Leadership Hausa Online

Leadership Hausa Online Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Leadership Hausa Online, Media/News Company, Abuja.

Ku kasance da Jaridar Leadership Hausa Online domin samun ingantattun labarai na gida Nijeriya hadi da Ketare,

Domin tallace tallace zaku iya tuntubar mu kai tsaye ta WhatsApp ko kira +2349038059408

ALLAHU AKBAR: Marigayi Shugaba Buhari ya cika kwanaki Arba'in da rasuwa, an bukaci Al'umma da su sanya shugaban a addu'a...
22/08/2025

ALLAHU AKBAR: Marigayi Shugaba Buhari ya cika kwanaki Arba'in da rasuwa, an bukaci Al'umma da su sanya shugaban a addu'ar ranar Juma'a.

YANZU-YANZU: Yan Shi'a a fadin duniya sun fara zaman makokin tunawa da ranar da Manzon Allah SAWW yayi wafati.
22/08/2025

YANZU-YANZU: Yan Shi'a a fadin duniya sun fara zaman makokin tunawa da ranar da Manzon Allah SAWW yayi wafati.

22/08/2025

Zamu Bude Ayyukan mu da

Muhammadur Rasulullah

Sheikh Ahmad Gumi Ya Yi Gargadi Kan Yiwuwar Shirin Mossad A NajeriyaBabban Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Dr. Ahmad A...
21/08/2025

Sheikh Ahmad Gumi Ya Yi Gargadi Kan Yiwuwar Shirin Mossad A Najeriya

Babban Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi, ya bayyana damuwa mai girma kan yiwuwar wasu jami’an cibiyar leken asiri ta ƙasar Isra’ila (Mossad) sun shiga Najeriya, inda ya ce hakan na iya zama barazana ga rayuwar wasu shugabannin Musulunci a ƙasar.

Sheikh Gumi ya yi wannan jawabi ne ta shafinsa na sada zumunta, inda ya yi zargin cewa zuwan Mossad zuwa Abuja na iya zama kafa ta kisan gilla ga manyan shugabannin Musulmi. Ya ce:

> “Wace irin riba ce gwamnati ke nema wajen bari ƙasar da aka sani da kisan kare dangi da zalunci ga Musulmi ta samu kafa a Najeriya?”

Malamin ya yi tsokaci kan mutuwar tsohon shugaban ƙasa, Janar Sani Abacha, inda ya ce gaggawar mutuwarsa bayan tarbar Yāsir Arafat a Abuja na iya nuna alamar cewa akwai wata ɓoyayyar alaƙa da irin waɗannan ayyukan leken asiri.

A cewar Sheikh Gumi, wannan matakin da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ɗauka wajen bari jami’an Isra’ila su taka ƙasa a Najeriya “shawara ce gurguwa” wacce zai fi shan wahala daga ita fiye da amfanin da zai samu.

Ya ƙara da cewa: “Wannan lamari kamar ƙwallon wuta ce a ƙasa, wacce idan ta tashi za ta fi shafar gwamnatin da ta bari fiye da yadda take zato.”

Har ila yau, Sheikh Gumi ya bayyana cewa haɗin kai da irin waɗannan ƙungiyoyi na iya haifar da tashin hankali, matsaloli, da kuma barazana ga tsaron ƙasa, musamman ga shugabannin Musulmi da ake gani a matsayin abin tsoro ga Isra’ila.

A halin yanzu dai, babu wata martani na hukuma daga gwamnatin Najeriya ko hukumomin tsaro, haka kuma Isra’ila ba ta fitar da wata sanarwa ba kan wannan zargi.

Sai dai kalaman Sheikh Gumi sun haifar da muhawara a shafukan sada zumunta, inda wasu ke goyon bayansa, yayin da wasu kuma ke yi masa tambaya kan dalilin nuna tsoron da ya bayyana a cikin zancensa.

YANZU-YANZU: Farashin kayan gona a kasuwar giwa.Ta jahar Kaduna a yau Alhamis21/08/2025Masara 40/42kDawa 38/40kWaken soy...
21/08/2025

YANZU-YANZU: Farashin kayan gona a kasuwar giwa.
Ta jahar Kaduna a yau Alhamis
21/08/2025

Masara 40/42k

Dawa 38/40k

Waken soya 68/70k

Farin wake zapa 90/93k

Farin wake Misra 89/90k

Shinkafa 38/42k

Dauro 48/50k

Allah ya ci gaba da kawo mana sauki a kasar nan.

21/08/2025

“Muƙira Muhammadu Rasulullahi.”

21/08/2025

“Domin tallace-tallace, zaku iya tuntubar mu kai tsaye ta WhatsApp ko ta kiran waya a wannan lamba: 09038059408.”

WATA SABUWA: Na Shirya Zama Da Farfesa Sani Rijiyar Lemo akan Kadiyar Sheikh Abduljabbar Farfesa Ibrahim Makari bai taɓa...
21/08/2025

WATA SABUWA: Na Shirya Zama Da Farfesa Sani Rijiyar Lemo akan Kadiyar Sheikh Abduljabbar

Farfesa Ibrahim Makari bai taɓa cewa yana goyon bayan Sheikh Abduljabbar Kabara ba. A maimakon haka, a cikin bayanansa na baya, ya bayyana a fili cewa:

"Sheikh Abduljabbar ba ya kare martabar Manzon Allah (SAW) da ilimi ba."

Saboda haka, kai Farfesan Hadisi, idan kana neman wanda zaka zauna da shi a tattaunawa ko zaman ilmantarwa saboda fahimtarsa da kuma tsantseni wajen bayyana sakon Sheikh Abduljabbar Kabara, to ni ne.

A matsayina na mai bin tafarkin ilimi da gaskiya, ina ganin dacewa a haska irin wannan zama a live, domin jama’a su saurara da kunnuwansu, su kuma fahimci ainihin gaskiyar maganganu. Wannan zai taimaka wajen kawar da shakku, hana yada jita-jita, da kuma tabbatar da cewa kowanne bangare ya ji da kansa abin da aka tattauna cikin gaskiya da hujja.

Allah ya sa hakan ya kasance abin amfanarwa ga al’umma, kuma ya sa ka, Farfesa, ka amince a gudanar da wannan zama cikin gaskiya da adalci.

TIRKASHI : Dan Gwagwarmaya Zangina Ya Caccaki Gwamna Dikko Radda Kan Aika-Aikar da Ta Afku a Katsina Na Kashe Al'umma Fi...
21/08/2025

TIRKASHI : Dan Gwagwarmaya Zangina Ya Caccaki Gwamna Dikko Radda Kan Aika-Aikar da Ta Afku a Katsina Na Kashe Al'umma

Fitaccen ɗan gwagwarmaya kuma ɗan asalin Jihar Katsina, Alhaji Sani Ahmad Zangina, ya fito fili ya nuna bacin ransa tare da kakkausar s**a ga Gwamna Umar Dikko Radda, yana mai cewa ya dace ya aje mulkin jihar sakamakon aika-aikar da ta faru a Katsina.

A cewar Zangina, wannan abin kunya da ya faru ba wai kawai cin amanar jama’a ba ne, har ma cin fuskar shugabanci da ya kamata ya kare rayuka da dukiyoyin al’umma. Ya ce lamarin bai shafi iyali ko ‘yan uwa na kusa da gwamnan ba, hakan yasa gwamnan ya zama mai shegen kwadayi da neman ribar kudi daga gwamnatin tarayya, wanda ya zarge shi da cewa shi ne ke ƙara hura wutar ta’addanci a Arewacin Najeriya.

“Abin da muke gani a Katsina da wasu jihohin Arewa, ba wani abu ba ne illa sakamakon wannan tsarin kudaden tsaro da ake bawa gwamnoninmu, kudaden da s**a koma tamkar jigon cin zarafin rayukan talakawa. Ina kira da babbar murya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya dakatar da irin wannan tsarin nan da nan, domin ya zama tushen zubar da jini da zaluncin da ake yiwa jama’ar Arewa,” in ji shi cikin kakkausar murya.

A ƙarshe, Alhaji Zangina ya yi addu’ar Allah ya jikanta da jinƙai ga waɗanda s**a rasa rayukansu a wannan masifa, ya kuma baiwa dangin da abin ya shafa hakuri, yana mai nanata cewa lokaci ya yi da al’ummar Arewa za su farka daga dogon barcin da suke yi, su daina bari ana cin mutuncinsu saboda kwadayin kudi.

KAJI LUKUTAR MAGANA: Duk wannan fadi tashin da nake yi wajen ganin na sulhunta kasashen dake fama da yake-yake ina yi ne...
21/08/2025

KAJI LUKUTAR MAGANA: Duk wannan fadi tashin da nake yi wajen ganin na sulhunta kasashen dake fama da yake-yake ina yi ne don fatan shiga Aljannah -inji Shugaban Amurka Donald Trump

Me zaku ce?

AURAN GATA: Hisbah Za Ta Aurar da Tubabbun ƴan Daba a KanoHukumar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa za ta duba yiwuwa...
21/08/2025

AURAN GATA: Hisbah Za Ta Aurar da Tubabbun ƴan Daba a Kano

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa za ta duba yiwuwar baiwa tubabbun ƴan daba da gwamnatin jihar ta yafewa damar shiga cikin shirin auren gata, domin su samu ƙarin kwanciyar hankali da tsari a rayuwarsu.

Kwamandan Hisbah na Kano, Sheikh Aminu Daurawa, ne ya bayyana hakan yayin taron yaye tubabbun ƴan daba 718 da gwamnatin jihar ta yafewa ƙarƙashin shirin “Safe Corridor”, wanda aka gudanar a shelkwatar ƴan sanda ta Kano a jiya Laraba.

Sheikh Daurawa ya ce, idan an tabbatar da shiryuwar waɗannan matasa, Hisbah a shirye take ta tallafa musu da guraben auren gata. Ya kuma ƙara da cewa, wannan zai taimaka wajen ƙarfafa mutuntakarsu da kuma kintsuwa a cikin al’umma.

Haka kuma, ya roƙi waɗanda s**a amfana da shirin da su zama masu ƙarfafa sauran ƴan uwansu waɗanda har yanzu ba su miƙa wuya ba, da su yi hakan.

Daurawa ya kuma shawarce su da su kasance masu bayar da sahihan bayanai ga hukumomin tsaro, domin taimakawa wajen cafke masu fataucin miyagun ƙwayoyi a cikin jihar.

Mùsùlmàn Nìjèŕiya Ba Za Su Taba Sanin Cewa Shèiķ Sani Yahaya Jingir Babban Garkuwa Ne Gare Su Ba Sai Ranar Da Aka Ce Bay...
21/08/2025

Mùsùlmàn Nìjèŕiya Ba Za Su Taba Sanin Cewa Shèiķ Sani Yahaya Jingir Babban Garkuwa Ne Gare Su Ba Sai Ranar Da Aka Ce Baya Nan

Daga Naseer Mande Ribah

Sheik Saniya Yahaya Jingir mutum ne mai son cigaban addini da kuma kishinsa, wanda kuma bai damu da tarkacen duniya ba. Idan kana so ka ga fushinsa, to ka taba addini, gashi kuma Allah Ya yi masa kwarjinin wanda ba kowane Malami yake da shi ba.

A kullum gwagwarmayar Sheik Jingir ita ce ya za a yì mùsùluñcì ya samu cigaba, dukkan tunaninsa na duniya wannan aikin ne ya sa a gaba, shi ya sa bai damu da zaģì ko s**a da kuma bin diddiginsa da wasu malamai suke yi masa ba, na ganin cewa ya aikata wani kusukurè domin su samu damar yadawa da kuma s**ar sa saboda bakar hassada da kuma son duniya irin tasu.

Sheik Sani Yahaya Jingir mutumin kirki ne sabanin wasu malamai 'yan son duniya, wadanda su duk wani zancè da za su yi za su yi ne domin kare muradunsu na neman abin duniya da kuma neman wata daukaka.

Hakika kasantuwar Sheik Jingir a wannan kasa babbar barazàna ce ga wasu baragurbìn mùsùlmàì.

Muna fatan Allah Ya kara masa hangen nesa da kuma jagoranci akan tafarki madaidaici, Ya kara tsare imaninsa Ya kuma kara yi masa kariya daga dukkan masharranta, amin Ya Allah.

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Leadership Hausa Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share