Gaskiya online

Gaskiya online Wannan shafin mun budashi ne domin kawo muku muhimman labarai na gaskiya masu asali da kuma tushe.

Jana’izar BuhariAn yi jana’izar tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, a ranar 15 ga Yuli, a garin Daura, jihar Katsina...
16/07/2025

Jana’izar Buhari

An yi jana’izar tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, a ranar 15 ga Yuli, a garin Daura, jihar Katsina, tare da girmamawa ta musamman – har da 21-gun salute. Shugaba Tinubu ya ayyana kwanakin makoki bakwai ga ƙasar. Buhari ya rasu a London yana da shekaru 82.

Gaskiya online

Harbin Mutane 20 a PlateauA garin Tahoss, a ƙaramar hukumar Riyom, jihar Plateau, akalla mutane 20 sun rasa rayukansu ba...
16/07/2025

Harbin Mutane 20 a Plateau

A garin Tahoss, a ƙaramar hukumar Riyom, jihar Plateau, akalla mutane 20 sun rasa rayukansu bayan wani mummunan harin makami da wuka da bindiga da aka kai a daren Talata. An ƙone gidaje da dama, kuma bidiyo da hotuna s**a nuna girman barna. Wannan lamari ya sake tada damuwa dangane da rikicin makiyaya da manoma a yankin.

Gaskiya online

Donald Trump da Yaƙin UkraineTsohon Shugaban Amurka Donald Trump ya ce an fara aikawa da mak**ai zuwa Ukraine. Ya kuma y...
16/07/2025

Donald Trump da Yaƙin Ukraine

Tsohon Shugaban Amurka Donald Trump ya ce an fara aikawa da mak**ai zuwa Ukraine. Ya kuma yi barazanar saka manyan haraji akan Rasha idan ba a samu zaman lafiya cikin kwanaki 50 ba.

A gefe guda, Rasha ta kwace wani gari mai suna Novokhatske a Donetsk, kuma an kai hari da jiragen drone akan wata masana’anta a Ukraine da ake dangantawa da Poland

Gaskiya online

Muna chan muna mining wasu project damu kammu munsan ba zasu fashe ba, mun bar dahir, a gaskiya a wannan lokacin ba wani...
01/09/2024

Muna chan muna mining wasu project damu kammu munsan ba zasu fashe ba, mun bar dahir, a gaskiya a wannan lokacin ba wani project damuke mining da yakai project din usecase point ne suke basuwa duk bayan 6 hours ake claiming, sannan har an fara connecting din wallet, Wanda Bai faraba yafara Wanda yafara ya maida hankali agurin claiming.

https://t.me/cryptorank_app_bot/points?startapp=ref_1334595389_

Saifullahi Bello

Ba ruwanmu da wata odar Kotu kawai mun tura Sojoji kano ne domin Shirin ko ta kwana ga masu son tayar da tarzoma ~Rundun...
27/05/2024

Ba ruwanmu da wata odar Kotu kawai mun tura Sojoji kano ne domin Shirin ko ta kwana ga masu son tayar da tarzoma ~Rundunar Sojan Nageriya.

Rundunar sojan Nageriya a wata sanarwa da ya fitar a daren Lahadi, Manjo Janar Onyema Nwachukwu, Daraktan hulda da jama’a na rundunar, ya ce rundunar ba ta da hannu a rikicin masarautar.

“Sabanin zarge-zargen da kungiyar lauyoyin Najeriya reshen jihar Kano ta yi k**ar yadda aka buga a ranar 26 ga Mayu 2024, sojojin Najeriya ba su da hannu a rikicin masarautar Kano kuma ba su da hannu wajen aiwatar da duk wani umarnin kotu. Sun dauki matakin ne kawai don duba duk wata matsala ko zagon kasa da za a iya samu a rikicin masarautar Kano.”

“Batun da ya fi daukar hankalin Sojojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro shi ne hana tabarbarewar doka da oda a jihar, wanda wasu masu adawa da gwamnati ba sa iya cin moriyar su. Sojoji za su shiga cikin gaggawa lokacin da ya bayyana cewa tsananin yanayin tsaro ya mamaye 'yan sanda.

“Duk abin da Sojoji ke yi a wannan mataki shi ne sanya ido kan lamarin da kuma kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana idan lamarin ya ta’azzara da zai kawo barazana ga tsaron jihar da ma yankin baki daya.

DA DUMI-DUMI: Kwamishinan 'yan sandan jihar Kano, Mohammed Usaini Gumel, ya ce gwamna Abba Kabir Yusuf ya daidaita rikic...
27/05/2024

DA DUMI-DUMI: Kwamishinan 'yan sandan jihar Kano, Mohammed Usaini Gumel, ya ce gwamna Abba Kabir Yusuf ya daidaita rikicin sarauta a jihar.

Ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da aka gudanar a gidan gwamnati dake Kano a daren yau Lahadi.

Da yake bayyana irin rawar da ‘yan sanda s**a taka a rikicin masarautar Gumel ya ce ‘yan sanda za su tabbatar da doka.

Ya kuma ce jami’an tsaro sun bankado wani shiri na tayar da kayar baya a jihar yayin da suke kokarin kai hari a wasu wurare ciki har da majalisar dokoki.

Gumel wanda tun da farko ya gargadi masu tayar da kayar baya da su kaucewa rikicin, ya sha alwashin cewa dogon hannun da doka ta tanada zai k**a duk wanda ya gwada taka kudirin jami’an tsaro.

A jawabin a ya ce, “A yau, mun zo nan ne domin mu yi muku jawabi kan wani muhimmin batu da ke da alaka da matsalar tsaro a jihar da ku da mu baki daya muke tafiyar da shi tare tun lokacin da aka fara batun sarauta a jihar.

“Mun samu sahihan bayanai game da ‘yan bata-gari da ke kokarin tayar da ta’addanci a wurare, musamman majalisar dokoki da sauran muhimman wurare a cikin jihar. Majiyoyi da yawa sun tabbatar da shi.

“Duk wanda ke son gwadawa ya sani jami’an tsaro na da karfin da za su iya tunkarar ta’addancin. Mun kammala shirye-shiryen fara sintiri sosai da gano wuraren da aka sanar da mu cewa bata garin na boye.

“Za mu shiga neman su gida-gida; duk wanda yake ganin ya fi karfin doka to ya gwada. Kano za ta zauna lafiya kuma babu wanda zai iya soke hukuncin.

“Batun harkokin sarauta ya cika ta bangaren zartarwa na gwamnati. Muna tsayawa kan doka kuma za mu aiwatar da dokar da ake da ita."

Ya ci gaba da cewa, an hada kungiyoyi daban-daban ana biyansu kudade domin kai hare-hare da kuma kawo cikas ga zaman lafiya.

Babu wanda ya fi karfin bin doka komai girmansa, don haka Gwamna Abba yabi umurnin kotu, Inji Sheikh Dahiru Bauchi. Shei...
26/05/2024

Babu wanda ya fi karfin bin doka komai girmansa, don haka Gwamna Abba yabi umurnin kotu, Inji Sheikh Dahiru Bauchi.

Sheikh Dahiru Bauchi, ya kuma tunatar da gwamnan Kano, Abba Yusuf cewa shi ma ya tabbata a kan kujerar gwamna ne saboda hukuncin kotu.

Sheihin ya kara da cewa "Babu wanda ya fi karfin doka komai girmansa, don haka akwai bukatar gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da zaman lafiya da adalci a jihar tare da kaucewa abin da zai haifar da rikici.

“Tunda kotu ta shiga tsakani, to akwai bukatar kowane bangare ya mutunta doka domin zaman lafiya.

"Ba daidai ba ne gwamnatin jihar Kano ta yi gaban kanta ta nada sabon Sarkin Kano, tare da tube sarakunan jihar biyar duk da umarnin kotu”.

Sheikh Dahiru Bauchi ya yi magana ne ta bakin shugaban gidauniyar Dahiru Bauchi, Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi a wani taron manema labarai a Bauchi ranar Lahadi.

✍️ Comr Abba Sani Pantami

SUBAHANALLAH Wanan bawan Allah Sunansa Salim Aminu Anamasa lakabi da (S baki)   A shiyar mabera  dakenan Birnin Sokoto W...
26/05/2024

SUBAHANALLAH

Wanan bawan Allah Sunansa Salim Aminu Anamasa lakabi da (S baki) A shiyar mabera dakenan Birnin Sokoto

Wasu da ba'asan ko suwayeba sun dauke wanan bawan Allah A hanyarsa ta dawowa daga makarantar (University)

Labarin da munkasamu kafin su dauki salim Sun sha Kiran mahaifinsa sunyi alwashin saceshi dashi da kanwarshi wada hakan tasa har s**a daina zuwa makaranta dashi da kanwarshi.

Daga baya salim ya koma Makaranta yakanji a boye Amma duk da haka saida Sunka daukeshi

To ayanzu ance sunkira mahaifin salim inda yabukaci safadi ko nawa suke nema zai basu Sunyi ikirarin cewa rayuwar salim kawai suke so

Kafin wananma akwanakin baya awa salim want duka Wanda saida s**ajimasa a wuya wadda ake zargin sune s**a aika tamasa hakan

Muna Rokon Allah shi ko6utarda salim daga hanunsu

Tinubu ya naɗa Olayemi Cardoso a matsayin sabon gwamnan CBNShugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana sunan Dr. Ola...
15/09/2023

Tinubu ya naɗa Olayemi Cardoso a matsayin sabon gwamnan CBN

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana sunan Dr. Olayemi Michael Cardoso a matsayin sabon gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) na tsawon shekara biyar, da zarar Majalisar Dattijan ƙasar ta amince da shi.

Wannan bayani na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale ya fitar, yau Juma'a.

Bayanin ya ce shugaban ƙasar ya ɗauki matakin ne bisa dogaro da sashe na 8 (1) na dokar Babban Bankin Najeriya ta 2007, wadda ta bai wa shugaban ƙasar karfin ikon naɗa shugaba da mataimaka huɗu na Babban Bankin.

Sanarwar ta kuma bayyana sunayen wasu mutane huɗu da shugaban ya amince da su domin naɗawa a matsayin mataimakan gwamnan babban bankin na Najeriya.

Mataimakan su ne:

(1) Mrs. Emem Nnana Usoro

(2) Mr. Muhammad Sani Abdullahi Dattijo

(3) Mr. Philip Ikeazor

(4) Dr. Bala M. Bello

Shugaban ya buƙaci waɗanda aka naɗan su mayar da hankali wajen aiwatar da muhimman sauye-sauyen da aka ɓullo da su a bankin a ƙoƙarin gwamnatinsa na sake fasalin tattalin arziƙin ƙasar.

A watan Yunin wannan shekara ne shugaban ƙasar ya dakatar da gwamnan babban bankin ƙasar, Godwin Emefiele.

Wata sanarwa da ta fito daga ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayyar ƙasar ta ce an dakatar da Emefiele ne ne domin gudanar da bincike da kuma kasancewa wani ɓangare na ƙoƙarin sauya fasalin harkokin kuɗi a ƙasar.

Kwanaki kaɗan bayan dakatar da shi ne rundunar tsaron ciki ta ƙasar, DSS ta tabbatar da k**awa tare da tsare tsohon gwamnan babban bankin.

DSS ɗin ta kuma gurfanar da Emefiele a gaban kotu bisa tuhumar sa da laifuka daban-daban.

Kai Tsaye: Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Shari'ar Zaben Shugaban Kasar 2023A yau Laraba, 6 ga Satumba, 2023, za a yanke h...
06/09/2023

Kai Tsaye: Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Shari'ar Zaben Shugaban Kasar 2023

A yau Laraba, 6 ga Satumba, 2023, za a yanke hukunci a kan karar shugaban kasa da 'yan takaran PDP, LP da APM su ka shigar.

Atiku Abubakar da Peter Obi ba su yarda da nasarar da Bola Tinubu ya samu ba, su na kalubalantar jam'iyyar APC da INEC a kotu.

Za a haska zaman kotun a gidajen talabijin kasar nan, kuma an ji cewa ba a bukatar ganin kowa sai wadanda aka tantance shi.

Za mu rika kawo rahoto kai-tsaye a kan yadda abubuwa su ke faruwa a kotun na Abuja.

Shugaban Bola Tinubu ya umarci bankin CBN da jami'an tsaro su kwato kudaden lamunin noma da 'yan Najeriya su ka handame....
05/09/2023

Shugaban Bola Tinubu ya umarci bankin CBN da jami'an tsaro su kwato kudaden lamunin noma da 'yan Najeriya su ka handame.

Wannan na zuwa ne bayan binciko biliyoyin Nairori da wadanda ke kiran kansu manoma su ka cinye.

Kungiyar Manoma a Najeriya (AFAN) ta ce tabbas samo kudaden zai yi wahala saboda mafi yawan wadanda su ka ci ba manoman gaskiya ba ne.

Najeriya na nazarin shiga ƙungiyar G-20Gwamnatin Najeriya ta ce tana nazarin aika buƙatarta ta shiga ƙungiyar ƙasashe 20...
03/09/2023

Najeriya na nazarin shiga ƙungiyar G-20

Gwamnatin Najeriya ta ce tana nazarin aika buƙatarta ta shiga ƙungiyar ƙasashe 20 masu ƙarfin tattalin arzikin duniya, ake yi laƙabi da G-20.

Mai magana da yawun shugaban ƙasar Ajuri Ngelale, ya ce gwamnati na auna alfanu ko kuma kasadar da ke tattare da zama mambar a ƙungiyar.

A ranar litinin ne shugaban ƙasar Bola Tinubu zai tafi birnin Delhi domin halartar taron ƙungiyar bisa gayyata ta musamman da firaministan Indiya Narendra Modi ya yi masa.

Gwamnatin Najeriya ta ɓullo da matakai na farfado da tattalin arzikin ƙasar da ƙarfafa zuba jari amma kuma ƙasar na fama da hauhawar farashin kayayyaki da basuss**a da rashin ingancin kayayyakin more rayuwa.

A halin yanzu Afirka ta Kudu ce kaɗai daga Afirka ta samu zama mamba ƙungiyar ta G20.

Adresse

Ogunia

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Gaskiya online publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Partager