CGTN Hausa

CGTN Hausa Sashen Hausa na Gidan Rediyon Kasar Sin
http://hausa.cri.cn/
(417)

Xi Jinping ya halarci bikin marhaba da Kim Jong-un ya shirya masaA yau Litinin ne babban sakataren kwamitin kolin Jam’iy...
08/06/2026

Xi Jinping ya halarci bikin marhaba da Kim Jong-un ya shirya masa
A yau Litinin ne babban sakataren kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban kasar, Xi Jinping, ya isa birnin Pyongyang don fara ziyarar aiki a kasar Koriya ta Arewa.
A kuma yau din, shugaba Xi da uwargidansa Peng Liyuan sun isa filin taro na Kim Il-sung dake birnin Pyongyang, inda babban sakataren jam'iyyar 'yan kwadago ta Koriya ta Arewa, kana shugaban kasar Kim Jong-un, ya shirya gagarumin bikin marhaba ga shugaba Xi Jinping.
Lokacin da Xi da uwargidansa Peng Liyuan s**a isa filin Kim Il-sung, sojin dawakai sun yi jerin gwano suna musu maraba da zuwa, kuma makada na soja sun yi kida na maraba. Yayin da shugaba Kim Jong-un da matarsa Ri Sol-ju s**a tarbe su.
Manyan shugabannin kasashen biyu sun hau dandalin kallo dake filin tare, kana makada na soja sun yi taken kasashen Sin da Koriya ta Arewa, kafin daga bisani an harba bindigogi sau 21 domin nuna girmamawa ga manyan baki. Bisa rakiyar Kim Jong-un, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya duba rukunin faretin girmamawa na sojojin kasa, da sama, da ruwa na Koriya ta Arewa.
Jama'ar birnin Pyongyang, ciki har da yara kanana sanye da kayayyakin biki, rike da tutoci, da furanni da balan-balan, sun yi lale marhabin da babban bakon da ya ziyarci kasarsu.
Bayan bikin maraba, Xi Jinping da Peng Liyuan sun tafi masaukin baki mai suna Kumsusan, bisa rakiyar Kim Jong-un da matarsa Ri Sol-ju. (Amina Xu)

https://hausa.cgtn.com/2026/06/08/ARTI1780900613111835

 Kokarin Gadon Al’adun Gargajiyadaga CGTN HausaAl’ummar kasar Sin suna kokarin karewa da gadon al’adunsu na gargajiya, d...
08/06/2026


Kokarin Gadon Al’adun Gargajiya
daga CGTN Hausa

Al’ummar kasar Sin suna kokarin karewa da gadon al’adunsu na gargajiya, don tabbatar da cewa ba a manta da abubuwa masu daraja na al’adun gargajiya ba. (Bello Wang)

 Kokarin Samar Da Ingantaccen Muhallin HalittuJama’ar kasar Sin suna kokarin hadin kai a tsakaninsu, wajen samar da inga...
08/06/2026


Kokarin Samar Da Ingantaccen Muhallin Halittu

Jama’ar kasar Sin suna kokarin hadin kai a tsakaninsu, wajen samar da ingantaccen muhallin halittu a kasar, tare da ba shi kariya mai dorewa yadda ake bukata. (Bello Wang)

Iran ta kaiwa Isra'ila "harin gargadi" yayin da Trump ya bukaci bangaren Isra'ila da ya kai zuciya nesaA jiya Lahadi kas...
08/06/2026

Iran ta kaiwa Isra'ila "harin gargadi" yayin da Trump ya bukaci bangaren Isra'ila da ya kai zuciya nesa
A jiya Lahadi kasar Iran ta kai hari da mak**ai masu linzami a arewacin Isra'ila, wanda ta ce na "gargadi" ne. Iran ta ce hakan martani ne ga fadada ayyukan soji da Isra'ila ke yi a Lebanon.
Sojojin Isra'ila sun ce sun kakkabo dukkan mak**ai masu linzami da aka harba, sannan sun ce za su kara kaimi wajen dakile kungiyar Hezbollah ta Lebanon, tare da rufe wata muhimmiyar kofar shiga zirin Gaza.
A nasa bangare kuwa, shugaban Amurka Donald Trump cewa ya yi dole ne Iran ta dakatar da matakan soji, ta koma kan teburin tattaunawa, kuma zai ja hankalin firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu da kada ya rama harin na Iran.
Wannan shi ne hari na farko da Iran ta kai wa Isra'ila hari, cikin kusan watanni biyu da fara aiwatar da matakin tsagaita wuta. Kuma rundunar tsaron kasa ta juyin juya hali ta Iran ko IRGC ta fitar da sanarwa, wadda ke cewa IRGC din ta yi amfani da mak**ai masu linzami wajen kai hari kan sansanin sojan saman Ramat David dake arewacin Isra'ila, a matsayin martani ga ayyukan soji da Isra'ila ke aiwatarwa a kudancin Lebanon da kuma kudancin birnin Beirut. Sansanin yana daya daga cikin muhimman sansanonin da Isra'ila ke amfani da su wajen aiwatar da ayyukan soji. (Amina Xu)
https://hausa.cgtn.com/2026/06/08/ARTI1780887732416687

Kungiyar kasashe masu arzikin man fetur ta OPEC da abokan kawancenta ko OPEC+, sun bayyana aniyarsu ta kara adadin man d...
08/06/2026

Kungiyar kasashe masu arzikin man fetur ta OPEC da abokan kawancenta ko OPEC+, sun bayyana aniyarsu ta kara adadin man da suke fitarwa da ganga 188,000 a kullum, tun daga watan Yuli mai zuwa.
Hakan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da OPEC din ta fitar a jiya Lahadi, bayan kammala taron membobin kungiyar ta kafar intanet, wanda kasashen Saudiyya, da Rasha, da Iraqi, da Kuwait, da Kazakhstan, da Aljeriya da Oman s**a halarta, tare da sake nazartar yanayin kasuwar mai ta duniya da kuma hasashen makomarta.
Wannan ne wata na hudu a jere da hadakar OPEC+ ke kara adadin mai da membobinta ke fitarwa, duk da ficewar hadaddiyar daular Larabawa daga hadakar ta OPEC da OPEC+ a ranar daya ga watan Mayu.
Sanarwar da hadakar ta fitar, ta kara da cewa dalilin kara adadin man da membobinta bakwai s**a ayyana fitarwa, shi ne burin bai daya na tallafawa daidaiton kasuwar mai. Kuma za su ci gaba da daidaita cikakkun matakan fitar da mai gwargwadon yanayin kasuwa.
Kasashen dake cikin hadakar ta OPEC+ sun amince da sake ganawa a ranar 5 ga watan Yuli mai zuwa don sake yanke shawarwari. (Saminu Alhassan)

Shugaban kasar Sin ya k**a hanyar zuwa ziyara a Koriya ta ArewaDa safiyar yau Litinin 8 ga watan nan na Yuni, babban sak...
08/06/2026

Shugaban kasar Sin ya k**a hanyar zuwa ziyara a Koriya ta Arewa
Da safiyar yau Litinin 8 ga watan nan na Yuni, babban sakataren kwamitin kolin jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban kasar Xi Jinping, ya tashi daga birnin Beijing ta jirgin sama na musamman zuwa Koriya ta Arewa, bisa gayyatar da babban sakataren jam'iyyar 'yan kwadago ta Koriya ta Arewa, kuma shugaban kasar Kim Jong-un ya yi masa.
Shugaba Xi ya tashi zuwa Koriya ta Arewa da rakiyar uwargidansa Peng Liyuan, da memban ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar jam'iyyar Kwaminis ta Sin, kana darektan ofishin kwamitin tsakiya na jam'iyyar, Cai Qi, da kuma memban ofishin siyasa na jam'iyyar, kana ministan harkokin waje na kasar Sin, Wang Yi , da dai sauransu. (Amina Xu)
https://hausa.cgtn.com/2026/06/08/ARTI1780886703893672

Babban sakataren kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin kana shugaban kasar, Xi Jinping, ya ce dangantakar kasar...
08/06/2026

Babban sakataren kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin kana shugaban kasar, Xi Jinping, ya ce dangantakar kasarsa da Koriya ta Arewa na kan wani sabon mafari na tarihi, inda suke fuskantar sabbin damammakin ci gaba, kana suna rike da sabbin kudurori masu dacewa da lokutan da ake ciki.
Shugaba Xi, ya bayyana hakan ne a Litinin din nan, cikin wata makala mai dauke da sa hannunsa, wadda aka wallafa a mujallar Rodong Sinmun mallakin gwamnatin Koriya ta Arewa. An wallafa makalar ne gabanin ziyarar aiki da shugaban na Sin zai gudanar a Koriya ta Arewa a yau Litinin zuwa gobe Talata, ziyarar da za ta kasance ta farko cikin shekaru bakwai.
Cikin makalar, shugaba Xi ya ce wanzarwa, da karfafa alakar Sin da Koriya ta Arewa sun zamo tabbatattun manufofi na Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da gwamnatin Sin, kuma kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da Koriya ta Arewa wajen bunkasa dangantakar sassan biyu ta mahangar manyan tsare-tsare, da dacewar alakarsu da lokutan da ake ciki, da ma burinsu na cimma manyan nasarorin raya dangantakarsu. (Saminu Alhassan)

Yayin da ake gudanar da shirye shiryen bikin ranar demokradiyya a tarayyar Najeriya, mataimakin shugaban kasa Sanata Kas...
08/06/2026

Yayin da ake gudanar da shirye shiryen bikin ranar demokradiyya a tarayyar Najeriya, mataimakin shugaban kasa Sanata Kashim Shettima ya jagoranci addu`o`i na musamman a karshen makon jiya a birnin Abuja, inda ya bukaci al`ummar kasar da su dukufa addu`o`in neman zaman lafiya.
Taron addu`o`in da aka gudanar a babban masallacin birnin Abuja ya sami halartar ministoci da manyan jami`an gwamnati da malaman addinin Musulunci da sauran al`ummar kasa.
Daga tarayyar Najeriya wakilin mu Garba Abdullahi Bagwai ya aiko mana da rahoto.
https://hausa.cgtn.com/2026/06/08/ARTI1780881226747733

Gwamnatin jihar Borno ta bayar da umarnin daukar sabbin ma`aikata har 350, da s**a hada da likitoci, domin aiki a sabon ...
08/06/2026

Gwamnatin jihar Borno ta bayar da umarnin daukar sabbin ma`aikata har 350, da s**a hada da likitoci, domin aiki a sabon asibitin koyarwa na buliyoyin naira da ake daf da kammala ginawa a birnin Maiduguri.
Gwamnan jihar farfesa Babagana Umara Zulum ne ya tabbatar da hakan a karshen makon jiya, lokacin da ya kai ziyarar gani da ido harabar asibitin, ya ce sabon asibitin koyarwa na Jami`ar Kashim Ibrahim an tsara zai dauki gadaje 400 kuma nan da watanni biyu za a kammala shi.
Daga tarayyar Najeriya wakilin mu Garba Abdullahi Bagwai ya aiko mana da rahoto.
https://hausa.cgtn.com/2026/06/08/ARTI1780880515148721

Address

16A Shijingshan Road
Beijing
100040

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when CGTN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to CGTN Hausa:

Share