Media Forum Jos Zone

Media Forum Jos Zone Maraba da Zuwa Shafin Media Forum Jos Zone, Shafi domin Samun Rahotanni Dangane da Harkar Musulunci.

Alhamdulillah!
30/11/2025

Alhamdulillah!

TARON ƘARAWA JUNA SANI NA MEDIA FORUM JOSDandalin yaɗa labarai (Harkar Musulunci);na Harkar Musulunci ƙarƙashin jagoranc...
26/11/2025

TARON ƘARAWA JUNA SANI NA MEDIA FORUM JOS

Dandalin yaɗa labarai (Harkar Musulunci);na Harkar Musulunci ƙarƙashin jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) na Jos Team. Muna sanar da ku taron karawa juna sani (Mu'utamar), na wuni ɗaya wanda ya haɗa dukkan masu kula da aikin Media na ɓangarorin Harka Islamiyya da s**a haɗa da Hurras, Jasaz, ISMA, Academic Forum, Sisters Forum, Dandalin Matasa, Ittihadu Shu'ara, Shaikh Zakzaky Gallery da sauran su.

RANA: Asabar 29/11/2025
WURI: Fudiyyah Rinji.
LOKACI: 10:00 na safe zuwa ƙarfe 5:00 na Yamma.

ƘARIN BAYANI: da yake taron na wuni ɗaya ne akwai rijista da za a yi naira dubu ɗaya kacal. ₦1,000 ga kowanne mahalarci.

Allah ya bada ikon halarta. Ilahi ajeeb ya Allah.

A yau Talata 27 ga watan Jimada Ula, 1447 daidai da 18 ga watan Nuwamba, 2025, wasu wakilan gamayyar ƴan jaridun Arewa a...
19/11/2025

A yau Talata 27 ga watan Jimada Ula, 1447 daidai da 18 ga watan Nuwamba, 2025, wasu wakilan gamayyar ƴan jaridun Arewa a kafafen sada zumunta a ƙarƙashin inuwar 'Arewa Online Journalists Forum' sun ziyarci Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a gidansa dake Abuja.

Gamayyar sun bayyanawa Jagora (H) manufofin ƙungiyar, tare da neman shawarwari domin cimma gaci.

A yayin jawabi, Jagora (H) ya basu shawarar kiyaye yaɗa abin da za su rarraba kan al'umma tare haifar da yamutsi da sunan addini.




27/Jimada Ula/1447
18/11/2025

Saminaka !
17/11/2025

Saminaka !

Yadda Zaman Media Forum Ya Kasance A Garin Jos.
10/11/2025

Yadda Zaman Media Forum Ya Kasance A Garin Jos.

SANARWA DAGA DA'IRAR  JOS. Ana sanar da dukkan Ƴan’uwa Almajiran Shaikh Zakzaky (H) Na Da’irar Jos, Zuwa Wurin Zaman Juy...
05/11/2025

SANARWA DAGA DA'IRAR JOS.

Ana sanar da dukkan Ƴan’uwa Almajiran Shaikh Zakzaky (H) Na Da’irar Jos, Zuwa Wurin Zaman Juyayin Wafatin SAYYIDA Fatima Az-Zahra (S.a) Tsokar jikin Manzon Allah (Saww).

Taron zai kasance kamar haka 👇 👇 👇

RANAR:- Alhamis 06–11–2025

LOKACI:- Ƙarfe 4:30pm NA YAMMA

WURI:- HUSSAINIYYATU SHEIKH ZAKZAKY (H) JOS.

Tunatarwa; Dan Allah kowa ya kasance cikin baƙaƙen kaya.

Allah ya bada ikon zuwa, fatan za a taya mu yaɗa wannan saƙon.

Forum Jos.
05–11–2025

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya amshi baƙuncin Wakilan Al'ummar Unguwar Nasarawa Kaduna, da s**a haɗa Mr. Zakari, ...
04/11/2025

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya amshi baƙuncin
Wakilan Al'ummar Unguwar Nasarawa Kaduna, da s**a haɗa Mr. Zakari, wakilin ƙungiyar CAN a ƙaramar hukumar Chikun, Alh. Aliyu Mai Lafiya Chiroman Nasarawa, Mr. Dominic Babban Paston Catholic Church unguwar Nasarawa,
Sheikh Alaraamma Jabir Muhammad Babban Limamin Masallacin Juma'a Nasarawa da sauran abokan rakiyarsu.

"Kar ku yarda a hada Ku rigima da juna koda da wani Irin abu za'a kira rigimar,
Ko da Sunan Addini Ko da Sunan Qabila ku haɗe Kai ku zauna Lafiya.

Kiristoci ba Sunan Su Arna ba, Sunan da Allah ya ambace su a Qur'ani Ma'abotan littafi."-Jagora (H) yayin da yake masu bayanin muhimmancin zaman lafiya.




13/Jimada ula/1447
04/11/2025

HOTUNA GUDA 20:  Daga Hussainiyyah Bakiyatullah Zariya Na Juyayin Shahadar Sayyida Zahra (H) Tare Da Jagoran Harkar Musu...
04/11/2025

HOTUNA GUDA 20: Daga Hussainiyyah Bakiyatullah Zariya Na Juyayin Shahadar Sayyida Zahra (H) Tare Da Jagoran Harkar Musulunci Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Wasu daga cikin hotunan zaman Juyayin Shahadar Sayyida Fatima Zahra (As) wanda Jagoran Harkar Musulunci Sayyid Zakzaky (H), ya gudanar a Hussainiyyah Bakiyatullah Zariya a Shekarar 13 ga watan Afrilu 2013.

- Idishia Jos



Matsayar Jagora Sayyid Zakzaky (H) Akan Kalaman Shugaban Amurka Donald Trump.
03/11/2025

Matsayar Jagora Sayyid Zakzaky (H) Akan Kalaman Shugaban Amurka Donald Trump.

Yunƙurin haɗin Kan Malaman addinin Musulunci, Prof. Ibraheem Maqari da tawagarshi sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zak...
02/11/2025

Yunƙurin haɗin Kan Malaman addinin Musulunci, Prof. Ibraheem Maqari da tawagarshi sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) yau Lahadi a gidansa dake Abuja.

Bayan gabatar da jawabai da shawarwari akan muhimmancin haɗin kai da kusantar juna tsakanin malaman addini, Jagora (H) ya ƙarfafi wannan ƙoƙari sannan yayi fatan alkhairi da samun nasara.




02/11/2025

JAGORA (H) YA RUFE MU’UTAMAR DIN MEDIA FORUM A ABUJADaga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)Da yammacin Asabar 10 ga Jim...
01/11/2025

JAGORA (H) YA RUFE MU’UTAMAR DIN MEDIA FORUM A ABUJA

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Da yammacin Asabar 10 ga Jimadal Ula, 1447 (1/11/2025) Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya rufe Mu'utamar da Dandalin Yaɗa Labaran Harkar Musulunci (Media Forum) a gidansa da ke Abuja.

Mu'utamar ɗin wanda Media Forum ta shirya na yini daya a garin Abuja, ya tattaro mahalarta daga dukkan sassan kasar nan, tare da wakilai daga bangarori daban-daban na Media din Harka Islamiyya, inda aka gabatar da jawabai akan Maudu'ai daban-daban da s**a shafi aikin jarida da Nizami Harka Islamiyya.

A yayin jawabinsa, Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky ya fara da bayyana tarihin yadda al’amarin isar da sako ta hanyar ‘media’ ya faro a Harkar Musulunci da buga ‘yan takardu masu isar da sako, daga bisani aka yi yunkurin samar da Mujallar Turanci mai suna Al-Mizan a farkon shekarun 1980s, inda a farkon shekarun 1990s aka samar da jaridar Hausa ta Almizan mai falle biyu, daga baya ta rika fadada tare da tasiri mai girma dukkan sassan kasar nan.

Harwayau, Jagora ya bayyana yadda aka rika samar da Jaridun Turanci na Pointer, da Pointer Express, da kuma Mujallu irin su Mujallar Gwagwarmaya, Mujallar Mujahida da sauransu, wanda duk daga baya s**a kwanta. Inda ya dauki lokaci yana bayani akan zuwan Intanet, da yadda ya rika cigaba har zuwa ga samuwar ‘Social Media’, wanda ya kunshi rubutu, hoto, da hoto mai motsi, kuma ake amfani da shi wajen yada sakon kaitsaye a cikin lokaci, ba kamar yadda jaridun takarda suke da jinkiri ba.

Shaikh Zakzaky (H) ya ja hankalin masu bibiyan kafafen sadarwa akan su rika bashi lokacin da za su rika dubawa a kowane rana, domin kar ya rika cinye musu lokaci. Ya ce, “in ka lura da lokacin da kake ci a Social Media, za ka kuma tambayi kanka, awa nawa na yi a karatun Alkur’ani da Sallah da sauransu. Kamata ya yi kowane abu ka bashi lokacinsa, in ba haka ba sai ka bannata lokacinka, domin shi wannan abin na da cin rai.”

Ya kuma bayyana yadda Yammacin Duniya ke kokarin sarrafa kakafen, wanda dama mafi yawa mallakinsu ne. Yace, wanda ma ba nasu din ba ne, to s**an yi kokarin kutse a cikinsa don su samu cikakken daman iko da shi. Inda ya bayar da misali da yadda Tiktok ya rika fallasa ta’addancinsu, alhali suna iya ‘control’ din sauran kafafe irin su Facebook, wanda hakan yasa yanzu s**a yi kokarin sayen ‘share a Tiktok din, don su rika sa ido akan wadanda suke ‘posting’ abinda bai yi daidai da ra’ayinsu ba kamar yadda suke yi a sauran kafofin.

Jagora ya kuma jaddada muhimmancin kafafen na sadarwa, inda ya bayyana cewa sun fi kowane kafa isar da sako a yanzu, saboda su suna zuwa ga mutane ne nan take.

Ya nuna takaicinsa matuka, akan yadda ganin amfaninsa mai kyau, sai kuma makiya ke amfani mare kyau da shi wajen kirkiran farfaganda da karairayi, da kuma kirkiran rigingimu da hayaniyar da wasu da gangan suke tado maganar da za a yi ta musu da musayar raddodi, in an kammala akan wani abin saisu kara kunno wani daban. Ya ce: “Kamar wasu sun dauka idan suna surutai irin wannan ana ta zuzutasu, kamar yana daukaka sunansu ne. Suna son su yi kaurin suna ne.”

Yace: “Kar wannan masu neman su yi kaurin suna su dauke ma mutane hankali, ya kamata a yi banza da su ne, a yi kokari a gina abin kirki, wanda kuma shi ke wahala.

Jagora ya nuna takaicinsa akan yadda makiya addini ke ta kokarin sai sun baiwa ‘yan uwa Musulmi sunan kungiya, ya ce: “Tunda su sun ce su kungiya ne, wai ala dole mu ma kungiya ne. Kuma yanzu ma suna wani yayi, wai suna neman su yi kungiya, su ce wai har da mu a ciki. Nace haba! Ai linzami ya fi karfin bakin kaza! wani bai isa ya ce ya yi kungiya ya saka mu a ciki ba, mu mun wuce nan! Ba dai akan addinin nan ba.

“Mutane yanzu kowane na ta fito da wani abu, wai mu kungiya ce. Wa ya ce maka? Mu mun ce muna addini ne, mu muke ‘representing’ din addinin. Amma sai s**a ce wai har da kungiyar kaza, wai kungiyar Mazhaba. A kafafen watsa labaru, wai kungiyar Mazhabar Shi’a, ko ‘yan Shi’a, ko kaza. Wai ala dole, tunda su sun yi kungiya, to ku ma kungiya ne. To ku kuke da kungiya, mu muna addini ne, mu bamu da wata kungiya, mu abinda muke yi sunansa addini ne. Ku ku yi ta kungiyoyinku!” Inji Shaikh Zakzaky (H).

Ya kara da cewa: “Na’am, ku kungiya ne, amma mu ba kungiya ba ne, ba kuma za mu taba zama kungiya ba. Ba kuma za a taba saka mu a cikin kungiya ba. Mu addini muke yi. Addinin Musulunci. Tun farko bamu taba ce muku addinin Musuluncin kuma ya kasu kashi-kashi ba, ba mu taba ganinsa a kashi-kashi ba, mu mun san addinin Musulunci bai kasu kashi-kashi ba! Abu daya ne rak! Sakon da Manzon nan ya zo da shi daga wajen Allah. Illa-iyaka, zance ya kare.”

Harwayau, Jagora ya ja hankali akan kokarin gina Fikira Sahihiya na sanar da mutane mene ne addini a hakikarsa, da kuma yunkurin dawo da ikonsa ya tabbata daram a doron kasa, wanda yace makiya kan kasa fahimtarsa, su yi ta masa fassara daban-daban.

Ya bayyana yadda Alkur’ani ya kawo tarihin Annabawa da s**a zo s**a kirayi al’ummarsu daban-daban, yace sam ba a kan kungiya ko mulki ko sarauta suke ginawa da’awarsu ba. “Ana ce mutane su zo su bauta ma Allah a bisa ka’idar da aka saukar ne, abinda ake ce ma mutane kenan. Ba an ce musu su zo su shiga wata kungiya ne ba.”

Yace: “To mu ma mukan ce, tunda mun yi sa’a mu dama al’ummar Musulmi ne, abinda muke cewa, al’ummar ta dawo bisa addininta. Illa iyaka. Amma sai s**a ce ku kaza ne.”

Jagora ya ja hankali akan kar mu daka ta mutane wajen amsa sunan ‘yan kaza da suke saka ma mutane. Ya bukaci “a dora mutane ne akan Fikira Sahihiya na cewa, addini ake yunkurin tabbatarwa, addinin nan kuma sunansa Al-Islam, shi kuma Al-Islam din nan ‘shaamil’ ne, karkashinsa ne aka sami fahimta daban-daban. Fahimta daban-daban ba addinai ne daban-daban ba, fahimtar shi wannan addinin ne. Kuma ana batun in addinin ya kafu, to shi zai tafi ne bisa shi ka’idan addinin, ba son ran wani ba, ba fahimtar wani ba.”

Jagora ya jadda jan hankalin ‘yan uwa akan kar su bari a rika shagaltar da su da wasu abubuwan da ba shi ke gabansu ba. “Na san wasu janibobi da s**an fada tarko, in an zage su su yi zagi, ka ga an yi batsattsale a ciki. Kuma abinda wadancan suke so kenan. To kai kar ka yarda a kautar da kai daga abinda kake kai. Ka yi ta fadan abinda yake shi ne daidai. Mai zagi ya yi ta zage-zagensa, kai kuma ka yi ta yi, in ka daka tasa, za ka koma ne ka zama kana bashi amsa, kuma abinda yake so kenan. To mu kar mu daka tasu, ya zama kullum kokarin kwakkwafa mutane akan abinda yake shi ne daidai, da kuma tsayawa kyam, da yi domin Allah, yi don Allah, yi don Allah, insha Allah.”

Ya karkare jawabinsa da nasiha kamar yadda ya saba akan yin kpomai saboda Allah. Ya ce: “Ana yi ne saboda Allah. Yi don Allah, yi don Allah, yi don Allah, ba don ka yi suna ba. Kuma in ana tare ana aiki kar ka dauka kowa zai ba da hadin kai a yi lafiya lau a tafi, a’a dabi’an mutum ne, in aka tara mutane, sai an ji abubuwa, sai an ce, wannan shi ya yi kane-kane, ko kuwa wannan dan bani na iya, wancan in ba shi aka ce ba rigima za a yi. Wannan an dinga yi kenan, dama dan Adam ba a raba shi da wadannan abubuwan. Kai dai ka yi abinka kawai, in kana yi saboda Allah ne. In kana yi saboda mutane ne, sai ka bari in dominsu ne, amma in kana yi domin Allah ne sai ka yi.”

A karshe, Jagora ya rufe da addu’ar, Allah Ya ba mu ladan abubuwan da muke yi, kuma ya kai mu ga kyakkyawan natija.





01/11/2025

Adresse

Jos
Plateau

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Media Forum Jos Zone publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Contacter L'entreprise

Envoyer un message à Media Forum Jos Zone:

Partager