Leadership Hausa Online

Leadership Hausa Online Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Leadership Hausa Online, Media/News Company, Abuja.

Ku kasance da Jaridar Leadership Hausa Online domin samun ingantattun labarai na gida Nijeriya hadi da Ketare,

Domin tallace tallace zaku iya tuntubar mu kai tsaye ta WhatsApp ko kira +2349038059408

Da gaske ne buhun masara ya dawo ₦13,000 a Taraba?
14/10/2025

Da gaske ne buhun masara ya dawo ₦13,000 a Taraba?

14/10/2025

Barkan Mu Da Dare Yanzu Haka Daga Ina Kake Bibiyan Mu..?

YANZU-YANZU: Iyalan Sheikh Abduljabbar Sun Ce An Dauke Shi Daga Kurkukun Kurmawa Cikin Yanayi Mai Cike Da RudaniDan uwan...
14/10/2025

YANZU-YANZU: Iyalan Sheikh Abduljabbar Sun Ce An Dauke Shi Daga Kurkukun Kurmawa Cikin Yanayi Mai Cike Da Rudani

Dan uwan Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara, Askia Nasiru Kabara, ya bayyana damuwar iyalan Sheikh Abduljabbar kan yadda aka ce an dauke shi daga gidan kurkuku na Kurmawa zuwa wani wuri da ba su sani ba.

A cewar Askia, daga baya ne s**a fara jin rade-radin cewa wai an kai Sheikh Abduljabbar gidan yarin Kuje da ke Abuja, lamarin da ya haifar da fargaba da tambayoyi masu yawa a tsakanin iyalansa.

Ya ce “Ina so in yi amfani da wannan dama, a madadin iyali da ’yan’uwa na Sheikh Abduljabbar, in sanar da Shugaban Hukumar Kula da Gidajen Yari ta Kasa da kuma Kungiyar Izala cewa duk abin da ya sami Sheikh Abduljabbar, to su tabbata yana wuyansu. Mun sani hukumar na da ikon kai fursuna duk inda ta ga dama, amma me ya sa sai a wannan lokaci aka dauke shi?”

Askia ya ci gaba da cewa, shekaru hudu kenan Sheikh Abduljabbar yana zaman kurkuku a Kurmawa, ba tare da matsala ba, amma sai yanzu da maganar Sheikh Lawan Triumph ta taso aka ji labarin an dauke shi.

“Mun ji maganganun da ’yan Izala s**a yi kan zargin cewa za a saki Sheikh Abduljabbar. Mu na zargin akwai wata bakarkashiya da makirci a cikin wannan lamari.”

Ya kuma yi kira ga manyan jami’an gwamnati da hukumomi su shiga cikin lamarin cikin gaggawa, domin a cewarsa, abu ne da ya shafi tsaron kasa baki daya.

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima
Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu
Sufeto Janar na ’Yan sanda
Daraktan DSS
Gwamnatin Jihar Kano
Da kuma kungiyoyin kare hakkin dan Adam

“Ba za mu lamunci a bar wasu su yi wasa da rayuwar Sheikh Abduljabbar ba. Yanzu da aka dauke shi daga Kano inda iyalinsa ke kai masa abinci, muna cikin damuwa da fargaba kan irin kulawar da yake samu a wannan sabon wurin.”

Ya kammala da cewa iyalan Sheikh Abduljabbar na fatan hukumomi za su ji kiran su, su binciki lamarin, kuma su tabbatar da aminci da lafiya ga Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara.

TIRKASHI: Ban shigo siyasa domin satar dukiyar al'umma ba, domin tun kafin na shigo siyasa ni mai arziki ne ba talaka ba...
14/10/2025

TIRKASHI: Ban shigo siyasa domin satar dukiyar al'umma ba, domin tun kafin na shigo siyasa ni mai arziki ne ba talaka ba. - Cewar Peter Obi

AN ZO WAJAN: Zan Iya Auŕen Mai Wushirya Amma Sai Yana Da Gidan Kansa, Cewar 'Yar GudaliyaHabashiya ta bayyana hakan ne a...
14/10/2025

AN ZO WAJAN: Zan Iya Auŕen Mai Wushirya Amma Sai Yana Da Gidan Kansa, Cewar 'Yar Gudaliya

Habashiya ta bayyana hakan ne a gaban kotu.

Me za ku ce?

DA ƊUMI-ƊUMI: An bukaci Majalisar Shura ta titsiye Sheikh Alkarmawy k**ar yadda ta titsiye Malam Lawan Triumph, kan kala...
14/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: An bukaci Majalisar Shura ta titsiye Sheikh Alkarmawy k**ar yadda ta titsiye Malam Lawan Triumph, kan kalamansa da ya yi cewar “ko mafarki mutum ya yi da raƙumi to Manzon Allah ya gani.

YANZU-YANZU: Budurwa ‘Yar Shekara 18 Na Neman Mijin Auren Da Ya Shirya Wata matashiya ‘yar asalin Jihar Kano ta bayyana ...
14/10/2025

YANZU-YANZU: Budurwa ‘Yar Shekara 18 Na Neman Mijin Auren Da Ya Shirya

Wata matashiya ‘yar asalin Jihar Kano ta bayyana burinta na yin aure cikin gaskiya da tsoron Allah.

Budurwar, wadda ta cika shekaru 18, ta ce tana da ilimin addini da na zamani, tare da iya sana’ar dinki wadda take dogaro da ita wajen neman halal.

Ta bayyana cewa tana da iyaye biyu, uwa da uba, suna raye cikin koshin lafiya, tana kuma gode wa Allah bisa ni’imominSa.

A cewar ta: “Duk wanda yake sona da gaskiya, kuma ya shirya yin aure tsakani da Allah, ina fatan mu hadu mu fahimci juna domin gina rayuwa ta aure mai tsafta da albarka.”

Lambar Tuntuba 08061630652

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Jihar Yobe Ya RasuRahotanni daga Jihar Yobe sun tabbatar da rasuwar Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ji...
14/10/2025

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Jihar Yobe Ya Rasu

Rahotanni daga Jihar Yobe sun tabbatar da rasuwar Shugaban Hukumar Zaɓe ta Jiha. Za a gudanar da Sallar Jana’izarsa a yau Talata, a Fadar Mai Martaba Sarkin Fika da ke garin Potiskum.

Allah Ya jikansa da rahama, Ya ba iyalansa da al’umma haƙuri da juriya.

TSEGUMI: Jarumin Kennywood Kb International tare da Samha Inuwa a daidai lokacin da hotunan su ke cigaba da jan hankalin...
14/10/2025

TSEGUMI: Jarumin Kennywood Kb International tare da Samha Inuwa a daidai lokacin da hotunan su ke cigaba da jan hankalin Al'umma a kafafen sada zumunta.

Shin wannan aure ne zai kara ko shiri ne?

YANZU-YANZU: Imam Junaidu Ya Bukaci Gwamnatin Kano Ta Shirya Zama Tsakanin Sheikh Abduljabbar da Majalisar ShuraImam Jun...
13/10/2025

YANZU-YANZU: Imam Junaidu Ya Bukaci Gwamnatin Kano Ta Shirya Zama Tsakanin Sheikh Abduljabbar da Majalisar Shura

Imam Junaidu ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Kano da ta shirya zama tsakanin Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara da Majalisar Shura, domin a ba shi shawarwari da nasiha cikin adalci.

A cewar Imam Junaidu, “Wannan shi ne abin da yafi k**a da adalci.”

Masu karatu, mene ne ra’ayoyinku kan wannan kira?

TIRKASHI: Kotun Majistare Mai Lamba 7 Ta Aike da ’Yar Guda Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon BatsaKotun Majistare mai lamba ...
13/10/2025

TIRKASHI: Kotun Majistare Mai Lamba 7 Ta Aike da ’Yar Guda Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa

Kotun Majistare mai lamba 7 karkashin jagorancin Mai Shari’a Halima Wali ta yanke hukuncin tura wata matashiya da aka fi sani da ’Yar Guda gidan gyaran hali, bayan ta same ta da laifin yin haɗin gwiwa da wani matashi mai suna Mai Wishirya wajen shiryawa da wallafa bidiyon batsa da ya bazu a kafafen sada zumunta.

BAZAN KARA BA: Jama’a ku taimaka ku ba Chairman Rarara hakuri, shi da Hajiya A’isha Humaira, don Allah su taimaka su, sa...
13/10/2025

BAZAN KARA BA: Jama’a ku taimaka ku ba Chairman Rarara hakuri, shi da Hajiya A’isha Humaira, don Allah su taimaka su, sa a sake ni.

Matashin mawaƙi Abubakar Umar Faruq, wanda aka fi sani da A.U.F, ya aiko da saƙon ba da hakuri ga shahararren mawaƙin siyasa, Dauda Kahutu Rarara tare da Amaryarsa A’isha Humaira, inda yake roƙon su da su yafe masa tare da taimakonsa a sake shi daga tsarewar da ake yi masa a gidan yari na jihar Katsina.

A cikin saƙon nasa, A.U.F ya bayyana cewa ya tuba daga duk wani abu da ya taɓa aikatawa da bai dace ba, yana mai cewa ba ya da niyyar yin fada da Rarara. Ya bayyana cewa Rarara uban girmansa ne, kuma shi ne abin koyin sa a harkar waka.

“Ban kai na yi fada da Chairman Rarara ba, shi ne abin koyi na kuma masoyina ne. Na tuba, kuma bana son a ɗauke ni a matsayin wanda yake rigima da shi,” in ji A.U.F.

Faruq ya kuma roƙi Hajiya A’isha Humaira da ta taimaka wajen sasantawa tsakaninsa da Rarara, yana mai cewa ba zai sake satar fasaha ta kowa ba a harkar waka.

Ya ƙara da cewa yana fatan za a gafarta masa tare da ba shi dama ya ci gaba da rayuwarsa cikin zaman lafiya da mutunta juna tare da samun yanci.

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Leadership Hausa Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share