14/10/2025
YANZU-YANZU: Iyalan Sheikh Abduljabbar Sun Ce An Dauke Shi Daga Kurkukun Kurmawa Cikin Yanayi Mai Cike Da Rudani
Dan uwan Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara, Askia Nasiru Kabara, ya bayyana damuwar iyalan Sheikh Abduljabbar kan yadda aka ce an dauke shi daga gidan kurkuku na Kurmawa zuwa wani wuri da ba su sani ba.
A cewar Askia, daga baya ne s**a fara jin rade-radin cewa wai an kai Sheikh Abduljabbar gidan yarin Kuje da ke Abuja, lamarin da ya haifar da fargaba da tambayoyi masu yawa a tsakanin iyalansa.
Ya ce “Ina so in yi amfani da wannan dama, a madadin iyali da ’yan’uwa na Sheikh Abduljabbar, in sanar da Shugaban Hukumar Kula da Gidajen Yari ta Kasa da kuma Kungiyar Izala cewa duk abin da ya sami Sheikh Abduljabbar, to su tabbata yana wuyansu. Mun sani hukumar na da ikon kai fursuna duk inda ta ga dama, amma me ya sa sai a wannan lokaci aka dauke shi?”
Askia ya ci gaba da cewa, shekaru hudu kenan Sheikh Abduljabbar yana zaman kurkuku a Kurmawa, ba tare da matsala ba, amma sai yanzu da maganar Sheikh Lawan Triumph ta taso aka ji labarin an dauke shi.
“Mun ji maganganun da ’yan Izala s**a yi kan zargin cewa za a saki Sheikh Abduljabbar. Mu na zargin akwai wata bakarkashiya da makirci a cikin wannan lamari.”
Ya kuma yi kira ga manyan jami’an gwamnati da hukumomi su shiga cikin lamarin cikin gaggawa, domin a cewarsa, abu ne da ya shafi tsaron kasa baki daya.
Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima
Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu
Sufeto Janar na ’Yan sanda
Daraktan DSS
Gwamnatin Jihar Kano
Da kuma kungiyoyin kare hakkin dan Adam
“Ba za mu lamunci a bar wasu su yi wasa da rayuwar Sheikh Abduljabbar ba. Yanzu da aka dauke shi daga Kano inda iyalinsa ke kai masa abinci, muna cikin damuwa da fargaba kan irin kulawar da yake samu a wannan sabon wurin.”
Ya kammala da cewa iyalan Sheikh Abduljabbar na fatan hukumomi za su ji kiran su, su binciki lamarin, kuma su tabbatar da aminci da lafiya ga Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara.