Kankara Post

Kankara Post Jairdar Kankara Post kafar yada labaru cedata shahara wajen samar maku da shahihai,ingantattun labar.

17/08/2025

Me Kuka Fi Bukata Gwamnati Tayi Maku?

Kungiyar Concern Teachers Forum For Educational Development A Karamar Hukumar Kankara Ta Karrama Sakataren Hukumar Ilmin...
17/08/2025

Kungiyar Concern Teachers Forum For Educational Development A Karamar Hukumar Kankara Ta Karrama Sakataren Hukumar Ilmin Bai Daya SUBEB Reshen Karamar Hukumar Kankara Jihar Katsina



‎Aranar 16/8/2025 Hadaddiyar kungiyar CONCERN TEACHERS FORUM FOR EDUCATIONAL DEVELOPMENT KANKARA ta gudanar taron karamawa da kuma mika wasu kayayyaki ga sakataren hukumar ilmin Bai daya reshen karamar hukumar Kankara Malam Ibrahim Sani PhD.


‎Ajawabin Comr. Nazifi Mansir Yargoje wanda shine Shugaban Kungiyar ya bayyana kungiyar ta Karrama Sakataren ne domin nuna jin dadin ta da ire iren aiyukan cigaba yake Kawowa a fannin Ilmi akaramar hukumar Kankara ta Jihar Katsina tun bayan hawan shi kujerar Shugabancin wannna Shiyyar.


‎Comr Naziru ya Kara dacewa kungiyar Concern Teachers Forum For Educational Development A Karamar Hukumar zata cigaba da bada goyon bayan ta akan dukkanin abubuwan da ya taso afannin ilmi a karamar hukumar Kankara.

‎M'ajin Kunagiyar Hajiya Aisha Lawal ta karane da godewa Sakataren Hukumar Ilmin ta Kankara abisa yake kakkarinfafannin ilmi


‎Takuma Yi fatan ya cigaba da Kawowa yankin dukkanin wasu abubawan cigaban Ilmin yakin kuma zasu marama shi baya akungiyance.


‎Bayan kammala jawabin Hajiya Aisha Comr. Aliyu Nasir ya jawabin nuna jin dadin shi da irin wannan muhimiyar nuna kauna da Kungiyar ta nunama Sakataren ilmin.

‎Aliyu Nasir Kankara ya kuma ba Shuwagabannin Kungiyar shawarwari masu mahimmanci akan yadda zasu kara hamakar Kungiyar.

‎Malam Ibrahim Sani PhD yayi jawabin godiya ga Yayan kungiyar ya bayyana matukar farin cikin shi da irin wannan muhimiyar karramawa dabai tunanin taba.

‎Malam Ibrahim Sani PhD ya yabawa Shugabani da sauran mabiya Kungiyar Zai basu cikakkiyar kulawar domin kawo cigaban Ilmi a karamar hukumar Kankara jihar Katsina.


‎Wasu daga cikin Ya'yan Kungiyar Sun kara bayyana Sakataren da mutum mai kokarin kawo sauyin a fannin Ilmi akaramar hukumar.

‎Daga cikin kayayyakin da kungiyar ta Karrama Sakataren sun hada da kyautar Karramawa ta musanman,Kalanda,Hatimi Mai dauke da Sunan shi.

📷 Rana24

HOTUNANYadda Wani Kansila Mai Suna Hon. Hassan Safiyanu Yargoje Kewa Al'ummar Mazabar Danmaidaki Aiki."Hon. Hassan Safiy...
25/07/2025

HOTUNAN
Yadda Wani Kansila Mai Suna Hon. Hassan Safiyanu Yargoje Kewa Al'ummar Mazabar Danmaidaki Aiki.

"Hon. Hassan Safiyanu Yargoje matashin dan siyane wanda yakeda zuciyar ganin Al'ummar yankin sunci gaba fiye da kanshi" Hakan yafito ne daga bakin wani mazaunin garin Yargoje ayayin ziyarar Ganin yadda ake gudanar da wani muhimmin aikin hanyar ruwa wato (DRAINAGE) atsakiyar Garin Yargoje dake Karamar hukumar Kankara.

Kamar yadda muka tarar ana cigaba da gudanar da aikin gadar tsallakawa da ababen hawa kebi, muntarar anar gudanar da ita cikin aminci da nagarta.

Munyi kokarin zantawa da Al'ummar yankin da akewa aikin inda wasu dama samu damar hakan s**a nuna matukar farin cikin su dasumawar aikin.

Haka zalika gamida godiya akan yimasu wannan Hanya ruwa mai dauke da Kwalbati, wadda arashinta abaya sun fuskanci rigingimu atsakankanin jama'a yankin da Ruwa ke bi.

Zamu cigaba da kawo maku yadda aikin ke gudana

📷
Rana24

Dan Majilisar Wakilai Hon. Shehu Dalhatu Tafoki Ya Rabawa Al'ummar Shi Na Yankin Kankara, Faskari Da Sabua N150m.Dan maj...
09/03/2025

Dan Majilisar Wakilai Hon. Shehu Dalhatu Tafoki Ya Rabawa Al'ummar Shi Na Yankin Kankara, Faskari Da Sabua N150m.

Dan majalisar Tarayya na mazabar Ƙanƙara/Faskari/Sabuwa Hon Engr Shehu Dalhatu Tafoki ya raba buhunan shinkafa ƙanana 10kg 2500,25kgs 500 da kuma manya Masu nauyin 50kgs 100.

Dan Majilisar Bai Tsaya nanba yakara da tsabar kuɗi N52m a matsayin tallafin azumi ga al'ummar mazaɓarsa

Taron rabon kayayyakin ya gudana ajiya Asabar 8 ga watan March 2025, daidai da 8 ga watan Ramadan 1446, a Farfajiyar Kasuwar Zamani ta garin Kankara.

Dr.Bishir Usman Ruwangodiya ya bayyana yadda tsarin rabon kayan arziki yake, inda yace kayan da aka sawo sun kai N98m sai kuma tsabar kudi N52m, da in an haɗa gaba ɗaya ƙimar kayan da kudin sun kai N150m

Dr. Ruwangodiya ya cigaba da cewa wadanda zasu amfana da tallafin akwai, Party excos na matakin dukkanin mazaɓun Kankara/Faskari/Sabuwa sun sami jimillar N4m, sai chairman party na mazabu su 31 kowa 20k, excos na LG su 72 kowa 20k each, shuwagabannin APC su uku na ƙananan hukumomin kowa zai sami 50k

Akwai kuma manyan exco na jiha suna da 500k, shuwagabannin jam'iyyar APC a matakin jiha N1m, hakimai kowa 50k, limamai 50k magaddai 20k masu da'awa 3m jami'an tsaro 3m, yan kwamiti 4m, yan Midiya 1.5m

Akwai kuma mutum 1500 da aka zabo daga Kankara/Faskari/Sabuwa, kowa 10k, ƴan amanar ɗan majalisar wato support interest group N5m, masu ruwa da tsaki na jam'iyyar APC N4m, executive stake holders N2m, wadanda iftilain yan bindiga ya shafa 2m, uwar gidan ɗan majalisar ya ware mata N3m don ta rarraba ma mata ƴan uwanta, masu dakko kaya don rarrabuwa N3m, yan jarida N1m, da dai sauransu

Jaridar Rana24 ta kasance yayin gudanar da taron ta kuma ruwaito buhunan shinkafa da za a raba wa shuwagabannin

Waɗanda s**a halarci taron akwai mataimakin gwamnan jihar Katsina Mai girma Faruk Lawal Jobe, sakataren jam'iyyar APC na jiha, zababbun shuwagabanin Kananan hukumomin Sabuwa Engr Sagir Tanimu, zababben shugaban karamar hukumar Kankara Hon. Kasimu Dantsoho, zababben mataimakin shugaban karamar hukumar Faskari Hon Isyaku Wada da sauran mutane da dama.
Dasauran manyan baki da dama

SANARWAR DAURIN AURE:  Amadadin Iyalan Marigayi Malam Idris Maikayan Miya Kankara  Na Farin Cikin Gayyatar Al'umma Zuwa ...
27/07/2024

SANARWAR DAURIN AURE:
Amadadin Iyalan Marigayi Malam Idris Maikayan Miya Kankara Na Farin Cikin Gayyatar Al'umma Zuwa Daurin Auren Shugaban Jaridar Rana24 Wanda Za'ayi Kamar Haka 👇

RANA:9th, August -2024
LOKACI:2:30 Na Rana
WURI:Kofar Fada Kahutu Karamar Hukumar Danja Jihar Katsina

AKaron  Farko Kungiyar FITIYANUL ISLAM Reshen Karamar Hukumar Kankara Jihar Katsina Tayi Taron Fadakarwar Ga 'Ya'yanta.K...
20/06/2024

AKaron Farko Kungiyar FITIYANUL ISLAM Reshen Karamar Hukumar Kankara Jihar Katsina Tayi Taron Fadakarwar Ga 'Ya'yanta.

Kungiyar Addinin ta FITIYANUL ISLAM ta gudanar da taron ne a ranar 19 ga watan Yuni Shekarar 2024 a Makarantar firamare Nuhu Model a garin Kankara jihar katsina.

Ayayin Taron Shugaban ta na wannan yanki Malam Tasiu Yusuf yayiwa Al'ummar malarta Wannan taron marhabin da kuma fatan Allah ya baiwa dukkanin wanda ya samu ikon Halarta da wadanda ma basu samu damaba sabili da wasu uzurirrikan rayuwa ladar sada Zumunci.

Shugaban ya kuma nuna farin ciki da godewa Manyan shehunnan Malumma da s**a halarci taron.

Kamar yadda Rana24 ta ruwaito Shugaban ya Kara da bayyana cewa Kungiyar FITIYANUL ISLAM dai na daya daga Kungiyoyin da suke was Addinin musulumci Hidindimu ayayin gudanar da wani Taron Al'umma ko ako'inama aduk lokacina da bawa Ke bukatar taimkon gaggawa.

Malam Abdullahi Na-Daura na daya daga cikin Malama da s**ayi jawabi ayayin taron inda yayi jawabi akan muhimmancin hadinkai ga dukkanin al'ummar da kuma matsalolin da rashin hadinkan Ke samarwa ga Al'umma da Kungiyoyi.

Mataimakin Babban Limamin Mabiya Darikar Tijjaniya reshen karamar hukumar Kankara Malam Ghali Abdullahi Ratibi ya fadakar da 'ya'yan Kungiyar FITIYANUL ISLAM din muhimman aikace aikacen s**a Rataya a wuyan Dan Agaji ga Addinin musulumci akoyaushe.

Hakazalika Babban Limamin Mabiya Darikar Tijjaniya Reshen Karamar Hukumar Kankara Malam Surajo Abdullahi Kankara yayi bayanai masu matukar mahimancin gaske da Kuma shwarwari ga dukkanin wanda yake gudanar da wannnan aiki.

Shehun Malamin yakumayi kira da Al'umma mu tashi TSAYE wajen ganin MUN nemi ilmi domin samun cigaba Adukkanin al'amurorin damuka sa agaba.

Limamin ya kuma kirayi mutane da musakasance masu hadin kai da rikon Amana da hakuri da fidda son zuciya Adukkanin al'amurori.

Malam Nasiru Mai-unguwa ya Gudanar Da Bayani akan waye Dan Agaji inda yakuma bayyana Wasu daga cikin Aikace aikacen da Halayen dukkanin Dan Agaji kamar haka

Yafara da bayyana Dan Agaji amatsayin Sojan Addinin musulumci,Mai juriya,Rikon Amana,Mai Gaskiya,Mai Hankali,Mai Tsafta,Mai Aikin Addini,Mai hakuri da nemana Ilmi akodayaushe.

Babban Kwamandan Dakarun matasan Agajin Na Fitiyanul Islam Reshen Karamar Hukumar Malam Auwal Salisu yayi godewa shugaban kungiyar Malam Tasiu Yusuf da dukkanin sauran Yan Kwamitin tafiyar da wannan Kungiyar duba da yadda s**a kokarta wurin shirya masu wannna taron Fadakarwa na Farko a karamar hukumar Kankara.

Wadanda s**a samu halartar Taron sun hada da Malam Magaji,Alhaji Masa'udu maikatako da sauran Al'umma da da dama.

A yau ne Babbar kotun Tarayya dake Kano zata yanke hukunci kan shari'ar da Babba Ɗanagundi ya shigar da gwamnatin jihar Kano, kan hana rushe masarautu 5

Mai shari'a Abdullahi Muhammad liman ne zai yanke hukunci a babban kotun Tarayya dake jihar Kano zata yanke hukunci kan karar da Babba Ɗanagundi ya shigar da gwamnatin jihar Kano kan hana rushe masarautun jihar.

Ko wa kuke fatan yayi nasara a wannan shari'ar?

Ku biyo mu domin jin yadda za'a toya wainar a yau.

KATSINA COLLEGE KATSINA OLD BOYS ASSOCIATION 2001/2006 GRADUATE'SƘungiyar tsofaffin ɗalibai na kwalejin Katsina watau Ka...
17/06/2024

KATSINA COLLEGE KATSINA OLD BOYS ASSOCIATION 2001/2006 GRADUATE'S

Ƙungiyar tsofaffin ɗalibai na kwalejin Katsina watau Katsina College Katsina ƴan shekarar 2006 (KCK 2006), a ƙarƙashin jagorancin shugaban kungiyar Nura Saulawa

Ana sanarwa tare da gayyatar dukkan mambobinta cewa, akwai taron sada zumunci (kamar yadda aka saba), a gobe sallah 18/06/2024.

Taron zai guda ne a harabar makarantar ta KCK, da misalin ƙarfe 4 na yamma, In shaa Allahu.

Allah Ya Bada Ikon Halarta, Amin.

Sanarwa daga jami'in huda da jama'a na kungiyar Mannir Idris Kankara

Katsina State Government Scores high marks in addressing Water Supply Challenges as CFM of Netherlands Pays Visit to the...
24/04/2024

Katsina State Government Scores high marks in addressing Water Supply Challenges as CFM of Netherlands Pays Visit to the Deputy Governor Mal. Faruk Lawal Jobe_

A team of Climate Fund Managers from Netherlands and InfraCo Nigeria have commended the Dikko Radda led administration in Katsina State for its unwavering commitment to addressing water Supply Challenges in the State.

The team gave out this commendation when its members paid a courtesy visit on the deputy Governor of Katsina State Mal Faruk Lawal Jobe in Katsina State Government House.

The Climate Fund Managers took the advantage of the visit and inspected water works, water treatment plants as well as the booster stations of Ajiwa and Zobe Dams situated in Batagarawa and Dutsinma respectively.

Earlier, the deputy Governor of the State Mal. Faruk Lawal Jobe spoke at length on the giant strides so far put in place in the area of water supply by the present APC administration in the State.

Kungiyar Tafoki Support Organisation Ta  Rabawa 'Yan Gudun Hijira Kayan Tallafi A Garin Kankara Jihar Katsina.✍️Mannir I...
30/03/2024

Kungiyar Tafoki Support Organisation Ta Rabawa 'Yan Gudun Hijira Kayan Tallafi A Garin Kankara Jihar Katsina.

✍️Mannir Idris Kankara

A ranar 28/3/2024 Kungiyar dake goyowa Dan majilisar wakilan mai wakiltar Kananan hukunomin Kankara, Faskari da Sabuwa a tarayya Hon. Shehu Dalhatu Tafoki ta bayar da tallafi ga masu gudun hijira da Kuma gajiyayyu dake shiyyar Unguwar Nasarawa cikin garin kankara.

Kayan tallafin sun hada da Buhunnan shinkafa 2 kwalayen kilin da Kuma na sabulun wanka guda goma sha biyu.

Anashi jawabin shugaban kungiyar baki daya Malam Musbahu Tukur Kogunan sarkin Pauwa,yace wannan sun yini ne amatsayin somin dabine.
Hasalima sunyi hakane maimakon suje hannu , Amma akwai abubuwan da dama dake kan hanyar zuwa.

Shugaban kungiyar TSKmatakin karamar hukumar kankara Nasir Wada Zango ya yaba da gudumuwar tallafin yakuma gargadi ga shuwagaban rabon kayan.

Malam Nazir Abdullah wanda shine jogaran wadanda kayan yayi Godiva duba da yanda aka zabi makarantar shi amatsayin inda, za'a kaddamar dactallafin.

Angudanar Da Rabon Shinkafar Da Dan Majilisar Tarayya Hon. Engr. Shehu  Dalhatu Tafoki Ya Tallafawa Al'ummar Kankara Jih...
24/03/2024

Angudanar Da Rabon Shinkafar Da Dan Majilisar Tarayya Hon. Engr. Shehu Dalhatu Tafoki Ya Tallafawa Al'ummar Kankara Jihar Katsina.

✍️Mannir Idris Kankara.

A ranar Lahadi 24/3/2024 kwamitin rabon tallafin kayan da Danmajilisar Tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Kankara, Faskari Da Sanuwa Hon. Shehu Dalhatu Tafoki ya bayar ga dukkanin jama'ar dayake wakilta.

Rabon Tallafin Wanda ya gudana karkashin Masu taimaka mashi na musan man afannin ayyukan majilisa Engr. Abdulbasir Gambo Kankara Da Hon. Nasir Wada Zango ya gudana kamar yadda aka tsara.

Abayanin da muke samu daga daya daga viking masu rabon Hon. Nasir Wada Zango ya bayyana wannan shinkafa da kudine da aka bayar domin tallafawa al'umma su gudanar da azumi lafiya.

Haka zalika Engr. Abdulbasir Yayi kira ga wakilan da aka baiwa sakon shinkafar da kudin suji tsoron Allah su kamanta gaskiya da sanin yakamata yayin da zasu rabawa al'ummomin su.

Bayan tabbatuwar wakilan kowace mazabun ne aka fara Kiran sunayen mazaba-mazaba ana damka wa wakilan buhunnan shikafa 20-20 tareda da mika masu N100,000 ga kowace mazaba.

Wakilin Rana24 ya tambayi wasu daga cikin wadanda s**a amfana da yanayin basu kayan inda s**a ce ba'abinda zasu ce tun daga Hon. Tafoki hat zuwa mask rabo illa s**e Allah ya Basu abinda suke nema.

Hon. Aminu Suleiman Wanda dayane daga cikin yan kwamitin rabon wadannan kayan Alheri yazo lokacin da ake bukatar shi, Yakima shedamana ba"ataba samun Danmajilisar dayayi masu makamanci irin wannan tallafi ba.

Hajiya Abule Hamza Mai baiwa shugaban karamar hukumar shawara ta fannin mata tace gaskiya irin wannan abune dake karawa shuwaganin farin jini da kwarjini a idanun al' umma da ake shugabanta.

Mazbu 7 ne wadanda aka s**ai saura Wanda aka mikawa 4 ayayin kaddamarwa.

Mazabun Da S**a karbi kayan tallafin sun hada :
Ketere, kukasheka, Zango Zabaro, Wawarkaza, Kankara A&B, da sauran su.

Bayan kammala rabawa mazabune kwamitin ya cigaba da Kungiyoyi al'umma matasa Dana sna'o'i na karamar hukumar inda wa

Dan-majilisar Dattawa Sen. Muntari Mohammed Dandutse Ya Gwagwaje Al'ummar Karamar Hukumar Kankara Da Kudade.Daga: Mannir...
21/03/2024

Dan-majilisar Dattawa Sen. Muntari Mohammed Dandutse Ya Gwagwaje Al'ummar Karamar Hukumar Kankara Da Kudade.

Daga: Mannir Idris Kankara

A yau Laraba Dan-majalisar Dattawa yankin Katsina ta kudu Sen. Muntari Mohammed Dandutse ya rabawa mutane 400 N10,000 a karamar hukumar kankara.

Hon. Abubakar Nuhu wanda shine jagoran wakilan da s**a gudanar da rabon kudaden wadanda s**a zo daga garin Funtua ya fara da bayyanawa Mutanen das**a amfana da sakon godiya daga Danmsjilisar ga Al'immar karamar hukumar ta kankara bisa nuna kauna da goyon bayan da suke nuna mashii.

Sannnan ya kuma tabbatar da akwai wasu ayyukan alheri dake tafe zuwa garin na kankara Wanda Sanatan yasamo daga tarayya daga bisani ya lissafawa al'umma yadda tsarin rabon kudin yake zuwa kaso 4.

Kason farko akwai Malamai 100, 50,50 daga Darika da Izala, Mata 100,Dattawa 100 sainkuma matasa 100 Wanda jimillar s**a kai 400 Inda kowa yasamu kunshin N10, 000 hannu da hannu.

Malam Hamisu Donawa na daya daga cikin kwamitin rabon ya bayyana sun kasa rabon shiyyoyi 11 na mazabun da karamar hukumar ta kunsa, wanda Hakan yasa mutanen wajen gari sun amfana matuka.

Daya daga cikin Malaman da s**a amfana Malam Abdulrashid ya yaba sosai da wannan tsari domin zai ragewa mutane radadin halin da ake ciki, shima Malam Isah ya godewa Danmajilisar gamida yin addu'a ta Kara samun cigaba.

Mata da Maza dama ne s**a kasance cikin farin ciki.

Nazir Isiya wanda shine mai taimakawa wajen biyan Malamai Addini ya yaba da halin dattakon da aka nuna.

Haka zalika shima Aliyu shehu dake bangaren biyan mata ya nuna godiya da yadda matan s**a nuna yayin tantacewa.

Sauran Yan kwamitin tafiyar da rabon kudin sun hada da Bature Omo, Shamsuddeen Magaji, Abdulbasir Maihoto, Danjuma Direba da Kuma Sadiq Pauwa.

Anyi rabon batare da samun Wani tarnakiba.

MACE MAI KAMAR MAZA : Mai Baiwa Gwamnan Jihar Katsina Shawarma Akan Huddatayyar Gwamnatoci Hon. Hadiza Hassan Maikudi Ta...
18/03/2024

MACE MAI KAMAR MAZA : Mai Baiwa Gwamnan Jihar Katsina Shawarma Akan Huddatayyar Gwamnatoci Hon. Hadiza Hassan Maikudi Ta Rabawa Al'umma Buhunnan Shinkafa 40.

Hon. Hadiza Hassan Maikudi wadda itace maibaiwa Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ta bayar da manyan Buhunnan shikafa masu nauyin 50 ga al'umma.

Kamar yadda wakilin mu ya tabbatas anyi rabon shinkafar ne Farfajiyar sabuwar Kasuwar Kankara wadda akafi sani da Modern Market dake kan titin Zuwa garin Dutsinma cikin garin Kankara. Shinkafar buhunna 40 masu nauyin 50 kowannanen su.

Ayayin jawabin shi Wakilin Rabon Shinkafar Engr. Abdulbasir Gambo Kankara ya bayyana "Wannan rabon shinkafa Hajiya Hadiza tayine domin tallafawa al'umma domin Allah da zummar ragewa jama'a wahalhalin alfarmar wannan wata na Ramadan.

Al'umma sun Yaba da yadda Engr. Abdulbasir ya tsaya Kai da fata tun daga farko rabo har karshen rabon wannan shinkafa .

Maitaimakawa gwamnan jihar Katsina ta fannin samar da labarai daga karamar hukumar kankara Muhammad Sale OC (Manga) wanda shima dayane daga masu rabon wannnan shinkafa Kuma daga cikin matasan da suke goyawa Hon. Hadiza Baya ya tabbatar cewa wannan kadan ne daga cikin alkairan da Hajiyar keda zummar samawa al'umma.

Wasu daga cikin wadanda s**a amfana da wannan shinkafa sun yaba da wannan taimako datayi musanman acikin irin wanna yanayi da ake ciki na rayuwa. Sun Kuma Yi addua'ar Allah ya jikan iyayenta yasa agama da duniya Lafiya.

Daga cikin wadanda s**ai aikin rabon sun hada da Malam Ibrahim Manager, Hon. Aminu Suleiman da sauransu

📷 Rana24

Address

Area 11 Fct Abuja
Abuja

Telephone

+2347032340606

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kankara Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kankara Post:

Share