Nigerian News Hausa

Nigerian News Hausa Nigerian New's Hausa, Jarida Ce Nagartacciyya Mai Ɗauke Da Nagartattun Labarai Cikin Harshen Hausa.
(1)

WANNAN SHI NE ASALIN TAIMAKO!!!Ko kun tina labarin yaron nan? A shekarar 2018 wani bidiyonsa ya yaɗu a Facebook, lokacin...
08/07/2025

WANNAN SHI NE ASALIN TAIMAKO!!!

Ko kun tina labarin yaron nan? A shekarar 2018 wani bidiyonsa ya yaɗu a Facebook, lokacin yana Almajiri (ku duba comment section don ganin bidiyon), ga cuta a jikinsa, ga duka daga malaminsa da sauransu, ga bara, mutane da yawa sun yaɗa bidiyonsa don jimami da tausaya masa, wasu har kuka sun yi lokacin.
Ita kuwa Hajiya Laylah Ali Othman ba ta tsaya jimami ba, kawai ta sa aka nemo mata shi, ta je har gurin iyayensa ta nemi izininsu, ta dauke shi a matsayin ɗanta, ta ɗauki ɗawainiyar rayuwarsa.
Yau ku dube shi yadda ya zamo mutum, kyawunsa ya bayyana, ya yi fresh abinsa.
Ba shi kaɗai ta yiwa haka ba, akwai sauran ma.
Allah Ya saka mata da alkhairi, Ya sa wannan aikin ya yi sanadin shigarta Aljanna.

AKWAI BIDIYON WANCAN LOKACIN A COMMENT.

Abu Albani

08/07/2025

An nemi yan Najeriya da su tashi da Azumi gobe don nemawa tsohon shugaban kasa Buhari lafiya

Yau Shekaru 14 da kotun koli ta sake tabbatar wa yar wasan hausa (Kannywood) Rabi Isma'il (Rabi Acid) hukuncin kisa.A ra...
08/07/2025

Yau Shekaru 14 da kotun koli ta sake tabbatar wa yar wasan hausa (Kannywood) Rabi Isma'il (Rabi Acid) hukuncin kisa.

A ranar 8 Ga Watan Yuli 2011, kotun koli ta tabbatarwa jarumar Kannywood hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Rabi Isma'il (wacce ake yiwa lakabi da Rabi Acid) yar Asalin Jihar Edo ce, amma haifaffiyar Tudun Wada a Kano ce, ta fito a fina-finan Kannywood wanda su ka hada da Tsumagiya, da Aya, da Manakisa. A ranar Kirsimetin shekarar 2002, Rabi ta tunkuda saurayinta Alhaji Ibrahim Zazu cikin ruwan Tiga, in da rai yayi halinsa. Amma kafin ta tunkudashi shi cikin ruwan, sai da ta ba shi alewa cakuletin Ekiles wacce tayiwa cushe da maganin bacci. Sai da Rabi ta tabbatar ya fita a hayyacinsa sannan ta lalube aljihunsa ta kwashe kudi naira dubu dari, kana ta tunkudashi cikin ruwan.

Wannan dama dai ya nuna da niyar kisa ta tura Auwalu Zazu cikin ruwan. Jami'an binkice sun gano rabi ta aikata hakane domin ta gaje dukiyarsa. Kasancewarsa hamshakin maikudi.

Don haka a ranar 5 ga Junairun shekarar 2005 babbar kotun jihar Kano ta sami Rabi Acid mai lambar fursuna k/22c da laifin kisan kai. Mai shari'a Halliru Muhammad Abdullahi ya yanke mata hukuncin kisa ta hanyar rataya, sai dai Rabi ta daukaka kara a kotun daukaka kara da ke Kaduna. A nanma dai kotun ta sake tabbatar wa da Rabi laifinta. Daga nan kuma sai ta sake daukaka kara zuwa kotun koli da ke Abuja. In da a rana mai k**ar ta yau 8 ga watan Yuli 2011 kotun koli ta tabbatar mata hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Alkalan kotun guda bakwai karkashin mai shari'a Francis fiddodi Tabai, sunce sun gamsu da hujjujin da aka bayar a kotun farko, don haka su ka sake tabbatar mata da hukuncin Kksa ta hanyar rataya. Sai dai k**ar a Fim! A ranar 16 ga watan disambar 2011, sai Rabi Isma'il tayi batan dabo daga gidan yarin Hadejia, in da aka neme ta kasa ko sama aka rasa.

Bayanai sunce a kurkukun Kano aka fara daureta kafin daga baya a mayar da kurkukun Kaduna lokacin da ta daukaka kara. In da a can ne Rabi Isma'il ta zama Jar wuya, in da ta rika safarar sigari da kwaya da Wiwi. Har ma anyi zargin Rabi tana sheke ayar ta ne da manyan jami'an gidan yarin a lokacin da ta ke a tsare.

Bayan da kotun koli ta yanke mata hukuncin kisa sai a ka sauya mata matsuguni zuwa gidan kurkukun Hadejia. A Hadejian ne ta yaudari wani babban Ganduroba, su ka tsunduma cikin kogin soyayya. Ana wannan halin ne ta ke shaida masa cewa ta mallaki Miliyoyin Naira, kuma da zai nema mata bizar Amurka ya fitar da ita daga kurkuku za ta aure shi," su ta re a can suyi ta cin duniyarsu da tsinke. Haka kuwa a kai a ranar 16 ga watan Disambar 2011, sai jami'in nan yayi hanyar da Rabi ta bi ta sulale daga kurkukun.

Sai dai a ranar 21 ga watan mayun 2017, jami'an tsaron DSS Su ka cafke Rabi Isma'il a kan iyakar Najeriya da Jamhuriyyar Benin.
A cewar mai magana da yawun hukumar gidan yarin, Francis Enobore, jami’an leken asiri na hukumar kula da gidajen yari ta Najeriya ne s**a sake k**a Ismail tare da goyon bayan jami’an tsaro na DSS.

Daga nan su ka mika ta ga hukumar kula da gidajen Kurkuku ta kasa, a in da su ka sa ma mata gurbi a gidan kurkukun Kuje da ke Abuja. Shi kuma Ganduroban da ya taimaka mata ta tsere, an rage masa mukami tare da sauya masa wajen aiki. Hakan dai bai wa abokan aikinsa sa yawa dadi ba! Kasancewar laifinsa ya cancanci kora da gurfana a gaban Kotu.

Izuwa yanzu dai ba ni da labarin wani hali Rabi Isma'il (Rabi Acid) ta ke ciki.

Muhammad Cisse

Lauyoyi 500 Sun Mamaye Fadar Shugaban Kasa, Majalisar Tarayya da Takardar Korafi Kan Zargin cin Hanci da Rashawa ga Shug...
07/07/2025

Lauyoyi 500 Sun Mamaye Fadar Shugaban Kasa, Majalisar Tarayya da Takardar Korafi Kan Zargin cin Hanci da Rashawa ga Shugaban NMDPRA

Don Bukatar a kori Ahmed Farouq nan take

YANZU- YANZU: Na fita daga APC sabida zalunci da Rashin adalci da Jam'iyar take Yiwa talakan Nigeria.--- Babachir Lawal,...
07/07/2025

YANZU- YANZU: Na fita daga APC sabida zalunci da Rashin adalci da Jam'iyar take Yiwa talakan Nigeria.--- Babachir Lawal, tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF) a mulkin Buhari.

Usman Ibrahim Kobie

Wata Sabuwa: Kwankwaso ba zai yi takarar shugabancin Nijeriya a jam'iyyarmu a zaben 2027 ba - NNPP
06/07/2025

Wata Sabuwa: Kwankwaso ba zai yi takarar shugabancin Nijeriya a jam'iyyarmu a zaben 2027 ba - NNPP

Tsohon Shugaban Sojoji a Nijeriya, Laftanal Janar Ihejirika, ya ce duba da halin taɓarɓarewar tsaro da Najeriya ke fuska...
06/07/2025

Tsohon Shugaban Sojoji a Nijeriya, Laftanal Janar Ihejirika, ya ce duba da halin taɓarɓarewar tsaro da Najeriya ke fuskanta, ya k**ata a tilasta wa ’yan ƙasar samun horon soja kuma yana da kyau a fara daga kan matasa masu yi wa ƙasa hidima wato NYSC.

Innalillahi Wa Inna ilaihi Raj'un.Allah ya yiwa Abdullahi Shehu Gano (Mai Qasidar Saba'a) rasuwa, bayan ya yi accident a...
06/07/2025

Innalillahi Wa Inna ilaihi Raj'un.

Allah ya yiwa Abdullahi Shehu Gano (Mai Qasidar Saba'a) rasuwa, bayan ya yi accident a satin da ya wuce.

Muna addu'ar Allah ya gafarta masa yasa aljanna makomarsa ya sada shi da Shugaba Sallallahu Alaihi Wasallama.

~Bashir Dandago

MARIGAYI SHEIKH DR IDRIS ABDUL-AZIZ BAUCHI YA BAR BAYA DA DUNBIN ALHERIWasu daga cikin 'ya'yan Marigayi Sheikh Dr Idris ...
03/07/2025

MARIGAYI SHEIKH DR IDRIS ABDUL-AZIZ BAUCHI YA BAR BAYA DA DUNBIN ALHERI

Wasu daga cikin 'ya'yan Marigayi Sheikh Dr Idris Abdul-Aziz Bauchi (Limamin jaddada Tauhidi na Afirka) guda biyar sun kammala karatun jami'ah a Kasar India

Malam Idris ya tura 'ya'yansa maza da mata Kasar India domin su yi ilimi a fannoni na kiwon lafiyar mutane su dawo su cike wa al'ummar Musulmi gurbi

Malam Idris ya gina Asibiti da kudin aljihunsa, ya kawo tsarin da mace Likita zata duba 'yar uwarta mace, a lokacin da ya gina asibitin ya nemi mace Likita tazo tayi aiki zai ninka mata albashi ya rasa, shine ya tura 'yar cikinsa taje tayi karatun

Malam yau baya raye Allah Ya cika masa burinsa, ku duba fannoni na ilimin kiwon lafiya masu tsada da yaransa s**a karanta a India, kuma sun kammala da sak**ako mai kyau, gasu k**ar haka:
👇
(1) Abdullahi Idris Abdul-Aziz ya karanta Physiotherapy

(2) Abdul-Aziz Idris Abdul-Aziz ya karanta Doctor of Pharmacy

(3) Muhammad Idris Abdul-Aziz ya karanta Medical Laboratory Technology

(4) Khadijah Idris Abdul-Aziz ta karanta Nursing

(5) Fatima Idris Abdul-Aziz ta karanta Radiology Imaging Technology

Idan ban manta ba akwai wanda ya kammala karatun MBBS, kunga asibiti guda ya hadu da Likitoci

Marigayi Malam Idris Abdul-Aziz rayuwarsa ta yi albarka, ya cike wa Musulunci gurbin da s**a rasa, tabbas ba mu yi nadamar kasancewa tare da shi ba a lokacin da aka tsangwamemu saboda shi

Yaa Allah Ka jikansa da rahama, Ka hada fuskokinmu da shi a cikin Aljannah Madaukakiya

Daga Datti Assalfi

DA DUMI-DUMI: Yadda kawancen yan adawa na ADC ya hana Tinubu da APC barciDaga A Yau A zaben shugaban kasa na 2023, ga ya...
02/07/2025

DA DUMI-DUMI: Yadda kawancen yan adawa na ADC ya hana Tinubu da APC barci

Daga A Yau

A zaben shugaban kasa na 2023, ga yadda manyan 'yan takarar s**a samu kuri'u a hukumance k**ar yadda INEC ta sanar:

1. Bola Tinubu (APC) – 8,794,726 (36.61%)

2. Atiku Abubakar (PDP) – 6,984,520 (29.07%)

3. Peter Obi (LP) – 6,101,533 (25.40%)

Yanzu da Atiku da Peter Obi s**a hade a karkashin sabuwar kawancen ADC don ceto Najeriya, hakan na nufin za su iya hade kuri’un su domin kalubalantar APC da gaske a zabe mai zuwa. Idan aka hada jimillar kuri'un Atiku da Obi na 2023, za su wuce na Tinubu da nisa sosai.

Wannan zai sa APC da Tinubu su yi taka-tsantsan, musamman ganin cewa kawancen zai iya tara goyon baya daga bangarori daban-daban na kasar, kuma ya samu karbuwa a tsakanin matasa da masu neman sauyi.

Kuna ga wannan kawance na yan adawa zai yi tasiri?

Me za ku ce?

Gamayyar Jagororin Siyasa Sun Kafa Sabuwar Hadaka Ta ADC Don Kalubalantar Tinubu a 2027Jiga-jigan jam’iyyun adawa a Naje...
02/07/2025

Gamayyar Jagororin Siyasa Sun Kafa Sabuwar Hadaka Ta ADC Don Kalubalantar Tinubu a 2027

Jiga-jigan jam’iyyun adawa a Najeriya sun jingine ADA da SDP, sun kuma ayyana African Democratic Congress (ADC) a matsayin sabuwar jam’iyyar hadaka da za su yi amfani da ita wajen kalubalantar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027 mai zuwa.

An nada Sanata David Mark a matsayin shugaban rikon kwarya, yayin da tsohon Gwamnan Osun, Ogbeni Rauf Aregbesola, ya zama Sakataren jam’iyyar.

Wannan mataki na nuna yadda ‘yan adawa ke kokarin hada kai domin karfafa gwiwa da samun nasara a babban zaben da ke tafe.

Shin kuna ganin wannan sabuwar hadaka zata iya samun nasara a Zaben 2027?

WATA SABUWA: Uba ya lakadawa saurayin ‘yarsa duka bayan ya k**a su suna lalataWani mutum ya fusata matuka bayan ya dawo ...
02/07/2025

WATA SABUWA: Uba ya lakadawa saurayin ‘yarsa duka bayan ya k**a su suna lalata

Wani mutum ya fusata matuka bayan ya dawo gida ba zato ba tsammani ya tarar da ‘yarsa da saurayinta suna aikata abin kunya. Cikin fushi da bacin rai, sai ya afka wa saurayin ya dinga jibgarsa.

JARIDAR A yau ta ruwaito saurayin, wanda aka bayyana sunansa da Alex, ya samu raunuka da dama kafin yan sanda s**a kawo dauki aka kwashe shi zuwa asibiti

Me zaku ce?

Adresse

Area 2 Mashood Abiola Road Abuja
Democratic Republic Of The

Site Web

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Nigerian News Hausa publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Partager