08/06/2026
Xi Jinping ya halarci bikin marhaba da Kim Jong-un ya shirya masa
A yau Litinin ne babban sakataren kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban kasar, Xi Jinping, ya isa birnin Pyongyang don fara ziyarar aiki a kasar Koriya ta Arewa.
A kuma yau din, shugaba Xi da uwargidansa Peng Liyuan sun isa filin taro na Kim Il-sung dake birnin Pyongyang, inda babban sakataren jam'iyyar 'yan kwadago ta Koriya ta Arewa, kana shugaban kasar Kim Jong-un, ya shirya gagarumin bikin marhaba ga shugaba Xi Jinping.
Lokacin da Xi da uwargidansa Peng Liyuan s**a isa filin Kim Il-sung, sojin dawakai sun yi jerin gwano suna musu maraba da zuwa, kuma makada na soja sun yi kida na maraba. Yayin da shugaba Kim Jong-un da matarsa Ri Sol-ju s**a tarbe su.
Manyan shugabannin kasashen biyu sun hau dandalin kallo dake filin tare, kana makada na soja sun yi taken kasashen Sin da Koriya ta Arewa, kafin daga bisani an harba bindigogi sau 21 domin nuna girmamawa ga manyan baki. Bisa rakiyar Kim Jong-un, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya duba rukunin faretin girmamawa na sojojin kasa, da sama, da ruwa na Koriya ta Arewa.
Jama'ar birnin Pyongyang, ciki har da yara kanana sanye da kayayyakin biki, rike da tutoci, da furanni da balan-balan, sun yi lale marhabin da babban bakon da ya ziyarci kasarsu.
Bayan bikin maraba, Xi Jinping da Peng Liyuan sun tafi masaukin baki mai suna Kumsusan, bisa rakiyar Kim Jong-un da matarsa Ri Sol-ju. (Amina Xu)
https://hausa.cgtn.com/2026/06/08/ARTI1780900613111835