KUKAN Kurciya

  • Home
  • KUKAN Kurciya

KUKAN Kurciya Domin samun Labarai da dumi-duminsu daga fadin Najeriya.

Liverpool ta dibi kaya a wajan Brentford Kwallaye 3 da 2Ya kuke ganin Liverpool a wannan kakan wasa ta 2025/26 ?
25/10/2025

Liverpool ta dibi kaya a wajan Brentford
Kwallaye 3 da 2

Ya kuke ganin Liverpool a wannan kakan wasa ta 2025/26 ?

LabaraiHisbah ta janye auren Mai Wushirya da ‘Ya Guda.Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta soke auren da ake shirin daurawa t...
25/10/2025

LabaraiHisbah ta janye auren Mai Wushirya da ‘Ya Guda.

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta soke auren da ake shirin daurawa tsakanin fitaccen jarumin TikTok mai barkwanci, Idris Mai Wushirya, da Basira ‘Yar Guda, bayan samun rahotanni da ke nuna akwai rashin fahimta da sabani tsakanin bangarorin biyu.

A cikin wani sautin murya da Mataimakin Babban Kwamandan Hisbah a sashen ayyuka na musamman, Dr. Mujahedeen Aminuddeen Abubakar, ya tura wa TST Hausa, ya bayyana cewa binciken da hukumar ta gudanar ya nuna cewa bangarorin biyu sun shiga maganar auren ne domin kauce wa wani lamari da ke gaban kotu, a yanzu an janye auren domin gudun rashin jituwa bayan auren nasu.

Ya ce hukumar ta dauki wannan mataki ne domin gujewa rikici da kuma tabbatar da cewa auren ya kasance cikin yardar juna da fahimtar duka masu ruwa da tsaki.

Rahotanni sun bayyana cewa hukumar Hisbah ta shiga lamarin ne bayan ce-ce-ku-ce da ta bulla a kafafen sada zumunta kan yadda aka tsara bikin da kuma wasu bayanai da ake ganin sun saba da ka’idojin aure na addinin Musulunci.

Dr Mujahideen yace hukumar Hisbah zata mayar da mutanen biyu zuwa kotu domin daukar mataki na gaba.

TST Hausa ta rawaito cewa batun auren Mai Wushirya da ‘Yar Guda ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta na zamani, inda Mai Wushirya kansa ya bayyana cikin wani bidiyo cewa “dama tsarota shi aka yi” ya amince da batun auren.

04/10/2025

Shugaban Kasa Ahmed Bola Tinubu ya sauka a Jos don yin ziyarar wuni daya

Bala Abdulkadir Muhammad (Kauran Bauchi) Gwamnan Jihar Bauchi
25/09/2025

Bala Abdulkadir Muhammad (Kauran Bauchi) Gwamnan Jihar Bauchi

Shugaban Tinubu ya bayar da umarnin tura ƙarin sojoji da jirage marasa matuka, domin murkushe 'yan ta'adda.Mataimakin Sh...
08/09/2025

Shugaban Tinubu ya bayar da umarnin tura ƙarin sojoji da jirage marasa matuka, domin murkushe 'yan ta'adda.

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ne ya sanar da hakan a wani sakon jajanta wa gwamnati da al'ummar Jihar Borno kan harin da 'yan ta'adda suka kai wa yankin Darajamal da ke Karamar Hukumar Bama, harin, wanda aka kai a daren Juma'a, ya yi sanadiyyar mutuwar fararen hula da sojojin Najeriya.

Shettima Ya kuma bayyana cewa gwamnatin tarayya na duba yiwuwar kafa 'yan sandan jihohi domin tunkarar kalubalen tsaro a matakin farko.

Tuni gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ziyarci yankin da abin ya shafa a ranar Asabar domin jajanta wa iyalan wadanda abin ya shafa.

Mataimakin Shugaban Kasar ya tabbatar wa da al'ummar jihar cewa za su ci gaba da samun goyon bayan gwamnatin tarayya a yakin da jahar ke yi da rashin tsaro.

Gwamnatin Tarayya Ta Yaba wa Ƙasar Finland Kan Hukuncin Daurin Shekaru Shida da Aka Yankewa Simon Ekpa Ɗan Ƙungiyar Biaf...
02/09/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Yaba wa Ƙasar Finland Kan Hukuncin Daurin Shekaru Shida da Aka Yankewa Simon Ekpa Ɗan Ƙungiyar Biafra

Gwamnatin Tarayya ta yi maraba da hukuncin da Kotun Gundumar Päijät-Häme da ke ƙasar Finland ta yanke a ranar Litinin, inda ta ɗaure Simon Ekpa, wanda ya bayyana kansa a matsayin mai rajin Biafra, shekaru shida a gidan yari bisa laifukan ta’addanci.

A cikin wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya fitar a ranar Litinin, ya bayyana cewa hukuncin ya kasance babbar nasara ga Najeriya da kuma al’ummarta da aka dade ana zalunta ta hanyar ayyukan ta’addanci da Ekpa da abokan aikinsa suka haddasa. Ya ce hukuncin na da muhimmanci ƙwarai wajen ƙarfafa dangantakar Najeriya da Finland.

“Shekaru da dama, kiran tayar da tarzoma da shirya tashin hankali da Simon Ekpa ya yi ta hannun ayyukan ta’addancin IPOB sun haddasa bakin ciki da ba za a misalta ba. Iyalan mutane sun tarwatse, kasuwanci ya rushe, yara sun zama marayu, al’ummomi kuwa sun kasance cikin tsoro. An rasa rayuka da dama, wasu kuma sun ji raunuka sakamakon bin wata manufa ta karya da ta yi ƙoƙarin lalata zaman lafiya, haɗin kan ƙasa da ikon mulkin Najeriya,” in ji Ministan.

Ya ƙara da cewa hukuncin da kotun Finland ta yanke ya tabbatar da matsayin Najeriya tun da farko, tare da aika saƙo a fili ga masu tsattsauran ra’ayi a duniya cewa idon duniya na kansu, kuma shari’a za ta cimma duk wanda ya nemi tayar da hankali ta hanyar ta’addanci.

Ministan ya nanata cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na nan daram wajen kare ikon mulkin Najeriya da mutuncin kowane ɗan ƙasa, tare da ci gaba da amfani da dukkan kayan hanyoyin diflomasiyya, soja, shari’a da sauran su – domin kiyaye zaman lafiya, haɗin kai da iyakokin ƙasa.

Haka kuma, gwamnatin ta yi kira ga duk masu bin sawun Simon Ekpa da sauran abokan aikinsa da su ajiye makamai su rungumi zaman lafiya. “Najeriya ƙasa ce mai faɗi da za ta iya ɗaukar kowa, amma babu ci gaba a inda tashin hankali da rarrabuwar kawuna ke faruwa,” in ji Ministan.

A ƙarshe, Gwamnatin Tarayya ta yaba da jajircewa da sadaukarwar Ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Rundunar Sojin Najeriya, hukumomin tsaro da leƙen asiri, Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya da Rundunar ‘Yan Sanda, bisa gudummawarsu wajen tabbatar da tsaron ƙasa duk da ƙalubalen da ake fuskanta.

Gwamnatin Tarayya ta raba kimanin Naira Biliyan 50 ga ƙananan asibitocin Sha-Ka-Tafi a faɗin ƙasar – PateGwamnatin Taray...
21/08/2025

Gwamnatin Tarayya ta raba kimanin Naira Biliyan 50 ga ƙananan asibitocin Sha-Ka-Tafi a faɗin ƙasar – Pate

Gwamnatin Tarayya ta ce ta raba kimanin Naira Biliyan 50 kai tsaye ga cibiyoyin kiwon lafiya na Sha-Ka-Tafi (PHCs) a fadin ƙasar nan ta hanyar Asusun Samar da Kiwon Lafiya na (BHCPF).

Ministan Lafiya Farfesa Muhammad Ali Pate, ne ya bayyana haka a Abuja a ranar Litinin. Ya ce hakan ya samar da ci gaba mai ma’ana wajen inganta tsarin kiwon lafiya a matakin ƙasa.

Farfesa Pate ya kuma ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta kuma saki sama da N20 biliyan don gyara da sabunta cibiyoyin kiwon lafiya 4,362 a jihohin Arewa 19 da Babban Birnin Tarayya (FCT).

Ministan ya kara da cewa, sama da mutane miliyan 37 ne suka je cibiyoyin kiwon lafiya na Sha-ka-tafi a fadin Najeriya a watanni huɗu na farkon shekarar 2025, wanda ke nuna cewa sabbin matakan gwamnatin Tinubu na tasiri wajen tsare-tsaren kiwon lafiya da samar da bayanan kididdigar wadanda aka duba.

Haka kuma, ya ce shirin inshorar lafiya na gwamnati ya samu ci gaba sosai inda ake sa ran shigar da mutane fiye da na shekara ta 2024 da suka kai miliyan 2.4 kafin karshen shekara.

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KUKAN Kurciya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to KUKAN Kurciya:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share