Hausa Trust News

  • Home
  • Hausa Trust News

Hausa Trust News Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Hausa Trust News, TV Channel, .

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin jihar Gombe za ta kirkiri sabbin kananan hukumomi guda (13). Ga jerin sabbin kananan hukumomin d...
13/08/2025

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin jihar Gombe za ta kirkiri sabbin kananan hukumomi guda (13).

Ga jerin sabbin kananan hukumomin da za a kafa tare da hedikwatocinsu;

Ga jerin su kamar haka;

1. Akko Arewa (Hedikwata: Amada)

2. Akko Yamma (Hedikwata: Pindiga)

3. Balanga Kudu (Hedikwata: Bambam)

4. Billiri Yamma (Hedikwata: Tal)

5. Dukku Arewa (Hedikwata: Malala)

6. Funakaye Kudu (Hedikwata: Tongo)

7. Gombe Kudu (Hedikwata: Bolari)

8. Kaltungo Gabas (Hedikwata: Wange)

9. Kwami Yamma (Hedikwata: Bojude)

10. Nafada Yamma (Hedikwata: Birin Fulani)

11. Pero-Chonge (Hedikwata: Filiya)

12. Yamaltu Gabas (Hedikwata: Hinna)

13. Yamaltu Yamma (Hedikwata: Zambuk).

“YADDA ƳAN SANDA S**A K**A NI, BA TARE DA SANIN CEWAR NINE KWAMISHINAN ƳAN SANDA BA” – MD ABUBAKAR“A lokacin da nake Kwa...
08/08/2025

“YADDA ƳAN SANDA S**A K**A NI, BA TARE DA SANIN CEWAR NINE KWAMISHINAN ƳAN SANDA BA” – MD ABUBAKAR

“A lokacin da nake Kwamishinan Ƴan Sanda a jihar Lagos, bana wasa da aiki — musamman ranar Asabar. Ko da yake ayyuka na suna farawa ne daga karfe 10 na safe, wannan rana na tashi tun 6 na safe don in kai ziyara ba tare da sanarwa ba.

Na hau motata Jeep na nufi ofis, amma sai na yanke shawarar yin ‘yin ziyarar ba-zata’ ga wasu 'yan sanda a kan hanya – domin in ga irin yadda suke gudanar da aikinsu.

A wani shingen bincike “checkpoint” dake t**in Herbert Macaulay, wasu matasan 'yan sanda s**a tsaida ni. Wani karamin dan sanda (constable) ya kalle ni yace:

> "Kai saurayi, ina zaka ne da motar mahaifinka?"

Ya bukaci takardun motar da shaidar lasisin tuƙi. Na ce masa sunana Mohammed. Yace dole sai na nuna ID card. Na ce masa, to ya fara nuna mini nasa. Bai da ID card, don haka sai ya kira sergeant dinsu.

Shi ma sergeant din ya bukaci ID card dina, na ce masa ya nuna mini nasa kafin nawa. Ganin bana jin tsoro ko nuna daraja, sai s**a ce mu tafi ofishin ‘yan sanda na Yaba (Panti) domin “gano ko ni wanene”.

Muna isa station – babu parking sai a wajen DPO. Na ajiye motata a can, constable din ya fusata yace: “Wannan wajen parking din DPO ne fa!” Ko uffan ban ce masa ba.

Bayan mun shiga ciki, sai s**a kaini wurin wani ASP (Assistant Superintendent of Police) wanda ke sanye da gajeren wando 'shorts'!. Yace na shigo, na ki, nace masa ba zai yiwu ya tuhumeni cikin kayan gida ba. Yayi fushi ya jawo ni ciki da ƙarfi – nima ina jan shi. Da ya duba fuskata da kyau sai ya fara zare ido…

A gefe guda, wani tsoho da ke ofishin ya leƙa ofishin DPO don duba hoton shugabannin rundunar Ƴan sanda dake jikin bango. Da ya tabbatar cewa ni ne, sai kawai ya tsallake taga ya gudu!

Sergeant da ya kawo ni ya kasa gane me ke faruwa, har sai da wani Ɗan sanda ya matso kusa da kunnensa, ya ce masa: “Kai, CP ne wannan fa!”.

Cikin firgici, ASP ɗin da ke sanye da shorts ma ya bi taga ya gudu!

Bayan haka, Area Commander ya kirani ya tambaya me ya faru. Aka gaya masa cewa an tsare DPO, ASP, da sauran ‘yan sanda da s**a shiga lamarin – suna jiran umarni na.

Abin da ya fi tada min hankali ba wai kamun da s**a yi min ba ne – a’a, amma irin yadda s**a nuna rashin tarbiyya, rashin horo, da rashin kwarewa a aiki.

Yaya dan sanda zai tsaya a t**i ba tare da ID ba, yana tsare jama’a? Yaya ASP zai zauna da kaya irin na gida yana sarrafa aiki? Wannan ya kara tabbatar min da cewa shugabanci ba sai ka zauna ofis ba – dole ka fita ka duba, ka gani da idonka, ka tabbatar da gaskiya da adalci a kowanne mataki.

Fassara: AB Damare

'Yan Kwankwasiyya Suna Cikin Wahala Ba'a taimakonsu kullum da shegiyar hula  yar N200 Suke yawo jama'a in sun gan Mu dau...
05/08/2025

'Yan Kwankwasiyya Suna Cikin Wahala Ba'a taimakonsu kullum da shegiyar hula yar N200 Suke yawo jama'a in sun gan Mu dauka Suke mune Masu Gwamnati.

Cewar ~ Abdullahi Abbas Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar Kano.

Idan Aka Zaɓe Ni Zan Yi Wa'adi Ɗaya Na Shekaru 4 Na Sauka Daga Mulki, Cewar Peter Obi Tsohon ɗan takarar shugabancin Naj...
03/08/2025

Idan Aka Zaɓe Ni Zan Yi Wa'adi Ɗaya Na Shekaru 4 Na Sauka Daga Mulki, Cewar Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter Obi ya ce idan ya samu nasarar zama shugaban ƙasar, wa'adi ɗaya na shekara huɗu kawai zai yi kamar yadda ya yi alƙawari.

Obi ya bayyana haka ne a shafinsa na X, inda ya ce ko tsohon shugaban Amurka, Abraham Lincoln wa'adi ɗaya ya yi na shekara huɗu, "sannan John F. Kennedy bai ma ƙarasa wa'adi ɗaya ba, amma ana cigaba da tunawa da su a matsayin shugabanni masu adalci."

Ya ce ko a Afirka, Nelson Mandela ya zama abin koyi a duniya wajen shugabanci na adalci, "amma wa'adi ɗaya kawai ya yi."

"Ba daɗewa a ofis ba ne ke alamta nasara, irin ayyukan da shugaba ya yi ne za a riƙa tunawa. Saboda haka ne nake sake nanata alƙawarin da na yi cewa wa'adi ɗaya na shekara huɗu kawai zan yi idan na zama shugaban Najeriya," in ji shi.

Ya ƙara da cewa ya san ƴan Najeriya ba su cika yarda da maganar ƴan siyasa ba, "amma duk da haka akwai masu cika alƙawari."

"Na ga wani yana rubuta cewa ko da me zan rantse ba zai yarda cewa wa'adi ɗaya zan yi ba, wani kuma ya ce duk wanda ya ce wa'adi ɗaya zai yi ya je asibitin ƙwaƙwalwa."

Obi ya ce ya fahimci abin da suke nufi, amma a cewarsa, yana da tarihi mai kyau wajen cika alƙawari tun daga lokacin da ya fara siyasa a Anambra, inda ya ce wata 48 sun isa duk wani shugaba da ya shirya mulki ya yi abin da ya dace.

"Idan na zama shugaban Najeriya a wa'adi ɗaya zan magance matsalar tsaro, zan yaƙi da talauci in inganta aikin gwamnati, sannan zan fifita ɓangaren ilimi da kiwon lafiya, sannan in yaƙi cin hanci da rashawa. Sannan uwa-uba zan inganta ɓangaren noma ta hanyar amfani da kimiyya da fasaha domin Najeriya ta zama ƙasa.

Daily Nigerian Hausa

Kalli Yadda Bikin Baje Kolin Dabino Mafi Girma Na Duniya Ke Gudana A Yankin Buraidah Dake Kasar Saudiyya.Shin Me Ke Burg...
03/08/2025

Kalli Yadda Bikin Baje Kolin Dabino Mafi Girma Na Duniya Ke Gudana A Yankin Buraidah Dake Kasar Saudiyya.

Shin Me Ke Burge Ku Game Da Dabino?

Hotuna: Fb/KSA Expats

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gy...
02/08/2025

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gyara Jam’iyya Cikin Gaskiya

Ofishinmu na Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) yana bayyana damuwarsa matuka kan yadda wasu sarakunan gargajiya ke kiran waya da nufin matsin lamba ga Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar, Alhaji Nafiu Bala Gombe, domin ya sauya matsayinsa na kare tsarin dimokuradiyya da doka na jam’iyyar.

Wannan barazana da kuma kiran da ake yi ga wasu mambobin Kwamitin Zartaswa na Kasa (NWC) domin su ja da baya daga goyon bayan shugabansu, abin takaici ne kwarai, musamman ganin cewa sarakuna sun bar turbarsu ta raya al’adu da zaman lafiya, sun rungumi muradin wasu 'yan siyasa masu son karbe jam’iyya ta kowane hali.

MAKIRCI NA BAYA-BAYAN NAN

Bayanan sirri daga majiya mai karfi na nuni da cewa wasu manyan ’yan siyasa da s**a hada da Janar David Mark da Mallam Nasir El-Rufai da wasu gungun mutane sun hada wata kungiya da ke shirin tura dattawa su je Gombe domin matsawa mahaifiyar Shugaban rikon kwarya da nufin tilasta masa mika jam’iyyar da nufin cinma burinsu na siyasa a shekarar 2027.

Wannan yunkuri na ziyarar mahaifiyar Shugaban jam’iyyar abu ne da ba za mu lamunta da shi ba. Hakan na nuna cewa wasu sun sadaukar da dimokuradiyya ga son zuciya da yin coge don biyan muradinsu na 2027.

1. Muna da tabbaci daga bayanen sirri masu inganci cewa wadannan sarakuna na kokarin tilasta Alhaji Nafiu Bala Gombe ya mika jam’iyya ga 'yan siyasa masu matasanancin kwadayin mulki ta hanyar matsa masa da kiraye-kiraye a wayarsa tare da shisshigi a boye. Wadannan sarakuna ba su kyauta ba, saboda suna neman rage kima da martabar al'adunmu masu nagarta ta hanyar neman zama 'yan koren masu mayatar son mulkin siyasa a shekarar 2027. Wannan abin jimami ne ga dukkan mai kishin martabar masarautinmu.

2. Wannan kuskure ne mai muni daga bangaren sarakuna, wadanda ya kamata su tsaya a gefe su kasance iyayen kasa masu kima.

3. Mu na kara fayyacewa: Sarakuna ba su da hurumin shiga harkokin jam’iyyar ADC ko zama 'yan gada-gadar 'yan siyasa. Wannan ba shekarar 1983 ba ce; yanzu idon kowa a bude yake. ADC ba ta sayarwa ba ce!

4. Alhaji Nafiu Bala Gombe ba zai ja da baya ba, yana da cikakken goyon bayan dokokin jam’iyya da mambobinta masu kishin kasa.

5. Wadanda suke fakewa da cewa suna hidimar “sasantawa”, yaudarar jama'a suke, da nufin biyan muradin 'yan cogen Hadaka ta Zaben 2027. Su sani cewa za mu bayyana sunayensu da cikakken bayani game da boyayyiyar manufarsu, in bukatar yin hakan ta taso.

6. Ga wadanda suke matsayin sarakuna amma s**a tsunduma siyasa da goyon bayan hargitsi, muna ba ku shawara: ku koma ku kula da masarautunku. Kada ku sayar da martabarku da al'adunmu masu nagarta don biyan bukatun 'yan siyasan da s**a shahara wajen yaudarar al'umma shekara da shekaru.

MATSAYARMU A KAN WANNAN KATSALANDAN:

Jam’iyyar ADC ba ta sayarwa ba ce. Ba za mu bar makircin wasu mayaudaran 'yan siyasa ya kassara mulkin dimokuradiyyan kasar nan ba, ko ya lalata alkiblar jam’iyyar ADC ba. Kuma za mu fallasa kowane mai hannu a ciki — ko saraki ne shi ko dan bangar siyasa.

In kunne ya ji, jiki ya tsira.

Sanya hannu:
Dr. Aminu Sani Alhassan
Mai Baiwa Shugaban Rikon Kwarya Shawara kan Harkokin Jama’a
Jam'iyyar African Democratic Congress (ADC)
Abuja

Gwamnatin APC Ta Jefa Ƴan Najeriya Cikin Kangin Talauci, Cewar Shugabar LPMuƙaddashiyar Shugabar Jam’iyyar LP, Sanata Ne...
27/07/2025

Gwamnatin APC Ta Jefa Ƴan Najeriya Cikin Kangin Talauci, Cewar Shugabar LP

Muƙaddashiyar Shugabar Jam’iyyar LP, Sanata Nenadi Esther Usman, ta ce gwamnatin APC ce ta fi jefa ’yan Najeriya cikin talauci sama da kowace gwamnati a tarihin ƙasar nan.

Riding Motorbike Alone Across Laos - Beautiful Memories from LAOS - Nếm TV

Da ta ke zantawa da manema labarai a Jihar Kaduna, Sanatan ta ce jam’iyyar LP ta shirya tsaf don gyara kurakuran da gwamnatin APC ta tafka.

Gwamna Bauchi ya sasanta manoma da makiyaya a Darazo
Ambaliya ta yi ajalin mutane, ta lalata gidaje a Adamawa
Ta roƙi ’yan Najeriya da su bai wa LP goyon baya, inda ta ce jam’iyyar za ta kawo canji na gaskiya.

Ta ce halin da ake ciki na wahala a ƙasar nan ya yi muni ƙwarai, kuma ta d6ora alhakin hakan kan gwamnatin APC.

Game da sauya sheƙa da wasu ’yan siyasa ke yi daga jam’iyyun adawa zuwa APC, ciki har da wasu daga LP, Sanatan ta bayyana hakan a matsayin abin takaici da rashin sanin darajar kai.

A cewarta, ba daidai ba ne mutum ya samu madafun iko da tallafin wata jam’iyya, amma daga baya ya koma wata jam’iyya don kawai samun riba ba.

Sai dai ta ce wannan ba zai girgiza jam’iyyarsu ba, domin ƙarfin jam’iyyar na ƙara bayyana da goyon bayan talakawan Najeriya.

Sanata Esther ta amince cewa jam’iyyar ta yi wasu kurakurai a baya, musamman wajen zaɓen ’yan takara da ba su dace da manufofin jam’iyyar ba.

Amma ta tabbatar da cewa sun ɗauki darasi, kuma suna shirin yin gyara kafin babban zaɓe na gaba.

“Yawancin waɗanda s**a bar jam’iyyar ba su da cikakken ƙudirin kafa sabuwar Najeriya. Ficewarsu ta sa mun fi fahimtar juna kuma ta ƙara mana ƙarfi,” in ji ta.

Ta roƙi mambobin jam’iyyar da aka ɓata ws raj da su manta da saɓanin, su haɗa kai domin ƙarfafa jam’iyyar.

Ta ce ana shirin gudanar da zaɓen shugabanni a matakin ƙasa da kuma babban taron ƙasa kuma Majalisar Zartarwar Jam’iyyar (NEC) ta amince da waɗannan sauye-sauye da suke buƙata.

Majiya: Aminiya

Ina Mai Bada Hakuri Kan Wannan Hoton Da Na Sa Aka Dauke Ni Ina Baiwa Mara Lafiya Tallafin Omo A Asibiti, Tabbas Na Yi Ku...
26/07/2025

Ina Mai Bada Hakuri Kan Wannan Hoton Da Na Sa Aka Dauke Ni Ina Baiwa Mara Lafiya Tallafin Omo A Asibiti, Tabbas Na Yi Kuskure, Inji Mutumin

YANZU YANZU: Na koma jam'iyyar Apc ne Saboda Tausayin talakawa, Na bar jam'iyyar NNPP na koma APC ne don samar wa al'umm...
23/07/2025

YANZU YANZU: Na koma jam'iyyar Apc ne Saboda Tausayin talakawa, Na bar jam'iyyar NNPP na koma APC ne don samar wa al'ummar yankina abin da zai amfanar da su, inji Kawu Sumaila

ɗan majalisar dattawa daga jihar Kano, Sanata Abdurahman Kawu Sumaila wanda ya fice daga NNPP ya koma APC, ya bayyana dalilinsa na ɗaukar matakin.

Ya kuma ce nan gaba akwai wasu ƙarin ƴan jam'iyyar NNPP a jihar da su ma za su fice daga jam'iyyar.

YANZU-YANZU : An sallami Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD daga Asibiti.
22/07/2025

YANZU-YANZU : An sallami Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD daga Asibiti.

Karya Ce Tsagwaronta: Muhammad Babangida Bai Ƙi Nadin Da Shugaba Tinubu Yayi Masa Ba Wasu mutane masu ƙazamin nufi sun b...
21/07/2025

Karya Ce Tsagwaronta: Muhammad Babangida Bai Ƙi Nadin Da Shugaba Tinubu Yayi Masa Ba

Wasu mutane masu ƙazamin nufi sun bazu da wani labari mara tushe a kafafen sada zumunta da ke cewa Muhammad Babangida, ɗan tsohon shugaban kasa Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya ƙi amincewa da nadin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya masa na chairman BOA.

Mun tabbatar da cewa wannan labarin ƙarya ne tsagwaronta, domin ba Muhammad Babangida bane ya fitar da sanarwar da ke yawo ba. Lambar da ke jikin takardar da aka yaɗa da kuma sa hannun da ke cikinta duk ba nasa ba ne.

Wannan wata makirci ce ta ɓatanci da ƙoƙarin jefa shakku a tsakanin shugaban ƙasa da manyan 'yan Najeriya, musamman waɗanda ke da sunaye da martaba a cikin al'umma.

Muhammad Babangida bai fito ya musanta nadin ba, kuma babu wata cikakkiyar shaida daga gare shi ko daga hannunsa da ke nuna ya ƙi karɓar kujerar. Wannan yana nuni da cewa an ƙirƙiri wannan labari ne domin yaudarar jama'a da haddasa ruɗani.

Muna kira ga 'yan Najeriya da su yi hattara da labaran ƙarya da ake yawan yaɗawa, su nemi gaskiya daga ingantattun majiyoyi kafin yarda da kowace irin sanarwa.

Allah ya ƙara haɗin kanmu da cigaban ƙasar nan.

Kwamitin Gudunar Da Musabaqar Alqurani Mai Girma Na Jihar Kaduna Na Tuhumar Shugaban Ta Jamilu Abubakar Albani Na Jiha K...
21/07/2025

Kwamitin Gudunar Da Musabaqar Alqurani Mai Girma Na Jihar Kaduna Na Tuhumar Shugaban Ta Jamilu Abubakar Albani Na Jiha Kan Almundahana Da Rasahawa.

Kwamitin Ya Aikawa Gwamna Malam Uba Sani Na Jihar Kaduna Da Takarda Inda Ta Bukaci Gwamna Ya Tsige Shugaban Musabaqan Jamilu Albani Sannan a Bincike Shi.

Hakazalika Kwamitin Ta Aikawa Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Wanda Rt Hon Dahiru Imam Ke Jagoranta Da Takarda Inda Ta Nemi Majalisar Ta Gayyaci Shugaban Musabaqan Jamilu Abubakar Albani Domin Binciken Sa.

Kwamitin na san gwamnatin jihar Kaduna tayi abubuwa kamar haka;

1. Kwamitin na san gwamnatin jihar Kaduna ta cire Jamilu Albani Nan Ta ke daga ofishin shugaban Musabaqa
2. Kafa wani kwamitin bincike don binciken dukkan ayyukan da jamilu albani ya gudanar daga 2015.
3. Kwamitin nasan gwamnati Ta tursasa Jamilu Albani ya mayar da dukkan kadarorin musabaqa ga kwamiti domin ba mallakin sa bane.

Daga Usman Rabiu

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Trust News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share