Tijjaniyya News

  • Home
  • Tijjaniyya News

Tijjaniyya News we create this page for the purpose of Awareness , because awareness is the passport to the future ,for tomorrow is belongs to those who prepare for it.

17/08/2025

Allahu akbar " Bayan sun bace cikin Sahara Allah ya kawo musu tallafi.

17/08/2025

Zikiri abincin ruhi.

02/01/2022

فداك أبي وامي ونفسي يا رسول الله 💪😭

صلوات الله وسلامه على سيدنا رسول الله وآبائه وأمهاته وءاله الطاهرين.
02/01/2022

صلوات الله وسلامه على سيدنا رسول الله وآبائه وأمهاته وءاله الطاهرين.

02/01/2022

TSOKACI AKAN MAGANAR JALINGO.

Bansan Meye Ribar Jalo Jalingo cikin wannan Magana da yake ta qoqarin dasa ta a zukatan Mutane ba? 😢 Bansan Wani Irin Baqin zuciya ke ga Jalo Jalingo ba. Bansan Wani Irin Mushen Fahimta Gareshi a addini ba.Burinsa Kullum saka baqinciki a zukatan masoya Annabi SAW. Burinsa yanuna ma mutane Annabin da kuke ta cewa fa toh ba Kowa bane shima yana da Tawaya! 😔
Eh Munji, Mu Qaddara Ma Misali Hadithin Ya Inganta Toh Wllh Duk Hadithin Da yake ta6a Janabin SalLaLlahu AlaiHi WasaLlam Bamu Yarda da wannan Hadithin ba, Hadithai Nawa ne suke Nuni Ga Girma da Martabar Annabi SAW amma Bamuga Jalo ya dage akansu ba.
Hadithin da Jalo yake ta kafa Hujja dashi Na Hammad Ibn Salamah Hadithi ne Guda 1. Wanda Astagfirullah wajen Jan Baqin Hadithin ma yai Kuskuren Lrbci. Sannan MUSLIM shi kawai ya kawo wannan Hadithin, Amma ya Lafta Qarya yace banda Muslim akwai wani Muna Jiran Mlm ya kawo mana wani banda MUSLIM din. Hadithi ne Wanda yake Akwai Wasu Ruwayoyin da s**a kawo shi da Ma'ana me kyau Wanda yafi wancan, Kuma Shi Wanda Ya Ruwaito wancan Hadithin Ma Yana Da Illa... Mlm yayi Bincike akai. Mlm Yayi Mgna akan Cewa Hadithin wai Anyi JIMA'I akai Kuma wannan Zallar Qarya ce, Hadithi Ne Guda 1 shikenan.
Malam yana Fassara wannan Hadithi ne tare da Son Zcyrsa da Qiyayyar sa ga Annabi, Abinda Ke Zcyrsa take Fitowa.
Haramun ne fitowa da abinda zai rarraba kawunan Mutane, Mas'alar da take da Sa6ani amma Mlm Ya Dage sai ya tabbatar da ita.

KIRA GA MALAMAI.
Indai Dagaske Lokacin da aka dinga Mgana akan ABDUlJABBAR har akayi Muqabala dashi akan dgske Kare Annabi SAW ake Toh fa Ga Jalo Jalingo shima....
Indai Kuma wani ya ta6a Sahabi Ko an ta6a wani Malami Ko Shehu Ko An ta6a Sheikh NAsiruddeen-Albany kun fito kunyi Rddi da sunan Kare annabi toh fa ga Jalo Iyayen Wanda ya kawo Musuluncin su yake so ya rushe 😭 Dole ne Kare martabar Annabi SAW.
Ba Yau Jalo Jalingo ya fara wannan abun ba, Shine Wanda Yakira sunan Syydna ALI A.S ya zageshi 😭 Sannan yana ta Bijiro da wannan Mas'alar ba wannan bane Na farko😭
Kuma wllh son Zcyrsa kawai yake.

Sannan wasu hadisan sun kuma zuwa akan wannan siyaki da suke tabbatar da amsuwar Addu'ar ANNABI IBRAHIM (A.S) da kuma tsarkin nasabar ANNABI (S.A.W) har zuwa kan ANNABI ADAMU (A.S).

√ Sayyadina Ibn Abbas (R.A) yace "ALLAH ya tafiyar da zuriyar ANNABI (S.A.W) daga kan wani ANNABIN, zuwa wani ANNABIN, Idan mahaifi na da ƴaƴa guda biyu, to tsatson MANZON ALLAH na fitowane daga wanda yake da gadon ANNABTA. (BUKHARI).

√ Tsatsona shine tsatson mafiya alkairin mutane, kakannina sune mafiya alkairan mutane (Tirmizi).

√ ALLAH ya zabeni a cikin kebantattun jama'ar Larabawa, na fitone daga mafiya alkairin mutane (Tabarani).

GRAGADI: Addini Na Allah ne Hujja ake buqata ba Tarin Shekaru ......

By: Abdulmalik Bin Khamis
31/12/2021.

02/09/2021
23/08/2021

ZUWA GA Dr. JALO JALINGO, AKAN BATUN TAUYE ALFARMAR KHUSUSIYAR MANZANNI.

Duk zantukan da ya fadi a game kalubalantar "Ismar" ANNABAWA ya ciro su ne cikin littafin Majmu'al Fatawa na Sheikh Ahmad Ibnu Taimiyyah duk da yayi kokarin boye hakan.

Kamar zancensa da ya baiwa lamba na biyu cewa.

2. Tabbatacciyar Ismar da Annabawa da Manzanni ke da ita ita ce Isma cikin isar da sakon Allah Madaukakin Sarki kawai.

Sheikh Ibnu Taimiyyah Yace" yace zancen cewa ANNABAWA an kare su daga aikata manyan zunubai (Kaba'irai) amma ba'a katange su daga aikata kananan zunubai ba (Saga'ir), yace hakan shine fahimtar akasarin Malaman Musulunci, na Tafsiri, Hadisi, da kuma Faqihai, babu wani abu da aka ruwaito daga wani magabaci (Salaf) kamar imamai, Sahabbai, ko kuma tabi'ai ko kuma halifofi da dayansu bai amince da wannan fahimta ba (Majmaa’ al-Fataawaa, 4/319).

Sannan zancen Malamin mai lamba na 3 , 4, 6 da 7 suma duk ya fitar dasu ne kamar haka.

3. Sam ba aibi ba ne ga Annabawa da Manzanni su yi mantuwa ko su yi kure cikin wani Ijtihadi da s**a yi.

4. Allah Madaukakin Sarki ba ya tabbatar da Annabawa da Manzanni a kan kure da s**a yi, a’a da sun yi kuren to nan da nan zai gyara musu kuren nasu.

6. Ayoyin Alkur’ani masu yawan gaske ne da suke tabbatar da cewa Manzon Allah mai tsira da amincin Allah yana iya yin mantuwa, kuma yana iya yin kure.

7. Lalle aqidar cewa Manzon Allah mai tsira da amincin Allah ba zai yiwu ba a ce ya yi kure, haka nan ba zai yiwu ba a ce ya yi mantuwa, Aqida ce ta batattun ‘yan bidi’ah. Allah Ya tsare mu. Ameen.

Shima ya ciro su ne a wannan littafi, inda Sheikh Ibnu Taimiyyah yake cewa :

Mafi yawa daga ruwayoyi, daga Ijma'in Malamai sun bayyana cewa ANNABAWA ba ma'asumai bane game da aikata kananan kusakurai, sai dai ba'a basu damar zarcewa a cikin aikatasu, kuma ba su ce hakan bazai taba faruwa ba har abada, bayanan farko shine "su dukkan su ma'asumaine hakan yazo ne daga Rafidawa, wadanda suke cewa dukkan ANNABAWA ma'asumai ne basu taba aikata wani kuskure ko da ta hanyar mantuwane, ko kuma rashin fahimta. (Majmu’ al-Fataawaa, 4/320).

Shehin Malamin ya kara da cewa "Ayar da take bayyana Annabtar ANNABAWA, kuma take bayyana cewa su ma'asumaine cikin sha'anin isar da sako daga ALLAH, to abinda s**a fadi shine kawai yake na gaskiya, wannan shine ma'anar ANNABTA, wanda ke nufin ALLAH na gaya musu wani abu na gaibu su kuma sai su gayawa mutane, kuma shi Manzo akan umarceshi da ya kira mutane zuwa ga ALLAH, kuma ya isar da sakon ubanginjinsa.

(Majmu’ al-Fataawaa, 18/7).

Duk da Shi Dr. Jalo bai kawo ba, amma wasu daga ababen da s**a rika a matsayin hujjarsu ta cewa ANNABAWA na yin kuskure sune:-

An ruwaito daga Raafi' Ibn Khudaij yace "MANZON ALLAH (S.A.W) yazo birnin Madina, su kuma sun kasance suna yiwa dabinai wasu dabaru na samun yabanya, sai yace dasu " me kukeyi haka? Sai s**a bashi amsa da cewa "ko da yaushe s**an yi masa wannan abin, sai yace dasu " amma da zaku daina yin hakan da yafi alkairi, sai s**a dena yi, sai ya zamo sun samu tawaya cikin abinda s**a saba samu, sai s**a sanar dashi abinda ya faru, sai yace dasu " ni kawai mutum ne kamarku, idan nayi muku umarni cikin abinda ya shafi Addini, to ku bi, amma idan na gaya muku wani abu akan sha'anin duniyarku to ku auna ku gani,......!."( Muslim, 2361)

Sannan da wasu daga kissoshi da s**a zo cikin Al-kur'ani kamar .

Ayayin da Kabeel ya kashe Habeel, da lokacin da Mala'iku biyu s**a zo ga ANNABI Dauda ya saurari dayan, amma bai saurari dayan ba, da kissar ANNABI YUNUS (A.S) sadda kifi ya hadiyeshi, da kuma abinda yazo daga Surar Abasa aya ta 1-2. da kuma abinda ya faru na cin itaciyar da ALLAH ya hani ANNABI ADAM(A.S) da ci.

Sai Malamin ya kawo cewa...!

5. Bukhariy ya ruwaito Hadithi na 401, da Muslim na 572 daga Abdullahi Bin Mas’ud Allah Ya kara masa yarda ya ce: Manzon Allah mai tsira da amincin Allah ya ce: انما انا بشر مثلكم انسى كما تنسون فاذا نسيت فذكروني Ma’ana: ((Ni mutum ne irinku ina mantuwa kamar yadda kuke mantuwa, idan na manta ku tunatar da ni)). Bukhariy ya ruwaito hadithi na 6398, da Muslim na 2719 daga Abu Musal Ash’ariy Allah ya kara masa yarda ya ce: Manzon Allah mai tsira da amincin Allah ya kasance yana rokon Allah da wannan addu’a: اللهم اغفرلي خطيئتي Ma’ana: ((Ya Ubangijina Ka gafarta mini kuskurena)). Ahmad ya ruwaito hadithi na 19,925, da Bazzar na 3,525, da Tabaraniy na 242 daga Imran Bin Husain Allah Ya kara masa yarda ya ce: ya kasance daga cikin addu’ar Manzon Allah mai tsira da amincin Allah cewa: اللهم اغفرلي ما اخطات Ma’ana: ((Ya Ubangijina Ka gafarta mini abin da na yi kuren shi)).

WAR-WARA.

1- Idan muka tambayi Mallam, shin wannan abu da yakeson karantarwa, wacce Maslahace cikinta da idan mabiya s**ayi riko da ita zata zame musu silar kyautata makomarsu ta lahira shin wacce amsa zai bamu...?

2- Malamin ya kamata ya sani cewa "Lallai rayuwar ANNABAWA Misaline ga Al'ummar Zamaninsu, sam basu kuskure, sai dai ALLAH ya kaddara musu aikata wani abin da silarsa zai fitar da wata hukunci ga al'umma, ko aikata wani abin da zai zamo silar samun wani sauki ko rahama ga Al'ummarsu, idan kuma suna kuskure sai ya gaya mana hukuncin Kuskurensu a wajen ALLAH.

Domin ALLAH yana fadi a hakkin MANZON ALLAH (S.A.W) Suratu Taubat Aya ta 128

لَقَدْ جَآءَكُمْ رَسُولٌ مِنْ أَنْفُسِكُمْ عَزِيزٌ عَلَيْهِ مَا عَنِتُّمْ حَرِيصٌ عَلَيْكُمْ بِالْمُؤْمِنِينَ رَءُوفٌ رَحِيمٌ

3- Kaddarama ANNABAWAN na yin kuskure, ai kai ba hurumin ka bane tattaunawa akai, domin ko kai mahaifinka na da hurumin bayyana kuskuren mahaifiyarka, amma kai ai baka da hurumin bayyana kuskurenta idan kayi hakan kayi mata rashin kunya da rashin ladabi, haka zalika hurumi ne da ya kadaita da ALLAH shi kadai yayi zance cikin sha'anin MANZONNIN SA dashi, ba dan hakan ya zamo abin tattaunawa tsakanin mutane ba, sai dan mu fahimci wata hikim dake cikin hakan.

4 Ya kamata Malamin ya fahimci hadisan da ANNABI (S.A.W) yake zance a babi na Zuhudu, Da Tawadi'u, kamar fadinsa

-KADA KU GIRMAMANI SAMA DA YUNUSA BIN MATTA, KO ISA DAN MARYAMA DA SAURANSU, SUNE MISALIN HADISAN DA YA KAWO GAME DA KUSKURE KO MANTUWA DA YAKE NASABTAWA ANNABI (S.A.W) amma hakan sam baya nufin cewa "SHI BA ABIN GIRMAMAWA BANE SAMA DA SU DOMIN SHINE YACE SHINE SHUGABAN DUKAN 'YA'YAN ADAMU BA ALFAHARI BA" ". Amma me Malamin zaice akan wasu hadisan kuma da ANNABI (S.A.W) da kansa yake cewa "SHI BA MUTUM BANE KAMAR SAURAN MUTANE" ka duba hadisi na 182 a kitabus siyam cikin Sahihul Bukhari.

Sannan da Malamin ya lura, zai gane cewa ANNABI (S.A.W) ya wuce mukamin da duk yake zato, domin shi akansa ALLAH bai aje mizanin dai-dai da kuskure ba, duk abinda ya aikata dai-dai ne, ba mamaki shi yasa ayoyi kamar haka s**a sauka cikin fadin ALLAH.

Kamar fadinsa a sura ta 3 aya na 31

قُلْ إِن كُنتُمْ تُحِبُّونَ ٱللَّهَ فَٱتَّبِعُونِى يُحْبِبْكُمُ ٱللَّهُ وَيَغْفِرْ لَكُمْ ذُنُوبَكُمْ وَٱللَّهُ غَفُورٌ رَّحِيمٌ

Da kuma fadinsa a Surata ta 4 aya na 80

مَّن يُطِعِ ٱلرَّسُولَ فَقَدْ أَطَاعَ ٱللَّهَ وَمَن تَوَلَّىٰ فَمَآ أَرْسَلْنَـٰكَ عَلَيْهِمْ حَفِيظًا

Lallai ya kamata Malamin yaje yayi Tafaqquri akan wadannan ayoyi, anan zai gane cewa "BIN ANNABI (S.A.W) CIKIN DUK ABINDA YA TA'ALLAKA DASHI, SHINE HAKIKAR BIN ALLAH" TO TAYAYA YAKE TUNANIN ANNABI (S.A.W) ZAI KUSKURE CIKIN ABINDA YA SHAFI RAYUWA, ALHALI BABU WANI ILMI DA ALLAH BAI BASHI SHI BA".

ME YASA KAFIRAN MAKKAH SUKE KIRANSHI DA SUNA AL'AMIN TUN KAFIN A AIKO SHI DA RISALA A ZAHIRI, HALA MU'AMALAR DA YAYI DASU ABUNE DA YA SHAFI WAHAYI, KO KUMA ABUNE DA YA SHAFI RAYUWA...?

Mai yiwuwa manufar Malamin so yake ya yaki wata daraja Khususiyya da ALLAH ya kebenceta ga ANNABI (S.A.W) wanda hakan kuma dama sanannen al'amarine game da Malamin da ya fito da zantukanshi daga gareshi.

ALLAH YA SHIRYA.

ALHAMDULILLAH.

KO YAUSHE ZA'A DENA YIWA JUNA KALLON 6 DA 9 TSAKANIN SASHEN MUSULMI ZUWA SASHE, KOWA YA FUSKANCI ABINDA KE GABANSHI...? ...
01/07/2021

KO YAUSHE ZA'A DENA YIWA JUNA KALLON 6 DA 9 TSAKANIN SASHEN MUSULMI ZUWA SASHE, KOWA YA FUSKANCI ABINDA KE GABANSHI...?

Idan kace dasu : Dan ALLAH abar rarrabuwar nan, azo a fuskanci masalaha da abinda zai kawo hadin kai, sai s**e dakai "Idan anason a hada kai dasu to dole sai an watsar da komai an koma kan karantarwar Kitab wa Sunnah, da fahimtar Sahabbai idan kuwa ba haka ba, to babu ranar da zamu hada kai da yan Bidi'ah, Mushrikai".

TO MUNJI.

Amma kusani, Yadda muke da Shehu Tijjani (R.T.A), Sheikh Ibrahim Inyass (R.T.A) muke bin fahimtarsu cikin abinda yazo a kitab wa sunnah da zantukan Sahabbai da Ijtihadinsu, haka kuke da Sheikh Ahmadu Ibnu Taimiyyah, Sheikh Ibnu Abdul-wahab, da Sheikh Nasirudden Albani kuma kuke bin karantarwarsu cikin abinda s**a fahimta a Kitab wa Sunnah, da kuma karantarwar Sahabbai da kuma Ijtihadin da s**ayi".

To menene ya bambantamu daku, tunda dai dukkanmu muna da wasu jagorori da muke adreshi dasu, kafin a riski Kitabu da Sunnah da kuma fahimtar Sahabban?

--> Duk wani abin laifi da zaku nuna a tattare damu, domin ku aibatamu dashi, to idan aka wai-waici naku aibin sai aga yafi namu da kuke kokarin muzantamu dashi .

--> Duk abinda kuke ganin aikatashi kamar kuskurene, a fahintarku, to haka zalika muna muna da tarin ababe da muke ganin aikatasu kuskurene a tattare daku, wadanda wasu muninsu a tamu fahintar na iya jawo matsala ga makomar wanda ya rayu yana aikatasu.

KU SANI.

Yadda kuke ganin kima da muhimmancin wadannan Maluma naku da kuka rika a matsayin jagorori, kuma baku sanya ranar da zaku sake su ba, to fiye da haka mu ma muke ganin kima, daraja da kuma muhimmancin namu Jagorororin, kuma mu ko tunani bamayi da wai zamu riski wani lokaci da zamu sakesu.

Yadda kuke ganin kuna kan wata ganuwa ta shiriya, da kuke ganin zaku rabauta ranar lahira dalilin riko da ita, to fiye da ku muke da yakini da nutsuwar zuciya akan tafarkin da muke kai.

Tunda mu da ku, duk yadda zaku jefemu da kalmomin bata, baku da hurumin ku iya shiryar damu zuwa ga abinda kuke ganin shine dai-dai, muma haka, to me zai hana mu da ku, kowa ya fuskanci abinda ya fissheshi, a guji kafirta juna, zagin juna, aibata juna, tare da jifan juna da kalmomin bata ko hakan zaisa Musulmi su samu zaman lafiya tare da gushewar fitintunu a tsakaninsu.

ALLAH YA NUNA MANA RANAR DA AL'UMMAR MUSULMI, ZASU RISKI WANI LOKACI DA ZA'A SAMU FAHIMTAR JUNA KOWA YA FUSKANCI ABINDA YAKE GABANSA.

ALHAMDULILLAH.

Tofa  Sibawaihi yasha wuya a waqan nan Daya daga ciki akwai inda yake cewa " YA HAMILUL ZULUMATI " maimakon " YA HAMILAL...
30/06/2021

Tofa Sibawaihi yasha wuya a waqan nan
Daya daga ciki akwai inda yake cewa

" YA HAMILUL ZULUMATI " maimakon
" YA HAMILAL ZULUMATI"
To wanda bai iya larabci ba ya za'ayi yayi waƙa . Shima wanda akai ma wakan ba iya larabci yayi ba .
ضعف الطالب و المطلوب

27/06/2021

HAKANAN GUGUWAR SAUYI ZA TA CI GABA YAYE KURAR KARYA TANA BAYYANA GASKIYA DA IZININ ALLAH..

Bayan ta tabbata cewa :Manyansu da Yaransu sun gaza tabbatar da waye Malamin Albani a ilmin hadisi,, banda abinda aka sansu dashi na musu da karfin jayayya babu hujja, kame-kame, zagi da gugar zana da kin sallamawa gaskiyar da ta mamaye su, gujewa sake tunkarar zama domin aci gaba da tattaunawa kamar yadda aka alkawarta, karshe dai sun fito da wani al'amari na borin kunya wanda lallai ya sanyani yin dariya a bisa ka'ida 🤣😀😂😀🤣.

Saboda batar basira irin na "Asadu Suna" tayaya zai fito Duniya, domin wawuntar da tunanin mutane akan bashin da ake binsu akan wancan Maudu'i na waye Malamain Albani a ilmin haidis, sai yace "SHEIKH IBRAHIM INYASS (R.T.A) BAI DA DALIBI KO GUDA DAYA" 🤣😀😂😀😂.

Babu shakka da a kasuwa ko tashar mota naji wani yana fadin irin wannan magana, to ko waigawa bazanyi ba na kalli wajen da yake ba, domin abinda zai zo tunanina shine: wannan zance da ya fito daga bakin Mahaukaci ko kuma wani mashahurin jahili makaryaci. Amma na cika da mammaki yadda wai ace mutum mai hankali harma da yake da'awar Malumta ya tara mutane masu hankali ya gaya musu wannan zance har cikinsu wani ma ya bashi lokacin da zai saurare shi, alhali zahiri da badinin waki'a na karyata duk wata kalma da zai furta akan wannan al'amari.

Abar maganar Tijjanawa, ko bakaken fatar Africa, ai idan ma'anar zamowa dalibta na nufin :- bayar da wani ilmi ga wasu akan wani al'amari su kuma su dauka suyi aiki dashi, to a wannan ma'anar za'a riski cewa "Jiga-jigan Malaman ku na Wahabiya na Saudiya da s**ai zamani da Maulanmu Sheikh Ibrahin Inyass (R.T.A) duk sun kasance dalibansa, a siffa da ma'ana, domin sun amfana da tarin ilminsa ta fuksoki mabambanta da idan muka samu lokaci zamu zayyanosu daya bayan daya.

Mudai kam, babu abinda zamucewa ALLAH sai godiya, domin ta tabbata duk abinda Sufaye s**a kore babu wani guda da ya isa ya tabbatar dashi cikin Wahabiya, sannan duk abinda aka tabbatar to ya girmi korewarsu, ayayin da su kuma ALLAH ya jarabcesu da akasin hakan.

Madallah da hazikan Mazajen Faidha Tijjaniyya, masu rarrabewa tsakanin tsaki da tsakuwa, wadanda s**a kusa kawo karshen cuwa-cuwa da ha'inci ta hanyar fakewa da "SUNNAH" da Wahabiyawa keyi tsawon zamani.

ALLAH MUNGODE MAKA, ZAHIRI DA BADININ MU, KA KARA TABBATAR DAMU AKAN GASKIYARMU, KA TSARE MU BIYEWA TAFARKIN YAN KAME-KAME DA SUNAN "SUNNAH" KABARMU AKAN TACECCIYAR SUNNAH TA MANZON ALLAH (S.A.W).WACCE MUKA SAMU MAGABATAN MU AKAI.

ALHAMDULILLAH.

26/06/2021

KUNDAI JI SON ZUCIYAR TA SOMA BAYYANA.

Sufa yan hakikar bogi, duk iya shegen da sukeyi, bazaka taba ji sun kawo wata hujja cikin wani littafi daga cikin litattafan Sufaye ba, hasali ma su a wajen su yin karatu alamace ta hijabi.

Kuma karara, Sheikh Ibrahim Inyass (R.T.A) ya barrantar da kansa, daga su a cikin wasikarsa ta Jawahirul Risala.

Amma tsabar rashin tsoron ALLAH, da son zuciya, hakanan wadannan Maluman Kungiya da wancenansu suke shiga cikin littafin diwani, da wasu litattafai na Shehu, su dauko wasu zantuka da s**a jahilta, suyi musu fassarar bugun kato a sarrafasu zuwa ga wata ma'ana da ake son fitarwa ta batanci, izgilanci ace hakan Shehu yake nufi, kuma ace hakan 'Yan Hakikar bogin s**a nakalto daga gare shi, duk domin a ribaci tunanin jahilai, alhali idan kaje gaban Malamai masana na gaskiya, zaka samu zancen bai kunshe da komai ba sai zunzurutun falsafa da hikima cikin isar da sakon da zai shiryar zuwa ganin girman zatin ALLAH da buwayarsa.

Amma su gashi, basu yarda cewa hujjojin da yan ta'adda ke kafa hujja dasu cikin litattafan Malaman su haka abin yake ba, hasalima har sun dai-daita matsayin Kur'ani da Litattafan Malaman su, duk da yake dukkan Kungiyoyin ta'addancin Duniya mashayarsu sune dai wadannan Maluma nasu, kuma dan batar basira bai lura da cewa "Meyasa basu fitar da zantukan ta'addancin cikin litattatan Malaman Mazahibu, ko kuma litattafan Sufaye ba".

Gaskiya sha'anin Yan Bidi'a masu lasisi akwai rainin wayo cikinsa, Amma babban fatarmu ALLAH dai ya ganar dasu.

Duk da kankantar shekarunmu, ba kasafai za'a iya yaudararmu ba ko kuma a yaki tunanin mu akan abinda yake na karya.

ALHAMDULILLAH.

25/06/2021

ZUWA GA "DAN BIDI'A MASU LASISI".

Bayan karanta rubutun wannan Malami, sai na cika da mamaki, yadda kuru-kure yake so ya juyar da gaskiyar da Duniya ta san dashi, zuwa karya, tsammanin shi yadda mabiyansa ke bin shi a makance, haka kowa ma yake, yadda mabiyansa tunaninsu, hangensu da kuma bincikensu yake a tauye, a kule haka na kowa ma yake.

Idan muka dubi wadannan bayanai nasa ta fuskar d yayi su, sannan kuma muka dubi wasu waki'oi da s**a wakana a Duniya, to lallai ne Mallam zai kasance mai jin kunya ga ababen da ya fadi cikin wadannan zantuka nasa, kuma masu yantacciyar tunani daga mabiyansa zasu fahimci kurensa.

Ga tambayoyi kamar haka, da mukeson Malamin ya taya mu nemo amsoshinsu..

1- SHIN AKWAI WANI MALAMI CIKIN MANYAN MALAMAN SALAFIYYA DA YA TAFI AKAN FAHIMTA SABANIN NA MALAMIN..?

A ranar 15 ga watan Agusta na shekar alif 2014, Babban Malamin Salafiyya, kuma tsohon baban limamin Masallacin Harami, kuma bakar fata ba farko da ya soma limanci a harami, ya fadi a tattaunawarsa da wata kafar yada labaro cewa "DUK ABABEN DA KUNGIYOYIN TA'ADDANCIN DUNIYA KEYI, NA CIKIN LITATTAFAN SU (NA WAHABIYYA/SALAFIYYA) DA SU SHEIKH IBNU TAIMIYA S**A WALLAFA.

2- SHIN AKWAI KASASHEN DA S**A HARAMTA AMFANI DA LITATTAFAN WAHABIYANCI DA SUKE KUNSHE DA KOYARWAR TA'ADDANCI..?

Akwai dimbin kasashen Musulunci da s**a haramta amfani da litattafan su Sheikh Ibnu Taimiyah, domin dakile ta'addanci a kasashen su, kasashen sun hada da :-

• Malaysia.
• Tunisia.
• Egypt.
• Jordan.
• Tajikistan
• Chechenia
• Bosnia
• Pakistan
• Da Sauransu.

Litattafan Malaman da suke dakatar su

√ Sheikh Muhammad Ibn Abdul Wahhab
√ Imam Ibn Taymiyyah
√ Sheikh Ibn Baz
√ Sheikh Ibn Uthaymeen
√ Sheikh Abu Ishaq al-Huweini
√ Sheikh Mohamed Hussein Yacoub
√ Sheikh Mohammed Hassan

Sunayen wasu daga litattafan:-

• Sharhu Fazli-l-Islam na littafin Shaikhi-l-Islam Mohammad bin Abdulwahhab at-Tamin wanda Saleh bin Abdul-Aziz bin Mohammad Al ash-Sheikh yayi.,

• Sharhu Lam’atul-Itiqadal-Hadi ila Sabili-r-Rashad na Imam Muwaffaqaddin ibn Qaddoma al-Maqdisi wanda Sheikh Muhammad bin Shalih bin Muhammad bin Utsaimin yayi.

• Fawaqirul-Izab fi Mu’taqad ash-Sheikh Muhammad bin Abdulwahhab na Mohammad bin Nasir bin Osman Mumir

• Al Juhudu-l-Hadisiya na Abdul-Aziz ibn Baz,

• Al-Ilokatu Bainat-Tashayuu wa Tasawwufuf na Falah ibn Ismail al Mandakar,

• Sharhu Muqaddima fi Usulit-Tafsir li Ibn Taymiya na Musaid bin Sulayman ibn Nasir at-Tayar,

• Al Aliu-l-Bahiyati fi Sharhi-l-Aqidatil-Wasitaya na Ibn Taymiya daga Saleh bin Abdul-Azizi bin Mohammad bin Ibrahim Al ash-Sheikh,

• Al-Majmuatu-l-Oliya na Ibn Taymiya,

• Kitabul-Iman by Abu Ubaid al-Qasim ibn Salam,

• Fazlu Ilmi-s-Salaf ala Ilmi-Khalaf na Abdul Qasim Abdul Azim,

• Fawaidu minat-Tafsir na Abdul Aziz bin Abdullah bin Baz,

• Taysirul-Ilah na Ubaid bin Abdullah bin Suleyman al-Jabiri,

• Al-Usulu min Ilmil-Usul Risala Mukhtasara fi Usuli-lFiqh na Muhammad bin Shalih bin Muhammad bin Usaimin.

3- SHIN BAYANA MALAMIN ZASU SAMU MUHALLI GA JAGORORIN KASAR DA S**A DAUKI NAUYIN YADUWAR TA'ADDANCI A KASASHEN DUNIYA..?

Jaridun Arab News, Times, Arab Gazette, da sauransu, a ranar 5, ga watan Afrilu ta shekarar alif 2018 yayi jawabin da misalin karfe 7:40 AM. Sun kawo jawabin Yarima Mai Jiran Gado na Saudiya, wato Muhammad Bin Salman, yayi zantuka masu tsayi, inda a ciki yake cewa "YANZU LOKACI YAYI DA KASARSU ZATA DAWO DAGA GOYON BAYA DA DAUKAR NAUYIN KUNGIYOYIN TA'ADDANCIN DUNIYA" abin tambayar shine shin da litattafan wadanne Maluma s**ai amfani, domin yada ta'addancin.

Bazanyi dogon bayani ba, duk wanda ya karanta rubutun wannan Malami, kuma yayi bitar wadannan waki'oi da suke karyatashi, zai samu cewa sam-sam zantukansa bazasu samu muhallin zama wajen mutane masu hankali da hangen nesa ba.

Kawai dai abin tambayar shine, shin me yasa su kungiyoyin ta'addancin, basu dauko litattafan Maluman Mazhaba, ko Malaman Sufaye ba wajen kafa hujjojin su na ta'addancin da sukeyi, dole sai litattafan Malamansu na Wahabiyawa da Salafawa..?

MUNA ROKON ALLAH, YA GANAR DA WANNAN MALAMI, DA MABIYANSA DA YAKE RUDARWA.

ALHAMDULILLAH.

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tijjaniyya News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share