WAT News Hausa

WAT News Hausa Tsantsar gaskiya da cikakken bayani

Isra'ila ta buƙaci Amurka da ta matsawa Masar kan sabon matakin soji da ta ɗauka a Sinai, wani yankin Masar da ke maƙwab...
20/09/2025

Isra'ila ta buƙaci Amurka da ta matsawa Masar kan sabon matakin soji da ta ɗauka a Sinai, wani yankin Masar da ke maƙwabtaka da Isra'ila, inda ta ƙaddamar da makamin kariya daga sama na ƙasar Sin mai suna HQ-9B.

Wannan makami na zamani na iya fatattakar jiragen yaƙi da mak**ai masu linzami daga adadin nisa mai tsawo, lamarin da ya tayar da hankalin Isra’ila wacce ta ce hakan barazana ce ga tsaronta.

Masar ta daɗe tana ƙarfafa iyakarta da Isra’ila da Gaza, abin da ke ƙara tada cece-kuce a yankin.

Shin a ganinku, wannan shiri kariya ne ga Masar ko barazana ga Isra’ila?

📷/: Benjamin Bibi Netanyhu/: Credit [Getty Images]

A taron ƙoli da aka gudanar a Doha, shirin Masar na kafa rundunar tsaro ta Larabawa irin ta NATO ya samu cikas bayan Qat...
20/09/2025

A taron ƙoli da aka gudanar a Doha, shirin Masar na kafa rundunar tsaro ta Larabawa irin ta NATO ya samu cikas bayan Qatar da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) s**a ƙi amincewa. Shirin ya dogara da yarjejeniyar tsaro ta 1950, inda Masar ta nemi kafa rundunar gaggawa domin kare Ƙasashen Larabawa daga barazana, musamman daga Isra’ila.

Sai dai rikici ya taso kan jagoranci inda Saudiyya ta nemi ta jagoranci rundunar, yayin da Masar ta ce ita ce tafi dacewa saboda ƙwarewar soji da take da ita. Duk da ƙin amincewa, Masar ta dage cewa rundunar za ta zama kariya ga Larabawa ba tare da dogaro da ƙasashen waje ba.

A ra'ayinku, wace ƙasa kuke ganin ya fi dacewa ace ta jagorancin wannan runduna?

📷/: Shugaba Abdel Fattah El-sisi na Masar/: Credit [Getty Images]

Juyin Mulki: Faransa ta sanar da dakatar da duk wata haɗin gwiwa ta yaƙi da ta’addanci da ƙasar Mali, bayan ƙarin rikici...
20/09/2025

Juyin Mulki: Faransa ta sanar da dakatar da duk wata haɗin gwiwa ta yaƙi da ta’addanci da ƙasar Mali, bayan ƙarin rikici na diflomasiyya.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Faransa ta ce ta kori jami’ai biyu daga ofishin jakadancin Mali a Paris, inda ta ayyana su a matsayin persona non grata wato kalmar diflomasiyya da ke nufin "ba a amince su zauna ko ci gaba da aiki a ƙasar ba".

A martanin Mali, ita ma ta kori jami’ai biyar na ofishin jakadancin Faransa.

Wannan mataki ya biyo bayan k**a wani ɗan ƙasar Faransa, Yann Vezilier, a Mali a watan da ya gabata bisa zargin shirin yin juyin mulki.

Shin menene ra'ayinku game da wannan hukunci na Mali?

📷/: Assimi Goita, Shugaban Juyin Mulkin Mali/: Credit [Getty Images]

Ma’aikatar Harkokin Waje ta ƙasar ta sanar da cewa wannan mataki ya zo ne kafin zaman Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA), in...
20/09/2025

Ma’aikatar Harkokin Waje ta ƙasar ta sanar da cewa wannan mataki ya zo ne kafin zaman Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA), inda kusan ƙasashe goma , ciki har da Biritaniya, Kanada, Faransa da Belgium, suke shirin su ma su amince da Ƙasar Falasɗinu.

Portugal ta ce ta ɗauki wannan mataki ne sak**akon matsanancin matsalar jin ƙai a Gaza da kuma damuwar da take da shi kan barazanar Isra’ila ta mamaye ƙasar Falasɗinu.

Shin kuna ganin wannan mataki zai ƙara matsa wa Isra'ila lamba?

📷/: Luis Montenegro, Firaministan Portugal/: Credit [Getty Images]

Saudiya, Faransa, Norway da Spain suna haɗa ƙwazo don tara tallafin gaggawa ga Hukumar Falasɗinu (PA) domin hana rushewa...
20/09/2025

Saudiya, Faransa, Norway da Spain suna haɗa ƙwazo don tara tallafin gaggawa ga Hukumar Falasɗinu (PA) domin hana rushewar ta, yayin da Isra’ila ke riƙe da ɗaruruwan miliyoyin daloli na Ramallah, in ji wata wasiƙa ga ƙasashen da za su iya bayar da gudunmawa.

Tun cikin watanni huɗu da s**a gabata, Ministan Kuɗi mai ra’ayin riƙau na Isra'ila, Bezalel Smotrich ya ƙi mika kuɗaɗen da Isra’ila ke tattarawa a madadin PA. Waɗannan kuɗaɗen sune mafi yawan kasafin kudin Ramallah, kuma riƙe su ya sa Hukumar Falasɗinu wato (PA) ke halin durƙushewa idan ba'a bada agajin kuɗi gare ta ba.

Shin me za ku ce game da wannan?

📷/: Shugaba Emmanuel Macron na Faransa da Yariman Saudiyya Mohammed Bin Salman (MBS)/: Credit [Getty Images]

Ministan Tsaron Pakistan Khawaja Asif ya bayyana hakan ne yayin da ɗan jarida ya yi masa tambaya jim kaɗan bayan rattaba...
20/09/2025

Ministan Tsaron Pakistan Khawaja Asif ya bayyana hakan ne yayin da ɗan jarida ya yi masa tambaya jim kaɗan bayan rattaba hannu kan sabuwar yarjejeniyar tsaro da Pakistan ta yi da Saudiyya, inda ya tabbatar cewa Saudiyya za ta tsaya kafaɗa da kafaɗa da Pakistan ƙarƙashin sabuwar yarjejeniyar tsaro da aka ƙulla da Riyadh.

Game da yiwuwar yaƙi da Indiya, Asif ya ce: "Eh tabbas. Babu wata shakka a kai, Saudiyya za ta tsaya a gefen Pakistan".

Shin kuna goyon bayan shigar ƙasar Saudiyya yaƙi da Indiya a duk lokacin da rikici ya ɓarke tsakaninta da Pakistan?

📷/: Khawaja Asif/: Credit [Getty Images]

Pakistan da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro a ranar 17 ga Satumba, wacce ta tanadi cewa duk wani hari ...
19/09/2025

Pakistan da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro a ranar 17 ga Satumba, wacce ta tanadi cewa duk wani hari da aka kai kan ɗaya daga cikin ƙasashen biyu, za a ɗauke shi a matsayin hari kan dukkansu.

Ministan tsaron Pakistan ya bayyana cewa ƙasar za ta ba da damar amfani da mak**an nukiliyarta idan Saudiyya ta buƙata, lamarin da ya jawo cece-kuce a duniya game da makomar tsaro a yankin Gabas ta Tsakiya.

Shin kuna ganin wannan mataki zai kawo kwanciyar hankali ko ƙara tayar da hankali a yankin Gabas Ta Tsakiya?

📷/: File Photo [X]

Aƙalla mutane 84 ne aka tabbatar sun rasu a safiyar Juma’a lokacin da dakarun ‘yan tawaye s**a harba makami cikin wani m...
19/09/2025

Aƙalla mutane 84 ne aka tabbatar sun rasu a safiyar Juma’a lokacin da dakarun ‘yan tawaye s**a harba makami cikin wani masallaci da ake gudanar da sallar Asuba a birnin El Fasher na Darfur, in ji likitoci da ƙungiyoyin agaji.

Rahotanni sun ce cikin waɗanda s**a mutu akwai mata da yara, yayin da wasu s**a jikkata. Gwamnan Darfur, Minni Minnawi, ya ce adadin waɗanda s**a mutu ya kai sama da 60.

📷/ Hoto/: Janar Mohammed Hamdan Dagalo, Shugaban 'yan tawayen RSF/: Credit [Reuters]

Rahotanni sun bayyana cewa Pakistan za ta tura makamin missail ɗinta na zamani mai suna Ababeel domin tsaron Saudiyya ta...
19/09/2025

Rahotanni sun bayyana cewa Pakistan za ta tura makamin missail ɗinta na zamani mai suna Ababeel domin tsaron Saudiyya tare da Haramain guda biyu, wato Masallacin Harami a Makka da Masallacin Annabi Muhammad (S.A.W) a Madina.

Makamin Ababeel na iya ɗaukar mak**an nukiliya kuma yana da ikon kai hari ga wurare masu nisa da sauya alƙibla a lokaci guda, abin da masana ke cewa zai ƙara ƙarfin tsaron haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu.

A ganinku, wannan mataki zai iya daƙile duk wata barazana da Saudiyya za ta fuskanta kuwa?

📷/: Hoto/: Firaministan Pakistan, Muhammad Shehbaz Sharif da Yarima Mohammed Bin Salman (MBS)/: Credit [X]

Wariya kan Afrika: Ƙungiyar ƙasashen Alliance of Sahel States (AES) wato Mali, Niger da Burkina Faso sun sanar da ficewa...
19/09/2025

Wariya kan Afrika: Ƙungiyar ƙasashen Alliance of Sahel States (AES) wato Mali, Niger da Burkina Faso sun sanar da ficewarsu daga Kotun Laifuka ta Duniya (ICC), inda s**a zargi kotun da nuna son kai da wariya kan ƙasashen Afirka.

Ƙasashen uku da sojoji ke mulki sun bayyana cewa za su kafa Kotun Laifuka ta Sahel don Kare Haƙƙin Ɗan Adam, wacce za ta riƙa gudanar da shari’o’in manyan laifuka da s**a shafi yankin.

Wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasashen ke ƙara ƙarfafa haɗin kan su da kafa sabbin tsare-tsaren yankin bayan janyewa daga ECOWAS a farkon shekarar nan.

Shin kuna ganin wannan sabon tsarin shari’a zai taimaka wajen kawo gaskiya da adalci a Afirka fiye da kotun ICC ta Duniya?

📷/: Hoto/: File Photo [GGL]

Iran da Isra'ila: Mazauna yankin filin gwajin mak**an roka na Semnan a Iran sun ruwaito wani gagarumin harba makamin rok...
19/09/2025

Iran da Isra'ila: Mazauna yankin filin gwajin mak**an roka na Semnan a Iran sun ruwaito wani gagarumin harba makamin roka da daddare. Shaidu sun bayyana jin ƙarar da ta ɗauki hankali tare da haske mai kaifi da ya ratsa sararin samaniya, k**ar yadda rahotannin na’urorin sa ido s**a tabbatar.

Yankin Semnan yana da nisan kusan kilomita 219 daga gabashin birnin Tehran, kuma tun da daɗewa Jamhuriyar Musulunci ta ke amfani da wannan yanki a matsayin cibiyar wasu manyan ayyukan sojinta.

Shin me za ku ce game da wannan?

📷/: Hoto/: Credit [X]

Cin karo da shari'a: Gwamnatin Taliban a Afghanistan ta ɗauki sabon mataki na cire littattafan da mata s**a rubuta daga ...
19/09/2025

Cin karo da shari'a: Gwamnatin Taliban a Afghanistan ta ɗauki sabon mataki na cire littattafan da mata s**a rubuta daga tsarin koyarwa a jami’o’i, tare da haramta darussa da s**a shafi ‘yancin ɗan Adam da kuma cin zarafin mata.

Rahotanni sun nuna cewa littattafai 140 da mata s**a wallafa, ciki har da na kimiyya k**ar "Safety in the Chemical Laboratory" na cikin littattafai 680 da Taliban ta ce suna da matsala saboda suna "saɓanin Shari’a" ko kuma manufofin gwamnatin.

Bugu da ƙari, an umarci jami’o’in da kada su sake koyar da darussa 18 saboda, a cewar jami’in Taliban, "suna saɓawa ƙa’idojin Shari’a da manufofin tsarin mulki."

Shin menene ra'ayinku game da wannan?

📷/: Getty Images

Address

Ibrahim Babangida Way Maitama Abuja
Abuja
900180

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when WAT News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share