni Dole ne al-ummar Nigeriya mu kaucewa tsarin siyasar sak.

Babu jam'iyyar da bata da mutanen kirki Acikin ta sannan babu jam'iyyar Da Bata da mutanen banza, Acikin ta,

Kamar yadda Shuwagabanni da wakilai suke manta Banbancin jam'iyyar siyasa idan s**a haɗu muma talakawan Najeriya lokaci yayi da zamu jingine batun jam'iyyar siyasa mu duba chancanta.

Tsarin yadda kiristocin Nigeriya s**a yi wajen zaɓen 2023 matuƙar akabi, irinsa babu Abinda zai hana Nigeriya samun damar zaɓar Shuwagabanni Nagari.

A zaɓen 2023 kiristoci sun tsayar da Peter Obi amatsayin ɗan takara ɗaya tilo na shugaban kasar Nigeriya, a jam'iyyar LP Sannan sun bawa jama'ar su damar kowa ya zaɓi duk ɗan takarar da yake so a sauran Kujerun siyasa, a kowace jam'iyya, a shugaban kasa ne s**a haɗu wajen ra'ayi ɗaya.

Akwai mutanen da guguwar sak tabasu Nasarar samun Shugabanci ko wakilcin Al-ummah Sai gashi Manufar sa ta sauya kan yadda mutane s**a yi tunanin samun Shugabanci nagari daga wajen su.

© Shehu Saleesu Farawa ✍️

GANDUJE YANA TSAKA MAI WUYA.....Ganduje Laifi yayiwa shugaban ƙasa Bola Tinubu ya sauke daga shugabancin jam'iyyar APC D...
29/06/2025

GANDUJE YANA TSAKA MAI WUYA.....

Ganduje Laifi yayiwa shugaban ƙasa Bola Tinubu ya sauke daga shugabancin jam'iyyar APC Dan haka komai Za'a yiwa Ganduje bai'isa yafice daga jam'iyyar APC saboda tsoron tuhuma.

Ku daina yaudarar kanku da cewa za'a bawa Ganduje kujerar sakataren gwamnatin tarayya ko kuma kujarar mataimakin shugaban ƙasar Nigeriya domin ba saboda dalilin bawa Ganduje wani muƙami bane yasa, aka sauke shi daga shugabancin jam'iyyar APC Na ƙasa.

Matuƙar Ganduje ya biyewa zugar ƴan Koren sa yace zai yi tutsu a shirye hukumar EFCC take ta gayyace shi kan zargin cin hanci da rashawa Sannan kuma itama gwamnatin Kano tana iya samun damar chafke shi domin gabatar da shi gaban Muhuyi Magaji domin ya titsiya shi kan dukiyar kanawa da yayi Sama da faɗi da ita.

Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) a Jihar Jigawa a zaɓen shekarar 2023, Malam Aminu Ibrah...
29/06/2025

Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) a Jihar Jigawa a zaɓen shekarar 2023, Malam Aminu Ibrahim Ringim, ya bayyana cewa mambobin jam’iyyar na jiran umarnin Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso.

Ringim ya bayyana haka a wata hira da DAILY POST yayin da yake mayar da martani kan jita-jita game da matakin da jam’iyyar za ta ɗauka kafin zaɓen 2027.

Dole ne Ƙasar Iran Ta Cire Tsoro Tayi Koyi Da Ƙasar Korea Ta, Arewa Matuƙar Suna Son Mallakar Mak**an Nukiliya.Babu bara...
22/06/2025

Dole ne Ƙasar Iran Ta Cire Tsoro Tayi Koyi Da Ƙasar Korea Ta, Arewa Matuƙar Suna Son Mallakar Mak**an Nukiliya.

Babu barazanar Da shuwagabanin Amurka Basu yiwa shugaban ƙasar Korea Lokacin Da Suke haɗa Mak**an Nukiliyar su Amma basuji tsoro ba.

Da shugaban ƙasar Donald Trump ya matsawa Korea a wancan Lokacin kaitsaye s**a bayyana cewa Zasuyi gwajin mak**an su Na nokiliyar su Akan ƙasar Amurka Daga ƙarshe shugaban Amurka Da kansa ya nemi shugaban korea s**a sulhunta Lamarin Da ya kasance cikin tarihi bayan tsawon Shekaru shugaba Trump ya kasance shugaban Amurka Na Farko Da ya gana Da shugaban Korea.

Lokaci yayi Da yak**ata ƙasar Iran ta zaɓi Rana tayi gwajin mak**an ta Na nokiliya ba tare Da Jin tsoron kowacce ƙasa Matuƙar s**a Yi haka Suma, a ƙarshe za'a neme su ne ayi Sulhu.

Babu Wata tattaunawar diflomasiyya Da Zata sanya ƙasashen kafurai su amince ƙasar Iran ta mallaki makamin nokiliya domin sunsan Mutanen ƙasar Iran bazasu Bari ajuyasu Kamar yadda, ake juya Sauran shuwagabanin ƙasashen Larabawa Da shuwagabanin ƙasashen Africa.

©Shehu Saleesu Farawa ✍️

YANZU-YANZU: Gidan Talabijin na Gwamnatin Iran zai Haska fuskokin matukan jirgin yakin F-35 na Isra'ila da ke hannun run...
17/06/2025

YANZU-YANZU: Gidan Talabijin na Gwamnatin Iran zai Haska fuskokin matukan jirgin yakin F-35 na Isra'ila da ke hannun rundunar sojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Babban Abin mamaki shine, yadda Iran ta kamo jirgin Isra'ila ta sako da shi duk da irin girman fasahar da jirgin ke ƙunshe da shi.

SHAWARA ZUWA GA HUKUMAR KAROTA.Ɗazu da Yamma nazo Wucewa ta gadar hotoro naga yadda sojoji s**a yiwa ƴan karotan da suke...
11/06/2025

SHAWARA ZUWA GA HUKUMAR KAROTA.

Ɗazu da Yamma nazo Wucewa ta gadar hotoro naga yadda sojoji s**a yiwa ƴan karotan da suke aiki a wajen Lamarin ya bani tausayi musamman yadda naga, ana yiwa jami'an karota...Dana tambayi mutanen da suke wajen s**a ce jami'an KAROTA ne s**a daki wani jami'in soja shine ƴan uwan sojan s**a zo Ramawa sojan.

A lokacin Da Naga Lamarin ya faru kai tsaye sojojin na Ɗorawa laifi sak**akon yadda s**a biyewa dokin zuciya wajen zuwa ɗaukar fansa kan Abinda, aka yiwa ɗan uwan su Domin Ni atawa Fahimtar maimakon wannan mataki da sojojin s**a ɗauka gwanda su shigar da korafin su a hukumar domin ta ɗauki mataki kan jami'in karotan.

Sannan kuma su kansu jami'an KAROTA Yak**ata su Canza salon aiki ta hanyar yin Amfani da Siyasa wajen hukunta wanda s**a k**a maimakon yiwa wanda, aka k**a taron dangi Dan yayiwa jami'an hukumar KAROTA Turjiya.

Yak**ata MD na KAROTA Hon Faisal Mahmud Kabir ya buƙaci gwamnati tabasu jami'an tsaron da zasu dinga shiga cikin ƴan karota domin basu kariya, a lokacin da suke gudanar da, aikin su.

© Shehu Saleesu Farawa

Matsalar Ƴan Social Media Na Kwankwasiyya Bamu Cika Zama Sanadin Warware Rikicin Gida Na Kwankwasiyya Sai Dai Mu Ƙara Ta...
08/06/2025

Matsalar Ƴan Social Media Na Kwankwasiyya Bamu Cika Zama Sanadin Warware Rikicin Gida Na Kwankwasiyya Sai Dai Mu Ƙara Ta'azzara Rikicin.

Banga Laifin Zaɓaɓɓen ɗan majalisar tarayyar DTR don yace mai girma Gwamnan jihar Kano yaja kunnen DG. Sanusi Bature D-Tofa domin yana yunƙurin haddasa rikicin cikin gida, a kwankwasiyyar DTR.

A kwanakin baya DG. Sunusi Bature yayi kalaman yabo ga wanda yayiwa jam'iyyar APC takarar majalissar Tarayyar DTR wato Abba Ganduje Ni atawa Fahimtar Sunusi Bature ya yabawa, Abba Ganduje ne domin zaburar da Hon Abdulƙadir Joɓe kan ya gyara.

A yanzu kuma, alamu sun gama bayyana kan DG. Sunusi Bature yana son yi takarar majalissar Tarayyar kananan hukumomin DTR lamarin da yasa magoya bayan Joɓe suke kokarin mai da martani bisa yadda magoya bayan DG. Sunusi Bature suke tallata gazawar Joɓe a yenkin domin samun karɓuwar ɗan takarar su wato DG. Bature.

Maimakon ƴan media na Kwankwasiyya muyi jan hankali ga ɓangarorin suyi haƙuri su fahimci juna mun ɓuge da kokarin ƙara iza wutar Rigimar.

Muna roƙon Allah ubangiji ya zaunar da kwankwasiyya ya ƙara haɗa kan magoya bayan ta.

© Shehu Saleesu Farawa

Cikin Hotuna:Mai martaba Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sanusi II ya gudanar da hawa a yammacin Asabar din nan, inda ya k...
07/06/2025

Cikin Hotuna:

Mai martaba Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sanusi II ya gudanar da hawa a yammacin Asabar din nan, inda ya kai gaisuwa ga mahaifiyarsa. Sarkin yasamu Rakiyar Dandazon masoyansa.

Ina mutanen mai gardama sarkin ƴan Dambe ya labarin jami'an tsaron da kuke cewa zasu hana mai martaba sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi II Gudanar da hawa to sarki yayi hawa ya kukaji a ranku.😂😂😂

Har Yanzu Babu Abinda yake Ɓatawa maƙiya Jihar Kano Rai Kamar kayakyawar Alaƙar dake tsakanin jagora Kwankwaso Da gwamna...
02/06/2025

Har Yanzu Babu Abinda yake Ɓatawa maƙiya Jihar Kano Rai Kamar kayakyawar Alaƙar dake tsakanin jagora Kwankwaso Da gwamna Abba Kabir Yusuf.

Tunda, ƴan tsaya Da Ƙafarka s**a kasa raba wannan Alaƙa Bana tunanin Akwai sauran makircin Da Zai raba kwankwaso Da, Abba don haka masu wannan yunƙuri su daina wahalar Da kansu.

An Haddasa Rigimar Masarautar Kano domin ragewa kwankwasiyya farin jini a faɗin Jihar Kano sunga basuyi Nasara ba shine s**a Yi yunƙurin lalata, Alaƙar kwankwaso Da Abba ta hanyar ƙiƙirar ƴan tsaya Da Ƙafarka gashi wannan hanya itama Taki ɓullewa.

A halin Yanzu mafi Yawancin al-ummar Jahohin Nigeria Suna kwantata gwamnatin Abba, Amatsayin wacce take Basu sha'awa don haka koda kwankwaso ne yake juya gwamntin jihar Kano mu a wajen alheri ne domin Yana Ɗora gwamnatin Akan Hanyar Daidai,

Muna roƙon Allah ubangiji ya ƙara Karya maƙiya kwankwasiyya.

© Shehu Saleesu farawa ✍️

Har Yanzu jagora Kwankwaso Bai Ce komai ba Kan Jitajitar k**awarsa Jamiyyar APC Amma Duk sun bi sun Tashi Hankalin Su.Na...
07/05/2025

Har Yanzu jagora Kwankwaso Bai Ce komai ba Kan Jitajitar k**awarsa Jamiyyar APC Amma Duk sun bi sun Tashi Hankalin Su.

Na farko Shi Abdullahi Ata ɗan siyasa ne Da bashi Da tasiri a local government ɗinsa ma ballantana Kuma, a Harkar siyasar Kano shiyasa Bamu Damu Da soko burutsun Sa ba.

Yak**ata duk ɗan kwankwasiyya ya Daina damuwa Da barazanar Audu tsiya-tsiya Domin surutun Sa Baya Hana kwankwasiyya taci zaɓe tun Daga, akwatin Sa zuwa Mazaɓar Sa Da Local government ɗinsa.

Shi Kuma kantoman Jamiyya kuyi masa Uzuri tasa matsalar ƙarama ce Domin umarni Kawai za'a bashi Daga fadar shugaban ƙasa yazo yayiwa jagora Kwankwaso mubayi'a Kuma Na tabbata Bai, Isa yace bazai Zo ba domin Idan yaƙi zuwa ma EFCC Zata dawo Dashi Kan layi.

A Shawarce Kowanne ɗan jam'iyyar APC ya shafawa zuciyar Sa Ruwan Sanyi ya Daina surutun banza Domin bazai amfanar Dashi Komai ba shigowa Kuma Sai Mun shigo Wanda ya Isa ya Hana mu ya tare ƙofa.

© Shehu Saleesu Farawa ✍️

A Wannan Rana Marigayi Tsohon Shugaban kasar Najeriya Alhaji Ummaru Musa Yar Addu'a Yake Cika Shekara 15 Da Rasuwa.A ran...
05/05/2025

A Wannan Rana Marigayi Tsohon Shugaban kasar Najeriya Alhaji Ummaru Musa Yar Addu'a Yake Cika Shekara 15 Da Rasuwa.

A rana mai k**ar ta yau ce shekaru 15 da s**a gabata 5 ga watan May 2010 aka yi janaizar tsohon shugaban kasa Alh. Umar Musa Yar'adua a mahaifarsa jihar Katsina.

Ummaru Musa ya zama shugaban kasa na farko mafi kwazo da tausayin Talaka wanda ya mutu da burin ganin Najeriya ta samu ci gaba mai ɗorewa ta kowace fuska.

Hakika a wancen lokacin wannan hotunan jana'izar marigayin sun sanya dubben 'yan Najeriya zubar da kwalla.

Allah gafartawa Malam Umaru Musa Yar'adua tare da sauran musulmi baki ɗaya.

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jigawa Online TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share