Musa Albany Dabai

Musa Albany Dabai Na bude wannan shafin ne domin sanya rubututtukan da zasu amfani al'ummar Musulmi. Kuma ni Albany Da

04/11/2024

IBNU MUSDIY

Abinda na rubuta a sama, haka malamai da yawa su ke rubutawa, wato za a yi wa "mimun" ɗin "rufu'a" sai a yi wa "sinun" ɗin "ɗauri". Wasu malam kuma su na rubutawa k**ar haka: IBNU MASDIY, wato za a yi wa "mimun" ɗin "fat'ha". Wasu kuma su na rubutawa k**ar haka: IBNU MUSDIN, wato k**ar dai na farkon kenan, amma a ƙarshe za a yi wa "dalun" ɗin "tanwini" (a sanya masa "kasra" guda biyu maimakon a sanya harafin "ya'un" a ƙarshen sunan).

Sunansa Muhammad bin Yusuf bin Musa bin Yusuf bin Musa bin Yusuf bin Ibrahim bin Abdillahi. Abubakr Al-azdiy, Al-andalsiy. An haife shi a shekara ta 598 ko 599 a wani gari da ake kira Ash a Garnaaɗah da ke Andalus. Babban malamin hadisi ne mahaddaci, limami, mai khuɗuba a Haramin Makka. Ya yi karatu a hannun malaman Tunusia da Dimashƙa da Magrib. Ya zauna a Masar, kuma ya yi karatu a hannun Masarawa.

Mudallisi ne, Ibnu Hajar ya ambace shi a cikin littafinsa "Ɗabkƙaatul Mudallisina", shi ne mutum na 26 a cikin su 33 ƴan martaba ta farko. Haka nan ya siffanta shi da wahami da shi'anci a cikin littafin "Lisanul Mizan" (7/601/7587) k**ar yadda Zahabi ya siffanta shi da hakan a cikin "Al-mizan" (4/73/8346). Malamai da yawa su na siffanta shi da shi'anci da bidi'a (wato ya wuce gona da iri a harkar), domin an ce ya na faɗin maganganu a kan Uwar muminai - Allah ya ƙara mata yarda, amin.

Ya yi rubuce-rubuce ma su yawa, daga cikinsu akwai "Musnadul Garib", wanda ya tattaro mazhabobin malaman hadisi. Ya na da littafin Araba'una Hadis, wanda ya yi magana a kan hadisan aikin hajji da ziyara. Ya na da littafin "Mu'ujam" da ya yi tarjamar malamansa a cikin mujalladi uku manya. Ya na da malamai masu yawan gaske (har da waɗanda ya yi riwaya da ijaza a wurinsu). Ya yi karatu a hannun kakansa Musa bin Yusuf. Daga cikin ɗalibansa akwai Al-hafizud Dimyaaɗi (malamin su Imamuz Zahabi). Haka nan Imamud Daraƙudniy ya na da riwayar hadisansa.

Ya rasu (an kashe shi) a Makka a shekara ta 663 bayan hijira.
Allah ya gafarta masa. Allah ya sa ya na cikin aminci, amin.

,
Cairo, Egypt.
4th Nov., 2024.

08/09/2024

YA HALATTA KO BAI HALATTA BA?!

Idan mutum ya shiga masallaci, sai ya iske Liman an riga an fara sallar farilla, k**ar a sallar asuba da ake yin dogon karatu, mutum zai iya yin nafila ko ba zai yi ba?

Akwai hadisi da Imamu Muslim (712), Abu Dawud (1265) Nasa'i (868), Ibnu Majah (1152) da Ahmad (20777) su ka ruwaito daga Sahabi Abdullahi bin Sarjis (na ambaci tarjamarsa a cikin littafi na "Ma su suna Abdullahi a cikin Sahabbai") cewar wani mutum ya shigo masallaci alhalin Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya fara sallar asuba, sai mutumin ya kabbara nafila, bayan ya sallame sai ya jona aka yi sallar asuba tare da shi (kuma alamu na nuna ya samu sallar asuba duka), lokacin da aka sallame sallar, sai Ma'aiki alaihis salam ya ce masa: "Ya kai wane, wacce ce sallar (asubar) ta ka, wadda ka yi kai kaɗai ko kuwa wadda ka yi tare da mu?"

Ibnu Abduilbarr a cikin "Attamhid" (22/68) ƙarƙashin hadisin Abu Salama bin Abdirrahman ya ce: "wannan inkari ne Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya yi ga (dukkan ma su aikata) wannan aikin. (Don haka), bai halatta ga ko wane mutum ba, ya yi sallar nafila a cikin masallaci alhalin an tayar da sallar farilla".

Duka bayan wannan, akwai wani hadisin na Abu Huraira da ya fi fitowa sarari, wanda Imamu Muslim (710), Abu Dawud (1266), Tirmidhi (423) da Ibnu Majah (1151) su ka ruwaito, Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya ce: "idan aka tayar da salla (farilla), babu salla (nafila ko wace iri) sai ta farilla".

,
Cairo, Egypt.
8th Sept., 2024.

20/08/2024

IMAMUZ ZUHURI DA ABDULLAHI BIN UMAR
(Ya ganshi ko bai ganshi ba?! )

Malaman JARHI da TA'ADILI sun tabbatar da kasancewar Imam Ibn Shihab Az-zuhuriy da Sahabi Abdullahi bin Umar a zamani ɗaya, saboda an haifi Zuhuri a shekara ta 50 ko 51 ko 52, shi kuma Ibn Umar ya rasu a shekara ta 73. Ibnu Bukhair ya ce Zuhuri shekararsa 16 lokacin da Ibn Umar ya rasu (kenan an haifi Zuhuri a shekara ta 56 k**ar yadda ya tabbatar da hakan a tarjamar Zuhuri).

Bisa la'akari da abinda mu ka ambata a sama, kenan zai yiwu a ce an samu ɗayan abubuwan nan guda uku;
1. Zuhuri ya ga Ibnu Umar,
2. Zuhuri ya ga Ibnu Umar har ma (ya ji hadisi) ya yi riwaya daga wurinsa,
3. Bai ganshi ba, b***e ya yi riwaya a wurinsa (kenan an kore duka biyun can).

Akwai malamai da yawa da su ka ambaci cewar Zuhuri ya ga Ibnu Umar, amma bai yi riwaya a wurinsa ba, daga cikinsu akwai; Abu Hatim, Imamu Ahmad, Imamu Muslim da Abu Ahmad Al-hakim. Haka nan kuma Ibn Rushaid, Ibn Rajab da Ibn Abdilbar su na da ire-iren waɗannan riwayoyin na wannan ra'ayin.

Daga cikin malamai, akwai ma su fahimtar cewar Zuhuri ya ga Ibnu Umar, har ma ya yi riwaya daga wurinsa, daga cikin ma su irin wannan ra'ayin akwai; Ma'mar, Abdurrazzaƙ, Imamuz Zuhliy, Al-hulwaniy, Ibnul Madiniy, Imamul Ijliyyu da Abu Nu'aim. Al-imam Ibnul Hazza'a (Abu Abdillahi, Muhammad bin Yahya bin Ahmad, Al-ƙurɗubiy, Al-malikiy, mai rasuwa shekara ta 416) ya ce Zuhuri ya ruwaito hadisai guda biyu daga Ibnu Umar.

Nau'i na ƙarshe, shi ne ɓangaren ma su korewa duka (Imamuz Zuhuri bai ga Ibnu Umar ba, b***e ma har ya yi riwaya a wurinsa. Daga cikin ma su wannan ra'ayin akwai; Imamu Malik, Amru bin Dinar (waɗannan mutum biyun kuwa ba kowa ne ya kai su ba a cikin ɗaliban Zuhuri, musamman Imamu Malik, wanda yake ya fi kowa, k**ar yadda ya ke sanannen abu), Ibnu Ma'in, Uƙail bin Khalid, sai kuma Alhafiz Ibnu Hajar, shi ma ya na da maganganun da ke nuni zuwa ga irin wannan ra'ayin.

Allah ya gafartawa Imamuz Zuhuri da sauran malamanmu na hadisi.

Nau'i na ƙarshe, shi ne abinda babban malaminmu; Dr. Ahmad Ma'abid Abdulkarim - Allah ya ƙara masa lafiya - ya tafi a kai.

,
Helwan, Cairo, Egypt.
20th August, 2024M.

NA DAWO DAGA HUTUN DA NA TAFI. Alhamdulillah, k**ar yadda na sanar a ranar 13 ga watan July, cewa zan tafi hutu na wasu ...
09/08/2024

NA DAWO DAGA HUTUN DA NA TAFI.

Alhamdulillah, k**ar yadda na sanar a ranar 13 ga watan July, cewa zan tafi hutu na wasu kwanaki, na tafi hutun ne bisa wasu uzururruka, amma yanzu cikin iko da taimakon Allah na dawo.

Daga yau za'a cigaba da gani na insha'allah, zan cigaba da rubuce-rubuce daidai gwargwadon iko, iya yanda Allah ya sawwaƙe mani...

Ina roƙo da fatan ƴan'uwa za su taimaka wajen gyara da janyo hankali na a kan abinda na rubuta na kuskure, wanda bai dace ba, ko wanda ba daidai ba, ni kuma zan yi ƙoƙari wajen ganin na samar da abinda ya k**ata insha'allah.

Allah ya yi mana albarka ni da ku gaba ɗaya.
Allah ya bamu sa'a a karatuttukanmu, ya sa mu dace da alheri duniya da lahira.

Albany Dabai,
Helwan, Cairo.
9th August, 2024.

DARUSSAN RAMADHAN 1445AHMA SU GABATARWA:Musa Albany DabaiAbu Abdillah SharadaWURI:No. 14 Wadi Hof, Zahra Helwan, Cairo, ...
09/03/2024

DARUSSAN RAMADHAN 1445AH

MA SU GABATARWA:
Musa Albany Dabai
Abu Abdillah Sharada

WURI:
No. 14 Wadi Hof, Zahra Helwan, Cairo, Egypt.
https://www.facebook.com/albany.dabai1

LOKACI:
Ƙarfe tara na dare agogon Nigeria.

SIYASAR DABAI WARD!!!A tsari na dimokraɗiyya, yin adawa halattacccen abu ne. Amma ya na da kyau mutanenmu su sani, tun d...
27/02/2024

SIYASAR DABAI WARD!!!

A tsari na dimokraɗiyya, yin adawa halattacccen abu ne. Amma ya na da kyau mutanenmu su sani, tun da dai har kashi casa'in da tara da ɗigo tara cikin ɗari (99.9%) na yan asalin mutanen Dabai musulmai ne, to ya na da kyau mu riƙa kallon maslahar musulunci da al'ummarmu a lokacin yin adawar siyasa. Sannan kuma mu riƙa duba zumuntar da ke tsakaninmu, domin sama da kaso tamanin cikin ɗari (80%+) na mutanen garin duk yan'uwan juna ne.

Ga waɗansu abubuwa da ya k**ata mu karanta, la'alla za mu amfana:

1. Mutunci: dole ne mu yi ƙoƙarin tsarewa kowa mutuncinsa, musamman kasancewar duk wanda ka nemi taɓa masa mutuncin, zai yi wahala a ce ba ku da alaƙa ta ƴan'uwantaka ta kusa kai da shi, in ma ta gefen iyayenku maza ko mata. Taɓa ma sa mutuncinsa k**ar taɓa mutuncin iyayen kanka da kanka ne, tun da kusan duk asalin ɗaya ne. Kuma a addini hakan haramun ne. Haka nan ma a siyasance ba na tsammanin hakan ya halatta.

2. Kasancewa ƴan gari ɗaya: Allah cikin ikonsa, sai ya ba mu mutane ma su muƙamin siyasa mabanbanta yan cikin garin namu, mu tambayi kawunanmu: shin murna da farin ciki ya k**ata mu yi ko bakƙn ciki da jin zafi a rai? Godewa Allah ya k**ata mu yi ta hanyar yin abinda ya k**ata (k**ar yin ƙoƙarin haɗa kawunan ƴan siyasar da mu kanmu mabiyansu da yaransu) ko kuma butulcewa Allah ya k**ata mu yi ta hanyar yin abinda duk mai hankali ya san yin wannan abin haramun ne a musulunce (k**ar cin mutuncin juna da cin duduniya da ƙarya da sharri da ƙazafi da ƙage)?

3. Haɗin kai: ya k**ata manyanmu a siyasance da ke garin Dabai su ji tsoron Allah su yi ƙoƙarin haɗa kai a tsakanin junansu, sannan kuma su yi kokarin daidaita mabiyansu wurin ganin ana yin abinda zai ciyar da garin na mu gaba. Ba a ce dole sai ka yi jam'iyyar wani ba, kuma ba a ce sai ka so gwanin wani ba, kowa na da na sa gwanin, amma ba bu in da aka ce ka yi abinda zai kawo rabuwar kai ko a siyasance.

4. Rubutu a social media: ma su yin rubutun siyasar da ta shafi Dabai ko ƴan Dabai, ku ji tsoron Allah ku san me za ku riƙa rubutawa, wallahil azeem, akwai yiwuwar za a bijiro ma ku da abinda ku ke rubutawa a lahira a tambayeku akai ku yi bayani, me za ku faɗawa Allah?

5. Sanya ido daga manya da mahukunta: wajibi ne ma su riƙe da muƙamai (su ko yaransu da su ka wakilta a harkar media) su riƙa kulawa da yanayin yadda mabiyansu ke yin rubuce-rubuce. Ku ma fa Allah zai tambaye ku a kan wannan rubutun da ake yi da sunanku; in an yi ƙarya a abinda ba ku yi ba, ko an yi sharri da ƙazafi da ƙage, ku yi ƙoƙarin saita lamuran (duk da na ga ana ɗan yin ƙoƙari ba laifi).

6. Ku zama ma su yin siyasa domin al'umma da kuma manufa mai kyau.

7. Ku riƙa ƙoƙarin kwatanta adalci da daidaito a tsakanin ra'ayoyin jama'a.

8. Misali: ban so in k**a sunan kowa ba a rubutu na, amma ya k**ata in ambaci sunan mutum biyu; Anas Jobe Aliyu da Abubakar Rabi'u Dabo Dabai, waɗannan ƙannen nawa, ina yaba masu ƙwarai wurin yadda su ke mu'amala da waɗanda ba sa tare a siyasance. Allah ya ƙara masu tabbatuwa a kan haka. Kuma ya k**ata su zama abin koyi ga kowa.

9. Ya k**ata a riƙa kai zuciya nesa a lokacin yin rubutu a social media, musamman ma su yin comments. Ya k**ata ku san cewa ba fa iya ku kaɗai ku ke cin karenku ba bu babbaka ba! Akwai dubban mutanen da ba ku yi tsammani ba su na karanta rubutunku. Kuma sannan ga Mala'iku nan a gefe su na naɗar abinda ku ke tattaunawa.

10. Neman kujera a tenuwa ta gaba: ya k**ata mutanenmu su maida hankali ne wurin ganin an yi mana ayyukan raya ƙasa da taimakon mabuƙata, ba wai maida hankali wurin ganin wane zai yi tazarce ko ba zai ba, wane zai canza kujera ya tafi ta gabanta ko kuwa ba zai je ba?! Duk wannan abinda mutum ya shuka da kuma lokaci su ne za su zama alkalai a nan gaba.

11. Ina ma na addu'ar samun dacewa da wakilci na gari daga wakilanmu, kuma ina addu'ar Allah ya ƙara karkato da hankulansu gare mu domin yi mana ababen da su ka dace ba ababen da za su bunƙasa ma su tattalin arziƙinsu ba!

12. Allah ya ba su ladan wannan aiki da su ke yi mana ba dare ba rana. Allah ya sanya ma su a mizani. Allah ya karawa rayuwarmu da ta su albarka gaba ɗaya, amin.

,
Cairo, Egypt.
27th Feb., 2024.

TAFIYA SUJUDA; DA HANNU KO DA GUIWA?! //01GabatarwaBismillah, alhamdulillah, was-salatu was-salamu ala rasulillah...Amma...
27/11/2023

TAFIYA SUJUDA; DA HANNU KO DA GUIWA?! //01

Gabatarwa
Bismillah, alhamdulillah, was-salatu was-salamu ala rasulillah...

Amma ba'ad;
Akwai hadisai guda biyu da su ka yi magana game da kaifiyyar yadda ya k**ata a tafi sujuda a sallah. Hadisin farko shi ne hadisin sahabi Abu Huraira - radiyallahu anhu - wanda ya ke magana a kan za a tafi sujuda da hannayenmu. Hadisi na biyu kuma shi ne hadisin sahabi Wa'il bin Hujr - radiyallahu anhu - wanda ya ke magana a kan za a tafi sujuda da guiwowi ko guyawu.

Mutane da yawa sun samu saɓani (a cikinsu har da malamai manya; na da, da na yanzu) game da siffar yadda za a tafi sujudar, shin da hannaye za a tafi ko kuwa da guyawu?!

Daga cikin abubuwan da zan kawo a wannan rubutun su ne:

1. Nassin hadisan guda biyu.

2. Takhriji, wanda zai yi magana game da malaman da s**a fitar da hadisan, gwargwadon bincike da nazari na.

3. Maganganun da malamai su ka yi (na inganci ko akasin haka game da hadisan) tare da yin bayanin yadda isnadan hadisan suke, domin tabbatar da inganci ko akasin haka a cikin isnadan da matanin hadisan.

4. Hadisan da suke shawahid (wato waɗanda su ke shaida) ne ga waɗancan hadisan guda biyu, tare da kawo matsayin kowanne daga cikin su ta fuskar inganci ko akasin hakan, kuma hakan zai tabbata ne ta hanyar ambaton waɗanda s**a fitar da hadisan.

5. Wasu daga cikin ra'ayoyin (wasu) malamai game da abinda ya k**ata mutum ya riƙa cikin abubuwa guda uku; shin da hannayen za a tafi ko kuwa da guyawun, ko kuma duk wanda mutum ya yi, ya yi daidai?

6. Matsaya ta da fahimta ta game da abinda ya k**ata a yi.

7. Rufewa da addu'a.

Allah ya sa mu dace da alheri, Allah ya k**a mana ya ba mu ikon yin daidai ya hana mu yin kurakurai. Allah ya amfanar da mu gaba ɗaya, amin.

,
Helwan, Egypt.
27th Nov., 2023.

ADDU'A RANAR LARABA, TSKANIN AZAHAR DA LA'ASAR!Akwai wani hadisi da Imam Ahmad ya ruwaito a Musnad ɗin sa (14,563), Imam...
17/05/2023

ADDU'A RANAR LARABA, TSKANIN AZAHAR DA LA'ASAR!

Akwai wani hadisi da Imam Ahmad ya ruwaito a Musnad ɗin sa (14,563), Imamul Baihaqiy ya ruwaito a cikin Shu'abul Iman (3874) sai Imamul Bazzar shima ya ruwaito hadisin k**ar yadda yazo a cikin Kashful Astar (431)...

Sheikh Muhammad Nasiruddeen Albaniy ya hassana hadisin a cikin Sahi'hul Adabul Mufrad (704) daga Sahabi Jabir bn Abdullahi - radiyallahu anhu -.

Hadisin yana nuna mana cewar idan wani muhimmin abu ya samu mutum, babu laifi zai iya yin kirdadon wannan lokacin ya yi addu'a, ana fata da sa-ran a amsa masa (musamman ma in ace dama ya kwana biyu yana yin addu'ar).

Ina ƴan'uwa na ɗaliban hadisi, da kuma Malaman mu, me za ku ce game da wannan hadisin; ta fuskar hukunci da kuma sharhin sa gwargwadon iko?! Ina da wasu muhimman addu'o'i da nake so in yi, yau Laraba.

Allah ya bada lada yasa albarka yasa a mizani.
Allah ya amsa mana addu'o'in mu na alheri, ya tsare mu daga dukkan sharrin mutane da Aljanu.

,
Helwan, Egypt.
17/05/2023.

Address

No 14 Zahra Street
Helwan

Telephone

+2348069123479

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Musa Albany Dabai posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Musa Albany Dabai:

Share

Category