27/08/2026
Am0rk@ na ci gaba da tura 'Yan aike domin shawo kan lran.
Game da ziyarar Ministan Harkokin Wajen Qatar zuwa Iran a daidai wannan lokaci.
Abin da ake gani a yanzu shi ne, Amurka ba ta son dakatar da yaƙin ko cimma wata yarjejeniyar ƙarshe da lɍ@ñ hair sai an cika wasu sharudda da s**a yi daidai da muradun ƙasar Ɗanyahoo. A lokaci guda kuma, Tuɍ0m yana cikin matsin lamba: a gefe guda akwai ƙarfin sojan lɍ@n ya zama barazana gare shi domin ba su tsammaci haka a farko, wanda ya haifar da gagaruma asarar da ta haifar da manyan matsaloli ga ci gaba da hare-haren Æm0rk@ kan lran, a ɗayan gefen kuma akwai matsin lamba daga masu goyon bayan ƙasar Ɗanyahoo a cikin Æm0ɍk@.
Kwana biyu da s**a wuce, wani babban jami’in Pakistan ya je Tehran babban birnin lran domin isar da saƙonni da buƙatun Æm0ɍk@, amma Iran ta ƙi amincewa da su gaba ɗaya.
Yanzu kuma Qatar ta shiga lamarin. Firaministan Qatar kuma Ministan Harkokin Wajenta, Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al Thani, ya je Tehran ne domin tattaunawa kan yadda za a yayyafawa zuciyar lran ruwan sanyi rage tashjn rikici da kuma sake buɗe hanyar diflomasiyya tsakanin lɍan da Æm0ɍk@.
Amma idan aka yi la’akari da wasu abubuwa lɍañ za ta iya nacewa a kan wasu muhimman sharuddanta.
Na farko: A ɗage dukkan takunkuman Æm0ɍk@ gaba ɗaya, ba a ɗage wani ɓangare kawai ba.
Na biyu: A kawo ƙarshen takunkumin katangewar ruwa da sauran matsin lambar tattalin arziki, sannan sojojin Æm0rk@ su rage ko su janye daga yankin gaba ɗaya.
Na uku: Batun Mashigin Hormuz ya kasance babban abin da ake takaddama a kai. Iran na son a mutunta matsayinta da ikonta a yankin, yayin da Æm0rk@ ke son mashigin ya kasance hanyar ruwa ta ƙasa da ƙasa wadda kowa zai iya amfani da ita domin ta samu ikon kubuta daga masifar karayar tattalin arziki da ke fuskanto ta. Wannan rashin jituwa na daga cikin abubuwan da s**a kawo cikas ga yarjejeniyar baya.
Na huɗu: Batun kuɗaɗen da ake karɓa daga zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigin na daga cikin muhimman batutuwan da Iran ke son a tattauna.
Na biyar: A yi yarjejeniya ta dakatar da yaƙin wadda za ta haɗa da ɗage takunkumi da kuma warware matsalar Mashigin Hormuz, maimakon a ware batutuwan ɗaya bayan ɗaya.
Me zai faru idan Iran ta amince?
Idan Tehran ta amince ta buɗe Mashigin Hormuz a madadin ɗage wani ɓangare kawai na takunkuman tattalin arziki, hakan zai iya nuna cewa rage matsin tattalin arziki shi ne babban abin da take nema.
Amma idan Iran ta ƙi amincewa da tayin Qatar, hakan zai ƙara nuna cewa tana kallon batun a matsayin babbar matsala ta siyasa, tsaro da kuma ikon yankin, ba wai tattalin arziki kaɗai ba.
A halin yanzu, Qatar da Oman suna ƙoƙarin samar da wata hanya ta wucin gadi da za ta ba jiragen ruwa damar wucewa ta Mashigin Hormuz, ciki har da shirin wata hanyar zirga-zirgar ruwa ta wucin gadi da kuma aikin kawar da nakiyoyi.
Idan diflomasiyyar ta gaza yin nasara fa?
Idan ƙoƙarin Qatar, Pakistan da Oman ya kasa samar da yarjejeniya, akwai yiwuwar abubuwa su ƙara tsananta:
1. Sake barkewar yaƙi:
Amurka da Iran na iya komawa ga ƙarin matakin soja idan diflomasiyya ta gaza.
2. Gulf ya koma filin yaƙi:
Idan rikicin ya sake ƙamawa, ƙasashen yankin za su iya shiga cikin babbar barazana, musamman saboda muhimmancin Mashigin Hormuz.
3. Matsalar mak**ashi ta duniya:
Raguwar zirga-zirgar mai da iskar gas ta Hormuz na iya ƙara matsa farashin mak**ashi tare da jefa tattalin arzikin duniya cikin matsala. Kafin yaƙin, kusan ganga miliyan 20 na mai a rana ke wucewa ta mashigin; yanzu zirga-zirgar ta ragu sosai.
A taƙaice
A yanzu ana ganin gagarumin ƙoƙarin diflomasiyya daga Qatar, Pakistan da Oman domin hana rikicin Iran da Amurka sake komawa yaƙi.
Qatar na da babban sha’awa wajen ganin an buɗe Hormuz, saboda tattalin arzikinta ya dogara sosai da fitar da LNG (Liquefied naturar Gas) ta wannan mashigi. Rahotanni sun nuna cewa rikicin ya riga ya yi wa fitar da LNG na Qatar babban tasiri.
Saboda haka, ziyarar Qatar zuwa Tehran ba ziyarar diflomasiyya ce kawai ba; **batun Hormuz, takunkuman Amurka, dakatar da yaƙi da kuma makomar tattaunawar Iran da Amurka duk suna kan teburin tattaunawar.**
Inji wani masani
Almujtabah Abubakar