ArewaFirm Tv Kamfanin Shirye _Shiryen Sanao'i Da Ala'adun Mu A Yau Na Arewacin Nigeria
(3)

30/05/2026

Yadda China Ke Cin Gajiyar Arzikin Afirka – Gaskiyar da Ba Kowa Ke Faɗa Ba!

30/05/2026

Daga Talakan Yaro Zuwa Dan Takarar PDP a Gombe – Labari Mai Ban Mamaki!

Professor Isa Ali Pantami

30/05/2026

Daga Talakan Yaro Zuwa Dan Takarar PDP a Gombe – Labari Mai Ban Mamaki!

Professor Isa Ali Pantami Abba Sani Pantami Ali Nuhu Mohammed AUDU BULAMA BUKARTI

Duk da kuɗaɗen da gwamnatin Ahmad Aliyu ta samu cikin shekara 3, jama’a ba su ga canji mai kyau ba - Ɗan takarar gwamna ...
29/05/2026

Duk da kuɗaɗen da gwamnatin Ahmad Aliyu ta samu cikin shekara 3, jama’a ba su ga canji mai kyau ba - Ɗan takarar gwamna na ADC a Sokoto

Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar ADC a jihar Sakkwato, Manir Muhammad Dan’Iya, ya ce duk da dimbin kuɗaɗen da gwamnatin jihar da ƙananan hukumomi s**a samu cikin shekaru uku da s**a gabata, har yanzu al’ummar jihar ba su ga ci gaban da ya dace ba.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaransa, Aminu Abdullahi ya fitar, Dan’Iya ya ce ya kamata a auna nasarar gwamnati da tasirin da take yi ga rayuwar jama’a, ba da jawabai ko tallata manufofi kawai ba.

Ɗan takarar gwamnan ya yi zargin cewa matsalolin tsaro da ƙarancin ruwa da tabarbarewar ilimi da lafiya na ci gaba da addabar al’ummar jihar duk da albarkatun da gwamnati ke samu.

Ya kuma yi s**a ga tsare-tsaren gwamnatin jihar guda 9, yana mai cewa mazauna jihar da dama har yanzu ba su ga sakamakon da ya dace daga manufofin ba.

Abdulsalam Gwarzo Ko Abba; Wa Kanawa Za Wu Zaɓa A Matsayin Gwamnan Kano A Zaɓen 2027?
29/05/2026

Abdulsalam Gwarzo Ko Abba; Wa Kanawa Za Wu Zaɓa A Matsayin Gwamnan Kano A Zaɓen 2027?

Kwankwaso na shirin ayyana Aminu Abdussalam a matsayin ɗan takarar gwamna na NDC a KanoRahotanni daga majiyoyi masu tush...
28/05/2026

Kwankwaso na shirin ayyana Aminu Abdussalam a matsayin ɗan takarar gwamna na NDC a Kano

Rahotanni daga majiyoyi masu tushe sun bayyana cewa jagoran Ɗariƙar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, na shirin bayyana tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Comrade Aminu Abdussalam, a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar NDC a jihar Kano.

A tuna cewa Abdussalam ya yi murabus daga mukaminsa na mataimakin gwamna a watan Maris, makonni kaɗan bayan Majalisar Dokokin Jihar Kano ta aika masa da takardar tsige shi daga mukamin.

Majiyoyi sun shaida wa DAILY NIGERIAN cewa an cimma wannan matsaya ne bayan tattaunawa ta sirri da aka gudanar a tsakanin jiga-jigan tafiyar Kwankwasiyya da abokan siyasa na kusa da Kwankwaso.

Tun da fari dai tsohon ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaɓen 2023, Nasiru Yusuf Gawuna, na daga cikin waɗanda ake ganin su ne na gaba-gaba wajen samun tikitin takarar gwamnan.

Sai dai rahotanni sun ce daga ƙarshe Kwankwaso ya amince da Abdussalam a matsayin wanda zai baiwa takarar.

Rahotannin sun ƙara da cewa Kwankwaso ya yi wa Gawuna tayin kujerar mataimakin gwamna ko kuma tikitin takarar Sanatan Kano ta Tsakiya, amma ana ganin Gawuna ya ƙi amincewa da tayin tare da jaddada biyayya da ci gaba da aiki domin nasarar jam’iyyar.

Majiyoyi sun ce Gawuna ya shaida wa Kwankwaso cewa ya shiga tafiyar Kwankwasiyya ne ba tare da wani sharadi ba, saboda haka rashin samun tikitin gwamna ba zai sa ya fice daga tafiyar ba.

An kuma rawaito cewa ƙin amincewar Gawuna da tayin ne ya jinkirta sanar da Aminu Abdussalam a hukumance, yayin da wasu masu ruwa da tsaki ke matsa lamba kan a sake duba cancantar Gawuna saboda ƙarfin siyasarsa.

Wasu daga cikin masu goyon bayan Gawuna sun bayyana cewa ya kamata ɗan takarar da zai fafata da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya fito daga Kano ta Tsakiya, kasancewar yankin ne ke da mafi yawan ƙuri’u a jihar.

Sai dai masu goyon bayan Aminu Abdussalam suna ganin tsohon mataimakin gwamnan ya nuna cikakkiyar biyayya, jajircewa da sadaukarwa wajen bunƙasa tafiyar Kwankwasiyya.

DA DUMI-DUMI: Atiku Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Jam’iyyar ADC Atiku Abubakar ya lallasa Rotimi Amaechi da Mohammed Hay...
27/05/2026

DA DUMI-DUMI: Atiku Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Jam’iyyar ADC

Atiku Abubakar ya lallasa Rotimi Amaechi da Mohammed Hayatudeen wajen samun tikitin takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC.

Sakamakon zaɓen ya nuna cewa Atiku ya samu ƙuri’u 1,855,787 inda ya zama wanda ya lashe zaɓen fidda gwani na jam’iyyar.

Amaechi ya zo na biyu da ƙuri’u 509,397, yayin da Hayatudeen ya samu ƙuri’u 180,903.

Jimillar ƙuri’un da aka kaɗa a zaɓen sun kai 2,546,457, yayin da jimillar mambobin jam’iyyar da s**a cancanci zaɓe s**a kai 3,113,599.

Shin ya kuka ga wannan lamarin...?

“Idan kaga wannan dressing ɗin ka san AREWA ce 😍✨Yan Niger 🇳🇪  inanan zuwa kasar ku domun kawo ziyara insha Allah. Wane ...
27/05/2026

“Idan kaga wannan dressing ɗin ka san AREWA ce 😍✨

Yan Niger 🇳🇪 inanan zuwa kasar ku domun kawo ziyara insha Allah.

Wane fata kikemun?

27/05/2026

Ina yima yan niger 🇳🇪 da masoyana barka da sallah.

Adresse

Gombe

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque ArewaFirm Tv publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Partager