Media Forum Jos Zone

Media Forum Jos Zone Maraba da Zuwa Shafin Media Forum Jos Zone, Shafi domin Samun Rahotanni Dangane da Harkar Musulunci.

Yunƙurin haɗin Kan Malaman addinin Musulunci, Prof. Ibraheem Maqari da tawagarshi sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zak...
02/11/2025

Yunƙurin haɗin Kan Malaman addinin Musulunci, Prof. Ibraheem Maqari da tawagarshi sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) yau Lahadi a gidansa dake Abuja.

Bayan gabatar da jawabai da shawarwari akan muhimmancin haɗin kai da kusantar juna tsakanin malaman addini, Jagora (H) ya ƙarfafi wannan ƙoƙari sannan yayi fatan alkhairi da samun nasara.




02/11/2025

JAGORA (H) YA RUFE MU’UTAMAR DIN MEDIA FORUM A ABUJADaga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)Da yammacin Asabar 10 ga Jim...
01/11/2025

JAGORA (H) YA RUFE MU’UTAMAR DIN MEDIA FORUM A ABUJA

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Da yammacin Asabar 10 ga Jimadal Ula, 1447 (1/11/2025) Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya rufe Mu'utamar da Dandalin Yaɗa Labaran Harkar Musulunci (Media Forum) a gidansa da ke Abuja.

Mu'utamar ɗin wanda Media Forum ta shirya na yini daya a garin Abuja, ya tattaro mahalarta daga dukkan sassan kasar nan, tare da wakilai daga bangarori daban-daban na Media din Harka Islamiyya, inda aka gabatar da jawabai akan Maudu'ai daban-daban da s**a shafi aikin jarida da Nizami Harka Islamiyya.

A yayin jawabinsa, Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky ya fara da bayyana tarihin yadda al’amarin isar da sako ta hanyar ‘media’ ya faro a Harkar Musulunci da buga ‘yan takardu masu isar da sako, daga bisani aka yi yunkurin samar da Mujallar Turanci mai suna Al-Mizan a farkon shekarun 1980s, inda a farkon shekarun 1990s aka samar da jaridar Hausa ta Almizan mai falle biyu, daga baya ta rika fadada tare da tasiri mai girma dukkan sassan kasar nan.

Harwayau, Jagora ya bayyana yadda aka rika samar da Jaridun Turanci na Pointer, da Pointer Express, da kuma Mujallu irin su Mujallar Gwagwarmaya, Mujallar Mujahida da sauransu, wanda duk daga baya s**a kwanta. Inda ya dauki lokaci yana bayani akan zuwan Intanet, da yadda ya rika cigaba har zuwa ga samuwar ‘Social Media’, wanda ya kunshi rubutu, hoto, da hoto mai motsi, kuma ake amfani da shi wajen yada sakon kaitsaye a cikin lokaci, ba kamar yadda jaridun takarda suke da jinkiri ba.

Shaikh Zakzaky (H) ya ja hankalin masu bibiyan kafafen sadarwa akan su rika bashi lokacin da za su rika dubawa a kowane rana, domin kar ya rika cinye musu lokaci. Ya ce, “in ka lura da lokacin da kake ci a Social Media, za ka kuma tambayi kanka, awa nawa na yi a karatun Alkur’ani da Sallah da sauransu. Kamata ya yi kowane abu ka bashi lokacinsa, in ba haka ba sai ka bannata lokacinka, domin shi wannan abin na da cin rai.”

Ya kuma bayyana yadda Yammacin Duniya ke kokarin sarrafa kakafen, wanda dama mafi yawa mallakinsu ne. Yace, wanda ma ba nasu din ba ne, to s**an yi kokarin kutse a cikinsa don su samu cikakken daman iko da shi. Inda ya bayar da misali da yadda Tiktok ya rika fallasa ta’addancinsu, alhali suna iya ‘control’ din sauran kafafe irin su Facebook, wanda hakan yasa yanzu s**a yi kokarin sayen ‘share a Tiktok din, don su rika sa ido akan wadanda suke ‘posting’ abinda bai yi daidai da ra’ayinsu ba kamar yadda suke yi a sauran kafofin.

Jagora ya kuma jaddada muhimmancin kafafen na sadarwa, inda ya bayyana cewa sun fi kowane kafa isar da sako a yanzu, saboda su suna zuwa ga mutane ne nan take.

Ya nuna takaicinsa matuka, akan yadda ganin amfaninsa mai kyau, sai kuma makiya ke amfani mare kyau da shi wajen kirkiran farfaganda da karairayi, da kuma kirkiran rigingimu da hayaniyar da wasu da gangan suke tado maganar da za a yi ta musu da musayar raddodi, in an kammala akan wani abin saisu kara kunno wani daban. Ya ce: “Kamar wasu sun dauka idan suna surutai irin wannan ana ta zuzutasu, kamar yana daukaka sunansu ne. Suna son su yi kaurin suna ne.”

Yace: “Kar wannan masu neman su yi kaurin suna su dauke ma mutane hankali, ya kamata a yi banza da su ne, a yi kokari a gina abin kirki, wanda kuma shi ke wahala.

Jagora ya nuna takaicinsa akan yadda makiya addini ke ta kokarin sai sun baiwa ‘yan uwa Musulmi sunan kungiya, ya ce: “Tunda su sun ce su kungiya ne, wai ala dole mu ma kungiya ne. Kuma yanzu ma suna wani yayi, wai suna neman su yi kungiya, su ce wai har da mu a ciki. Nace haba! Ai linzami ya fi karfin bakin kaza! wani bai isa ya ce ya yi kungiya ya saka mu a ciki ba, mu mun wuce nan! Ba dai akan addinin nan ba.

“Mutane yanzu kowane na ta fito da wani abu, wai mu kungiya ce. Wa ya ce maka? Mu mun ce muna addini ne, mu muke ‘representing’ din addinin. Amma sai s**a ce wai har da kungiyar kaza, wai kungiyar Mazhaba. A kafafen watsa labaru, wai kungiyar Mazhabar Shi’a, ko ‘yan Shi’a, ko kaza. Wai ala dole, tunda su sun yi kungiya, to ku ma kungiya ne. To ku kuke da kungiya, mu muna addini ne, mu bamu da wata kungiya, mu abinda muke yi sunansa addini ne. Ku ku yi ta kungiyoyinku!” Inji Shaikh Zakzaky (H).

Ya kara da cewa: “Na’am, ku kungiya ne, amma mu ba kungiya ba ne, ba kuma za mu taba zama kungiya ba. Ba kuma za a taba saka mu a cikin kungiya ba. Mu addini muke yi. Addinin Musulunci. Tun farko bamu taba ce muku addinin Musuluncin kuma ya kasu kashi-kashi ba, ba mu taba ganinsa a kashi-kashi ba, mu mun san addinin Musulunci bai kasu kashi-kashi ba! Abu daya ne rak! Sakon da Manzon nan ya zo da shi daga wajen Allah. Illa-iyaka, zance ya kare.”

Harwayau, Jagora ya ja hankali akan kokarin gina Fikira Sahihiya na sanar da mutane mene ne addini a hakikarsa, da kuma yunkurin dawo da ikonsa ya tabbata daram a doron kasa, wanda yace makiya kan kasa fahimtarsa, su yi ta masa fassara daban-daban.

Ya bayyana yadda Alkur’ani ya kawo tarihin Annabawa da s**a zo s**a kirayi al’ummarsu daban-daban, yace sam ba a kan kungiya ko mulki ko sarauta suke ginawa da’awarsu ba. “Ana ce mutane su zo su bauta ma Allah a bisa ka’idar da aka saukar ne, abinda ake ce ma mutane kenan. Ba an ce musu su zo su shiga wata kungiya ne ba.”

Yace: “To mu ma mukan ce, tunda mun yi sa’a mu dama al’ummar Musulmi ne, abinda muke cewa, al’ummar ta dawo bisa addininta. Illa iyaka. Amma sai s**a ce ku kaza ne.”

Jagora ya ja hankali akan kar mu daka ta mutane wajen amsa sunan ‘yan kaza da suke saka ma mutane. Ya bukaci “a dora mutane ne akan Fikira Sahihiya na cewa, addini ake yunkurin tabbatarwa, addinin nan kuma sunansa Al-Islam, shi kuma Al-Islam din nan ‘shaamil’ ne, karkashinsa ne aka sami fahimta daban-daban. Fahimta daban-daban ba addinai ne daban-daban ba, fahimtar shi wannan addinin ne. Kuma ana batun in addinin ya kafu, to shi zai tafi ne bisa shi ka’idan addinin, ba son ran wani ba, ba fahimtar wani ba.”

Jagora ya jadda jan hankalin ‘yan uwa akan kar su bari a rika shagaltar da su da wasu abubuwan da ba shi ke gabansu ba. “Na san wasu janibobi da s**an fada tarko, in an zage su su yi zagi, ka ga an yi batsattsale a ciki. Kuma abinda wadancan suke so kenan. To kai kar ka yarda a kautar da kai daga abinda kake kai. Ka yi ta fadan abinda yake shi ne daidai. Mai zagi ya yi ta zage-zagensa, kai kuma ka yi ta yi, in ka daka tasa, za ka koma ne ka zama kana bashi amsa, kuma abinda yake so kenan. To mu kar mu daka tasu, ya zama kullum kokarin kwakkwafa mutane akan abinda yake shi ne daidai, da kuma tsayawa kyam, da yi domin Allah, yi don Allah, yi don Allah, insha Allah.”

Ya karkare jawabinsa da nasiha kamar yadda ya saba akan yin kpomai saboda Allah. Ya ce: “Ana yi ne saboda Allah. Yi don Allah, yi don Allah, yi don Allah, ba don ka yi suna ba. Kuma in ana tare ana aiki kar ka dauka kowa zai ba da hadin kai a yi lafiya lau a tafi, a’a dabi’an mutum ne, in aka tara mutane, sai an ji abubuwa, sai an ce, wannan shi ya yi kane-kane, ko kuwa wannan dan bani na iya, wancan in ba shi aka ce ba rigima za a yi. Wannan an dinga yi kenan, dama dan Adam ba a raba shi da wadannan abubuwan. Kai dai ka yi abinka kawai, in kana yi saboda Allah ne. In kana yi saboda mutane ne, sai ka bari in dominsu ne, amma in kana yi domin Allah ne sai ka yi.”

A karshe, Jagora ya rufe da addu’ar, Allah Ya ba mu ladan abubuwan da muke yi, kuma ya kai mu ga kyakkyawan natija.





01/11/2025

An ƙaddamar da shafin Intanet na Harkar Musulunci na Hausa Dandalin yaɗa labarai (Media Forum) na Harkar Musulunci a ƙar...
30/10/2025

An ƙaddamar da shafin Intanet na Harkar Musulunci na Hausa

Dandalin yaɗa labarai (Media Forum) na Harkar Musulunci a ƙarƙashin jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky na sanar da al'umma cewa an samar da sabon shafin Harkar Musulunci na Intanet na Hausa bayan ƙwace tsohon da Amurka ta yi a 2020.

Daga yanzu za ku iya samun labarai da rahotanni da bayanai na musamman dangane da Harkar Musulunci a wannan babban shafi na Intanet.

Za ku iya leƙa shafin a www.harkarmusulunci.ng

Sanarwa:
Media Forum Na Harkar Musulunci
30 Oktoba, 2025

Gagarumin taron bikin Mauludin Manzon Allah (SAWA) a garin Shendam.Hotuna daga gurin gagarumin Mauludi Manzon Allah (S) ...
14/10/2025

Gagarumin taron bikin Mauludin Manzon Allah (SAWA) a garin Shendam.

Hotuna daga gurin gagarumin Mauludi Manzon Allah (S) kenan daya gudana a yammacin yau Talata, 14 Oktoba, 2025 a garin Shendam jihar plateau wanda yan uwa Musulmi Almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) s**a shirya.

An fara taron ne da budewa da addu'a, se karatun Alqur'ani mai girma daga bakin ɗaliban Fudiya, se daga bisani yan fareti s**a gabatar da display don girmamawa ga fiyayyen halitta.

Sannan aka gabatar da Mai Jawabi wato Shaikh Muhammad Nuruddeen Ahmad Lafia. Yanda Malamin yayi takaitaccen bayanin Tarihin Manzon Rahama mai cike da shauki da gamsarwa ga mahalarta.

A cigaba da program ɗin har wala yau rundunar Jaishu Shaheed Ahmad Zakzaky (Jasaz) na garin Shendam sun bada kyautar littafin 'RAYUWATA' na Jagora (H) ga wani dan Shahidi mai suna Ahmad Ibrahim charanchi mai mahaifiya Zeenat. Sunyi kyautar ne don nuna murnan su na birthday commander Sayyid Ahmad ake cikin yi yanzu haka a Abuja. Kyautar wanda Shaikh Muhammad Nuruddeen ya mika shi a hannun Malam Uzairu Badamasi Kano a madadin shi ɗan shahidin (Ahmad).

Daga karshe aka gabatar da babban mawakin harkar musulunci Sidi Uzairu Badamasi Kano ya cigaba da rairo waken yabon Manzon Allah da iyalinsa da su Sayyid (H) har zuwa lokacin rufe taron.

Rahoto
Shendam Media
14 October, 2025

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihirraji'uun 💔 Sakon Ta'aziyya Na Media Forum Jos Zone Zuwa  Ga Ɗan Uwa Hassan Bala Al-Rafidhy N...
06/10/2025

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihirraji'uun 💔

Sakon Ta'aziyya Na Media Forum Jos Zone Zuwa Ga Ɗan Uwa Hassan Bala Al-Rafidhy Na Rashin Mahaifinsa !

بسم الله الرحمن الرحيم
إنا لله وإنا إليه راجعون
اللهم صلي على محمد وال محمد

A madadin dukkan Ƴan Media Forum na yankin Jos muna mika sakon Ta'aziyya ga ɗan uwa na gwagwarmaya Malam Hassan Bala wanda yayi rashin mahaifinsa a jiya Lahadi 05-Oct-2025, wanda aka yi jana'izarsa a yau Litinin 06-Oct-2025 da misalin ƙarfe 12:00Pm ba rana A Kofar gidan Marigayin da ke Badarawa, Kaduna.

Muna miƙa wannan sako gare ka tare da sauran ƴan uwanka na wannan Babban rashi. Muna roko da fatan Allah ya jikansa ya gafarta masa Ta kyautata Makwancinsa.



Labari Cikin Hotuna; Yadda Aka Gudanar Da Gagarumin Taron Mauludin Manzon Allah (S) A Garin JosA Jiya Lahadi 5 ga Watan ...
06/10/2025

Labari Cikin Hotuna; Yadda Aka Gudanar Da Gagarumin Taron Mauludin Manzon Allah (S) A Garin Jos

A Jiya Lahadi 5 ga Watan October 2025 Ƴan'uwa Musulmai Almajiran Shaikh Zakzaky (H) s**a Gudanar da Gagarumin Taron Mauludin Fiyayyen Halitta Manzon Allah Muhammad (S) wanda s**a Kira da Makon Haɗin Kan Musulmai, an Fara Gudanar da Taron ne da Misalin Ƙarfe 11 inda aka Buɗe da Addu'a tareda Karanta Alkur'ani mai Girma da Ziyarar Manzon Allah (S) sannan Sha'irai daga Ɓangaren Shi'a da Ɗarika s**a Rera Waƙokin Yabo na Manzon Allah da Ahlul Baiti.

Shaikh Sulaiman Jawundo daga Ɓangaren Ɗarikar Tijjaniyya ya Fara Gabatar da Jawabi akan Maudu'in (Wajibcin Haɗinkan Musulmai Da Yiwa Juna Uzuri) inda a Jawabin na Shaikh ɗin yake cewa shi Haɗinkai Umarmi ne na Allah Ta'ala akan mu, sannan Shaikh Abubakar T/Fulani shima daga Ɓangaren Ɗarikar Tijjaniyya ya Gabatar da Jawabi akan Maudu'in (Son Annabi Da Ahlul Baiti) Shaikh yayi Dogon Jawabi Dangane Maudu'in nasa inda Bayan ya Kammala akayi Sallah da Walimah.

Bayan an Dawo daga Sallah da Walimah sai Shaikh Lamin Salis daga Ɓangaren Ɗarikar Ƙadiriyya Ashabul Kahfi ya Gabatar da Jawabi akan Maudu'in (Taɓa Shaksiyyar Annabi Rusa Musulunci) inda Shaikh ɗin yayi Kule ga masu Taɓa Shaksiyyar Annabi, sannan Wakilin Ƴan'uwa na Garin Jos Shaikh Auwal Gangare Gangare yayi Khatamar Taron da Jawabi akan Maudu'in (Makirce-makircen Da Ƙasashen Akan Al'ummar Palasɗinu) inda Shaikh yayi Kira ga Al'ummar Musulmai da su Dawo Hayyacin su.

Yake cewa Al'umma su Sani cewa Hakkin Ƴan'uwan mu dake Palasɗinu ya Haukan Dukkan Al'ummar Musulmai na Duniya ne baki Ɗaya har ma da Waɗanda ba Musulmai ba Domin suma Mutane ne kamar kowa kuma suna da Ƴancin Rayuwa, Ɗaruruwan Al'umma Musulmai daga Ɓangaren Ɗarikar Tijjaniyya da Ƙadiriyya ne s**a Halarci Taron Mauludin wanda ya Gudana a Muhallin Ƴan'uwa na Hussainiyyatu Shaikh Zakzaky (H) dake Anguwan Rogo a Cikin Garin Jos Babban Birnin Jihar Plateau.

Hotuna; Abdulrazaq Isah

Ibrahim Muh'd Tahir
Forum Jos

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihirraji'uun 💔 Sakon Ta'aziyya Na Media Forum Jos Zone  Zuwa  Ga Ɗan Uwa Hassa Bala Al-Rafidhy N...
06/10/2025

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihirraji'uun 💔

Sakon Ta'aziyya Na Media Forum Jos Zone Zuwa Ga Ɗan Uwa Hassa Bala Al-Rafidhy Na Rashin Mahaifinsa !

بسم الله الرحمن الرحيم
إنا لله وإنا إليه راجعون
اللهم صلي على محمد وال محمد

A madadin dukkan Ƴan Media Forum na yankin Jos muna mika sakon Ta'aziyya ga ɗan uwa na gwagwarmaya Malam Hassan Bala wanda yayi rashin mahaifinsa a jiya Lahadi 05-Oct-2025, wanda aka yi jana'izarsa a yau Litinin 06-Oct-2025 da misalin ƙarfe 12:00Pm ba rana A Kofar gidan Marigayin da ke Badarawa, Kaduna.

Muna miƙa wannan sako gare ka tare da sauran ƴan uwanka na wannan Babban rashi. Muna roko da fatan Allah ya jikansa ya gafarta masa Ta kyautata Makwancinsa.



JAGORA YA GANA DA WAKILAN 'MEDIA FORUM'Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) Da yammacin Asabar 11 ga Rabi'ul Thani, ...
05/10/2025

JAGORA YA GANA DA WAKILAN 'MEDIA FORUM'

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Da yammacin Asabar 11 ga Rabi'ul Thani, 1447 (4/10/2025) Jagora, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gana da wakilan bangaren 'Media Forum' na Harkar Musulunci a gidansa da ke Abuja.

A yayin ganawar, Jagora ya fara da bayani akan Media, da yadda ta riƙa bunƙasa, inda ya bayyana samuwar Social Media a matsayin cigaba a daidai wannan lokacin. Sai dai ya koka da yadda mutane ke amfani da shi ba bisa yadda ya dace ba, ta yadda ake ƙirƙira musu abin cecekuce su yi ta fama, maimakon su mai da hankali akan abin da ya fi amfani.

Shaikh Zakzaky ya ƙarfafi muhimmancin dawo da jaridar Turanci da ake da ita mai suna Pointer Express, wanda ya bayar da tarihin kafuwarta daga farko har zuwa lokacin da ta durkushe a karo na biyu. Ya kuma nuna muhimmancin karfafa isar da sako a shafukan sadarwa kamar Website, da shafukan sada zumunta, kamar Facebook, X (Twitter), Instagram da sauransu, musamman da yarukan Ingilishi, French da kuma in dama ya bayar har da Larabci da Farsi.

Jagora ya jaddada jan hankali akan yadda ya dace a rika yin raddi. Ya ce, in aka samu mutum ɗaya ya yi magana akan abu ya gamsar, to ya wadatar, ba sai kowa ya sa baki har a shagaltar da mu da wannan abin ba. Ya bayyana yadda wasu ke bude shafuka da sunan 'yan uwa su yi ta abinda bai kamata ba. Ya ce, ya kamata Media Forum su fahimci yadda za su magance shirin maƙiya.

Harwayau, ya bayyana dacewar Media Forum ta kwakkwafe 'yan uwa ta hanyar yin tsari, da irshadi zuwa ga abinda shi ne daidai. A nan ne ya yaba wa Tiktok Team, kan yadda suke isar da saƙo ta hanyar yayyanka jawabai suna ɗorawa a shafukan Tiktok, inda ya ja hankali akan a riƙa sanin daidai gaɓan magana, inda ya dace a fara, da inda za a datse magana a yayin yankowa.

Jagora (H) ya bayyana manufar Media Forum a matsayin samar da tsari mai kyau na isar da sako a cikin 'yan uwa na Harka Islamiyya, kuma saƙo ya isa zuwa ga al'umma. Inda ya lissafa wasu ayyuka daban-daban da ya dace Media Forum din su tsayu da shi.

A karshe, Jagora (H) ya ja hankali akan yin aiki saboda Allah. Ya ce, aiki tare ya gaji matsaloli, da kushe, da guna-guni. Yace: "Amma in kana yi saboda mutane ne sai ka fasa in ka ji s**a, in kuwa don Allah ka ke yi, sai ka cigaba da abinka.”

Bayan jawabin Jagora (H), an assasa kwamiti mai dauke da mutane takwas, a matsayin masu kula da lamarin Media Forum a matakin baiɗaya (Centrallly), inda s**a ayyana Ammar Muhammad Rajab a matsayin shugaban Kwamitin na Media Forum. An baiwa kwamitin dama, su tsara ayyuka, da ayyana masu gudanar da Lajanar ta Media Forum a bangarori daban-daban na sassan Harka gabaɗaya.






11/RabiuThani/1447
04/10/2025

SANARWAR Gayyata Daga Da'irar Jos Gobe Ana gayyatar Ƴan'uwa Musulmi Maza da Mata, akwai gagarumin taron Mauludin Manzon ...
04/10/2025

SANARWAR Gayyata Daga Da'irar Jos Gobe

Ana gayyatar Ƴan'uwa Musulmi Maza da Mata, akwai gagarumin taron Mauludin Manzon Allah (Saww) tare da Makon haɗin kai ƙarƙashin Jagorancin Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) A Markaz Anguwan Rogo Jos.

Wanda za'ayi kamar haka..👇👇👇

GOBE:– Lahadi 05–October– 2025.

LOKACI:– 10:00 Am Na Safiya zuwa yamma.

WURI:– Hussainiyyatu Sheikh Zakzaky (H) Jos Anguwar Rogo Jos.

Allah ya bada ikon zuwa, Dan Allah a taya mu ya ɗawa...

Forum Jos
04-October-2023.

MALAM AUWAL GANGARE YA RUFE MUZAHARAR GARIN JOS ; Yadda Akai Yi Muzaharar Nuna Goyon Baya Ga Al'ummar Palasɗinu A Garin ...
03/10/2025

MALAM AUWAL GANGARE YA RUFE MUZAHARAR GARIN JOS ; Yadda Akai Yi Muzaharar Nuna Goyon Baya Ga Al'ummar Palasɗinu A Garin Jos

Da Misalin Karfe 9 na Safiyar wannan Rana ta Juma'a 3 ga Watan October 2025 Ƴan'uwa Musulmai Almajiran Shaikh Zakzaky (H) s**a Gudanar da Gagarumar Muzaharar Nuna Goyon Baya ga Al'ummar Palasɗinu a Cikin Garin Jos Babban Birnin Jihar Plateau.

Muzaharar ta Samu Halartan Ɗaruruwan Ƴan'uwa Maza da Mata inda inda aka Faro daga Bakin Gadar Bauchi Road aka Hauro ta Zololo sannan daga Bisani aka Tsaya a Babban Masallacin Juma'a na Garin Jos aka Gabatar da Slogans da kuma Jawabin Rufewa.

A Cikin Jawabin na Wakilin Ƴan'uwa na Garin Jos Sayyid Auwal Gangare yayi Bayanin Dalilin wannan Fitowar da Ƴan'uwa s**a yi sannan yayi Allah Wadai da Yunkurin Trump Shugaban Ƙasar America na sake Rura Wutar Yaki a Gaza dake Ƙasar Palasɗinu.

Hotuna:- Abdulrazaq Isah

Rohoto Ibrahim Muh'd Tahir

Media Forum Jos Zone

  TARON KYAUTATA ALAKA TSAKANIN MUSULMAI DA KIRISTA  KARO NA 18 HADE DA MAULIDIN MANZON (S) A GARIN LAFIA.Kwamitin Kyaut...
28/09/2025

TARON KYAUTATA ALAKA TSAKANIN MUSULMAI DA KIRISTA KARO NA 18 HADE DA MAULIDIN MANZON (S) A GARIN LAFIA.

Kwamitin Kyautata Alaka Tsakanin Musulmi da Kristoci Ƙarƙashin Jagoranci Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) a Yanki Lafia Jahar Nasarawa, sun sake Shirya taron Maulidin Fiyayyen Halitta Annabi Muhammad (S) hade da kyautata Alaka tsakani Al'ummar Musulmi da Kuma Kiristoci Karo Na 18 a garin Lafia Jahar Nasarawa a jiya Asabar 27th September 2025.
Inda s**a Gayyaci Kiristoci da bangarorin Al'umma Musulmi s**a gabatar da jawabai akan maudu'ai daban-Daban a wajan taron.

Taron Mai taken: Zaman Lafiya, Hadin Kai da Kuma Adalci wato ( , & ).
Ya gudana ne a Savannah Hall dake Jos Road Cikin garin Lafia jihar Nasarawa.

An Sadaukar da Ladar wannan Taron ga Ruhin Iyalan Gidan Jagora Shaikh Zakzaky (H).

©Media Forum Lafia
28/09/2025.

Adresse

Jos
Plateau

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Media Forum Jos Zone publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Contacter L'entreprise

Envoyer un message à Media Forum Jos Zone:

Partager