Baye Barhama Inyass

Baye Barhama Inyass FAIRA IBRAHIMIYYA MUHAMMADIYYA

20/07/2025

MAGANI A GONAR YARO.!
:
:
ZAN TABBATAR MAKA DA LALLAI MANZON
ALLAH (SAW) SHINE FARKON "MU'ASSASIN"
DARIKA"
Zan Riskar Dakai, Amsan Tamboyin Ka Cikin
Kur'ani Da Hadisi Kamar Yadda Ka Buqata,
Idan Har Ka Bini A Tsanake.
:
:
GA CHALLANGE, GAMI DA TAMBAYAR DA WANI
BAWAN ALLAH, YAYI MIN COMMENT DA SU
KAMAR HAKA.
Shafi'u Sani
Dukwanda yamutu abatijjane ba
amusulmiba tabbas yayi hasara, Allah yace
(WALATAMUTUNNA ILLAH WAANTUM
MUSLIMUN) kuma wai don Allah, wacce
dariqa annabi da sahabbansa s**ayine?
Shin tijjaniyya s**ayi? ko kadiriyya ko
ahmadiyya ko shazaliyya ko
naqashebandiyya ko arusiyya ko burhaniyya
s**ayi? shin mawai, cikin wayannan dariqu
waccece annabi yazabama alummarsa yace
sushiga? DON ALLAH MALAN KAAMSAMIN
TAMBAYOYINNAN KURANI DA HADIS. Like ·

ALHAMDULILLAH.
* Amsar Tambayar Ka Bisa Qalubalen Ka Na
Farko Karkashin Wannan Aya 102 A Ali
Imrana.
ﻭَﻟَﺎ ﺗَﻤُﻮﺗُﻦَّ ﺇِﻟَّﺎ ﻭَﺃَﻧْﺘُﻢْ ﻣُﺴْﻠِﻤُﻮﻥَ
* Ai Kasani, Ba Yadda Mutum Zai Zamo,
Batijjane, Har Sai Ya Kasance Cikekken
Musulmi, Mai Cikekkiyar Sallamawa ALLAH
(Swt),
Sannan Ba Ta Yadda Mutum Zai Kasance Mai
Sallamawa ALLAH Har Sai Ya Kasance Mai
Riko Da Bibyar Sharuddan Muqaman Addinin
ALLAH Guda 3.
A Muqamul Islam, Tijjanawa, Sun Kadaita
ALLAH Bisa Haqiqar Kadaitawa (Tauhidi),
Sannan Duk Abinda Yazo Na Ibadu Cikinta,
Kamar Sallah, Azumi Zakka, Aikin Hajji To
Sunayi Shin Aikin Wanne Addini Ne Wannan?
Sannan Kuma, A Mukamul Imani, Tijjanawa
Sunyi Imani Da Sharuddan Ta Guda Shida
Shin Aikin Wanne Addini Ne Wannan?.
* Muqamul Ihasan Kuwa, Wannan Dama
Sansanin 'Yan Gatace, Anan Yan Darika S**ai
Sansani, Kuma Anan S**a Tare.
* IDAN BA TIJJANE YA MUTU A WANNAN
TAFARKI, SHIN BAI KASANCE MUSULMI BA.?
Amsar Tambaya Ta Biyu.
Kafin Kayi Wannan Tambaya Akan Me Yasa
ANNABI (SAW) Da Sahabban Sa, Basuyi Daya
Daga Darikun Da Ka Zayyano Ba, To Ya
Kyautu, Kasoma Tambayar Kanka Cewa.
* Shin Me Yasa ANNABI (SAW) Da Sahabban
Sa, Basubi Mazhabobi Ba, Kamar Malikiyya,
Shafi'iyya, Hambaliyya, Hanafiyyy

19/07/2025

Kula Da Charbinku📿

Yanzu Muna Zamanin Fashin Imani, Idan Kayi Sake Da Wasa Sai Ayi Maka Choge.

Shi Kadai Ne, Babu Waninsa Ko Mujaddadinsa.
GAYATUL-MURAD, MUNTAHAL-MUQAMATI.

Ya Sheikhu Ibrahimu INYASS 🥰
نفسي ماتت فيكم
Wal abdu Shehu Bafulatani mungode Allah yakara Lafiya Da Nisan kwana 🤲

SHEHU ALFULATY Fardun Nee ☝️☝️

19/07/2025

An haifi Marigayi Shehu Abubakar Atiku Sanka dan Halliru dan Abubakar dan Musa (Mairisala) a garin Katsina a shekarar 1896. Mahaifinsa Malam Halliru da kakansa malam Abubakar duk haifaffun Katsina ne. Amma mahaifin kakansa Mallam Musa (Mairisala) ya zo ne daga kasar Tunis shi da jama’arsa; shi ya sa a ke ce mu su Rumawa. Dalilin kiran sa da Mairisala kuwa shi ne malamin fikhu na farko da ya kawo littafin Risala kasar Hausa lokacin da ya je aikin Hajji ya gamu da ‘yan’uwansa Larabawan kasar Tunis sai ya fansheta daga wajensu ya taho da ita kasar Hausa ya kuma yada ta.

Shehu Abubakar Atiku ya girma a hannun ‘yar’uwar kakarsa mai suna Rahmatu (Yaya Babba) matar malam Abba Dan Fannah a Dandalin Turawa da ke Kano. Ta dalilin kulawarta ne har yay i karatun alkur’ani a hannun mijinta. An shaidi Rahmatu da mace ce mai ibada da tsananin da rikon addini. Jajirtacciya mai bin tafarkin darikar Tijjaniya sau da kafa. Sannan mai zartaccen Imani cikin Shehu Ahmadu Tijjani. Ita ce ta tsaya tsayin daka a tarbiyyarsa har zuwa lokacin da Allah ya yi mata rasuwa a shekarar 1972.

Shehu Atiku ya fara da karatun al-kur’ani a hannun mijin kakarsa Malam Abba Dan Fanna haka ya yi ahalari da kurdabi da alburda da Badamasi duk a wajensa. Daga nan sai ya koma da karatu a wajen Shaihu Muhammadu Salga dan Alhaji Umaru inda ya karanci risala da Iziyya da arshada ta ibn Rushidi da Mukhtasarul Khalil har zuwa babin aure, ya kuma karanta littattafan akida kamar su Mukaddamatul Burhamiyya ta Imamu Sunusi da Akidatul wusda da sauransu. Ya karanci littatafan darika kamar su Su’al wal jawab na shehu Muhammadu Salga da Yakutul faridah na shehu Nazifi. Ya ci gaba da neman ilimi a fannoni da dama kamar tafsiri da Hadisi da harshen Larabci inda ya karanci littattafan Alfiyya ta dan Malik da Ajrumiyya da Mulhatul I’irab da sauransu.

Shehu Atiku ya zurfafa iliminsa da nean ilmai a fannonin fikhun darika da tasawwuf da sauran fannonin harshen Larabci a wajen Shehu Abubakar Mijinyawa Bakin ruwa. Ya karanta littafai kamar haka a gun Shehu Mijinyawa kamar su Jawahirul ma’any da Durratul Kharidah ( Sarhin Yakutatul Faridah) da Bugyatul mustafida na shehu Arabi da Alfiyatul tasawwuf ta shehu Mustapha da sauran littattafai da dama

Shehu Atuku Sanka ya karbi darikar Tijjaniya a hannun Shehu Muhammadu Sanka a shekarar 1916. Sannan ya yi tarbiyyar Ruhi a hannun Shehu Abubakar mijinyawa.

Shehu Atiku na Shehu bai tsaya a karatun littattafai ba, a’a har da harshen Larabci saboda shi ne harshen da malamai kan yi muhawara da shi a tsakaninsu a garin Kano a wancan lokacin. Ya karanta ilimin hisabi a wajen Muhammadu dan Ajurum da Mulhatul-irab ta Imamu Hariri mai littafin mukamah da sauran littattafan da s**a shafi adabi da lugga (Harshe) da kuma ka’idojin Larabci.

Shehu Atiku na daya daga cikin manyan shaihunnan malamai na garin Kano da ma Afrika baki daya wanda tarihi ba zai taba mantawa da sunansa da gudummawarsa musamman a garin Kano da Najeriya da ma Afrika baki daya. Shehi Atiku ya kasance Shaihin darika wadda ya yi mata hidima jini da tsoka da tunaninda da lokacinsa da ruhinsa. Shehu Atiku ya wallafa litttattafai da daman gaske wadanda a kiyasi ana da tabbacin sun haura casa’in tun daga na rubutun zube da rubutattun wakoki wanda ma fi yawa suna Magana ne a kan al’amuran addini da harshen larabci da kuma sufanci. A takaice rubuce-rubucensa sun kasu gida uku wato Sufanci da Adabi da kuma Fikhu.

Babu shakka Shehu Atiku ya yi gagarumin kokarin da ba za a raina ba dangane da rubuce-rubucensa litattafai ya kuma tsara wakoki a harshen Hausa da Larabci a kan abubuwa daban-daban. Misali ya rubuta wakoki na:

Yabon Annabi SAW

Yabon Shehi Tijjani

Yabon Shehi Ibrahim Inyass

Wa’azi da gargadi

Akida

Ibada

Da sauransu

Daga cikin wakokinsa akwai

8-Wakar amsar mai tambaya a cikin ma’aloli da yawa.

-Tusamma

-Taimakon Dakiki

-Asma’u zatil jamali

-Matserar mata

-Nasiha ga ‘yan’uwa

-Yabon fiyayyen halitta

-Arzikin masoya

-Tarihin kwaki

-Begen Muhammadu

-Rakada’u

Shehu Atiku Sanka yana da madaukakiyar daraja a wajen malaman zamaninsa musamman ta bangarorin ilimai daban-daban tare da karfin hujja da kwarewa wajen bincike da gogewa wajen hujja da fasahar zance. Kuma ya nutse a cikin ilimin sanin darikar Tijjaniyya hakan ta sanya ya himmatu da darussan ta da bincike a kanta har sai da ya zamana ba shi da wanda za a kwatanta shi da shi a wannan fanni.

Shehi Atiku malami ne da har a karshen rayuwarsa yana neman sani, mai hakuri da rashin gazawa da kyauta da daukar nauyi. Gidansa ya zama sansani na neman sani inda almajirai ke zuwa daga ko’ina a fadin kasar nan har da Nijar.

Daga cikin Almajiransa akwai:-

Shehu Balarabe Jega

Shehu Ibrahim Alti Funtua

Shehu Ahmad Abulfathi Maiduguri

Shehu Muhammadu Jibiya

Shehu Yahya Jibiya

Shehu Muhammadu Birnin magaji

Shehu Ibrahim Kaya

Shehu Adamu Katibi

Shehu Imrana Damari

Allah ya yi wa Shehi Atiku rasuwa ranar laraba 9 ga watan rabi-ul thani 1394 Hijiriyya. Yana dan shekaru 64 an binne shi a makabartar Gwauron Dutse

19/07/2025

An haifi Marigayi Shehu Abubakar Atiku Sanka dan Halliru dan Abubakar dan Musa (Mairisala) a garin Katsina a shekarar 1896. Mahaifinsa Malam Halliru da kakansa malam Abubakar duk haifaffun Katsina ne. Amma mahaifin kakansa Mallam Musa (Mairisala) ya zo ne daga kasar Tunis shi da jama’arsa; shi ya sa a ke ce mu su Rumawa. Dalilin kiran sa da Mairisala kuwa shi ne malamin fikhu na farko da ya kawo littafin Risala kasar Hausa lokacin da ya je aikin Hajji ya gamu da ‘yan’uwansa Larabawan kasar Tunis sai ya fansheta daga wajensu ya taho da ita kasar Hausa ya kuma yada ta.

Shehu Abubakar Atiku ya girma a hannun ‘yar’uwar kakarsa mai suna Rahmatu (Yaya Babba) matar malam Abba Dan Fannah a Dandalin Turawa da ke Kano. Ta dalilin kulawarta ne har yay i karatun alkur’ani a hannun mijinta. An shaidi Rahmatu da mace ce mai ibada da tsananin da rikon addini. Jajirtacciya mai bin tafarkin darikar Tijjaniya sau da kafa. Sannan mai zartaccen Imani cikin Shehu Ahmadu Tijjani. Ita ce ta tsaya tsayin daka a tarbiyyarsa har zuwa lokacin da Allah ya yi mata rasuwa a shekarar 1972.

Shehu Atiku ya fara da karatun al-kur’ani a hannun mijin kakarsa Malam Abba Dan Fanna haka ya yi ahalari da kurdabi da alburda da Badamasi duk a wajensa. Daga nan sai ya koma da karatu a wajen Shaihu Muhammadu Salga dan Alhaji Umaru inda ya karanci risala da Iziyya da arshada ta ibn Rushidi da Mukhtasarul Khalil har zuwa babin aure, ya kuma karanta littattafan akida kamar su Mukaddamatul Burhamiyya ta Imamu Sunusi da Akidatul wusda da sauransu. Ya karanci littatafan darika kamar su Su’al wal jawab na shehu Muhammadu Salga da Yakutul faridah na shehu Nazifi. Ya ci gaba da neman ilimi a fannoni da dama kamar tafsiri da Hadisi da harshen Larabci inda ya karanci littattafan Alfiyya ta dan Malik da Ajrumiyya da Mulhatul I’irab da sauransu.

Shehu Atiku ya zurfafa iliminsa da nean ilmai a fannonin fikhun darika da tasawwuf da sauran fannonin harshen Larabci a wajen Shehu Abubakar Mijinyawa Bakin ruwa.

19/07/2025

Daga Lokacin da ka fara yiwa ANNABI ﷺ kallon Mutum kamar kowa 🤔to daga Wannan Lokacin ka fada Rami!!!

Allah ya bamu ikon yin biyayya ga Allah da Annabin sa,

06/07/2025
26/01/2025

Un grand merci à mes nouveaux followers ! Adamu Abu, Umar Barhama

Adresse

Rn
Niamey

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Baye Barhama Inyass publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Partager