Jaridar Arewa

Jaridar Arewa Jarida ce ta Online da za ta kawo maku ingantattun labarai na cikin gida Nijeriya, da kuma ƙasashen ƙetare.
(2)

Yadda shahararren Mawaƙin Kudu, Davido ya gabatar da wasan Kalankuwa na musamman yau Alhamis a garin Adamawa.
30/10/2025

Yadda shahararren Mawaƙin Kudu, Davido ya gabatar da wasan Kalankuwa na musamman yau Alhamis a garin Adamawa.

HOTUNA: Yadda sabbin Hafsoshin tsaron Nijeriya s**a karɓi ragamar k**a aiki a yau Alhamis 30 ga watan Oktoba, 2025.
30/10/2025

HOTUNA: Yadda sabbin Hafsoshin tsaron Nijeriya s**a karɓi ragamar k**a aiki a yau Alhamis 30 ga watan Oktoba, 2025.

Yadda Sabbin sarakunan da Gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed ya naɗa s**a kai gaisuwar bangirma ga mai martaba Sarkin Ba...
30/10/2025

Yadda Sabbin sarakunan da Gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed ya naɗa s**a kai gaisuwar bangirma ga mai martaba Sarkin Bauchi Dr. Rilwanu Sulaiman Adamu a yau Alhamis, a fadarsa da ke cikin garin Bauchi.

HOTUNA: Yadda aka gudanar da Jana'izar kwamandan kwamitin yaƙi da ƙwacen waya na jihar Kano Inuwa Salisu. An gudanar da ...
30/10/2025

HOTUNA: Yadda aka gudanar da Jana'izar kwamandan kwamitin yaƙi da ƙwacen waya na jihar Kano Inuwa Salisu.

An gudanar da jana'izar na'izar ne a unguwar Sharada, tare da halartar gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da sauran jami'an gwamnati da ƴan uwa da abokan marigayin.

A daren ranar Talata ne aka zargi wasu ɓatagari da kai wa kwamandan hari tare da kashe shi a gidansa da ke Sharada.

30/10/2025

Jawabin ƙarshe na kwamandan kwamitin yaƙi da ƙwacen waya na jihar Kano Inuwa Salisu, kafin a kashe shi.

30/10/2025

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da sabon babban hafsan sojan ƙasa na Najeriya Lt Gen Wahidi Shaibu yanzu haka a fadar shugaban ƙasa.

Hukumar NELFUND ta raba fiye da Naira biliyan 116 ga dalibai sama da dubu 600 tun bayan kaddamar da shirin lamunin a Naj...
30/10/2025

Hukumar NELFUND ta raba fiye da Naira biliyan 116 ga dalibai sama da dubu 600 tun bayan kaddamar da shirin lamunin a Najeriya

Hukumar bayar da lamunin karatu ta Najeriya (NELFUND) ta ce ta raba sama da Naira Biliyan 116.4 ga dalibai fiye da 624,000 tun bayan kaddamar da shirin lamunin karatu a ranar 24 ga Mayu, 2024.

A cewar rahoton da hukumar ta fitar a shafinta na X (Twitter) a ranar Talata, 28 ga Oktoba, NELFUND ta karɓi fiye da rejistar ɗalibai 929,000, inda sama da 624,000 daga cikinsu s**a amfana da shirin.

Rahoton ya nuna cewa an amince da sabbin masu rejista 12,398, adadin da ya kai ƙarin kaso 1.4 cikin 100 idan aka kwatanta da rahoton baya.

Hukumar ta kuma bayyana cewa daga cikin kudaden da aka rarraba, An biya Naira Biliyan 65.3 kai tsaye ga makarantu 239 a fadin ƙasar a matsayin kudin makaranta, yayin da aka bada Naira Biliyan 51.1 ga dalibai a matsayin kudin walwala da abinci, jimillar kudin ya k**a Naira Biliyan 116.4 zuwa yanzu.

A wani bangare na sanarwar, NELFUND ta bayyana bude sabon shafin neman lamunin karatu domin zangon karatu na 2025/2026, wadda za a bude daga Alhamis, 23 ga Oktoba, zuwa Asabar, 31 ga Janairu, 2026.

A cewar darektan sadarwa na hukumar, Oseyemi Oluwatuyi, sabbin masu neman lamuni za su iya amfani da lambar shiga jami’a (admission number) ko lambar JAMB wajen cikawa, maimakon lambar dalibi (matric number).

Hukumar NELFUND dai an kafa ta ne bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan dokar kafa shirin lamunin dalibai a watan Afrilu 2024. Shirin yana bai wa daliban da ke karatu a makarantu na gwamnati damar samun lamuni ba tare da ruwa ba, domin biyan kudin makaranta da kuma samun kuɗin abinci yayin karatu.

Manufar shirin ita ce rage cikas na kudi da ke hana matasa shiga manyan makarantu da kuma bunkasa damar ilimi ga ‘ya’yan talakawa.

Ana sa ran daliban da s**a ci gajiyar shirin za su fara biyan lamunin bayan sun sami aikin yi da zarar sun kammala karatunsu.

CDS: Ba zan iya nesanta kaina da matsalolin sojoji ba, amma zan kawo sauye-sauye masu kyau — O Oluyede Shugaban hafsan t...
30/10/2025

CDS: Ba zan iya nesanta kaina da matsalolin sojoji ba, amma zan kawo sauye-sauye masu kyau — O Oluyede

Shugaban hafsan tsaron ƙasa mai jiran gado, Olufemi Oluyede, ya ce zai kawo sauye-sauye masu amfani ga rundunonin tsaron Najeriya.

Yayin da yake magana a ranar Laraba a birnin Abuja lokacin da majalisar wakilai ta gudanar da tantancewarsa ta haɗin gwiwa tsakanin kwamitocin tsaro, na ruwa, na ƙasa da kuma na sama, Oluyede ya amince cewa ba zai iya raba kansa da ƙalubalen da dakarun sojojin ƙasar ke fuskanta ba — kasancewar ya shafe shekaru da dama yana aiki a cikin rundunar.

Sai dai ya yi alkawarin cewa zai kawo gyare-gyare na gaske da zasu taimaka wajen inganta harkokin tsaro a ƙasar.

ATP Hausa

Shugaba Bola Tinubu ya amince da kafa harajin shigo da kayayyaki na ad-valorem kashi 15 cikin 100 kan shigo da man fetur...
30/10/2025

Shugaba Bola Tinubu ya amince da kafa harajin shigo da kayayyaki na ad-valorem kashi 15 cikin 100 kan shigo da man fetur da dizil zuwa Najeriya.

An kaddamar da wannan tsari ne domin kare masana’antun sarrafa man cikin gida da kuma daidaita kasuwar man fetur, sai dai ana iya samun ƙarin farashi a tashar sayar da man (pump price).

A cikin wata wasika mai kwanan wata 21 ga Oktoba, 2025, da aka bayyana ga jama’a a ranar 30 ga Oktoba, 2025, wacce aka aikawa Hukumar Tara Haraji ta Ƙasa (FIRS) da Hukumar Kula da Masana’antar Mai ta Tsakiya da Ƙasa (NMDPRA), Tinubu ya umarci a fara aiwatar da kudirin nan take a matsayin wani ɓangare na abin da gwamnati ta kira “tsarin harajin shigo da kayayyaki mai bin kasuwar man.”

Wasikar, wacce Sakataren Shugaban Kasa na Musamman, Damilotun Aderemi ya sanya wa hannu, ta bayyana amincewar Shugaban kasa bayan shawarar da Shugaban Hukumar FIRS, Zacch Adedeji, ya gabatar.

Shawarwarin sun nemi a fara amfani da harajin kashi 15 cikin 100 bisa farashi, inshora da kudin jigilar kayayyaki (CIF) na man fetur da dizil da ake shigo da su, domin daidaita kudin shigo da kaya da yanayin kasuwar cikin gida.

A cikin takardarsa zuwa ga Shugaban Kasa, Adedeji ya bayyana cewa wannan mataki wani bangare ne na ci gaba da ake yi na farfado da masu tace mai na cikin gida, tabbatar da daidaiton farashi, da kuma karfafa tattalin arzikin mai da ke dogaro da naira domin cika manufofin gwamnatin “Renewed Hope Agenda” na tsaron mak**ashi da dorewar kudaden gwamnati.

A cewar hasashen da ke cikin wasikar, harajin shigo da kaya na kashi 15 cikin 100 na iya karawa farashin shigo da lita daya na man fetur kimanin naira 99.72.

DA DUMI-DUMI: Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta amince da ƙirƙirar sababbin ƙananan hukumomi guda 29 daga cikin guda 20 ...
30/10/2025

DA DUMI-DUMI: Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta amince da ƙirƙirar sababbin ƙananan hukumomi guda 29 daga cikin guda 20 da ake da su a halin yanzu.

Wannan kuduri tuni majalisar ta karanta shi daga karatu na farko zuwa na ƙarshe, sannan ta tura shi zuwa kwamitin da ya dace domin duba yiwuwar aiwatar da shi.

Ina masu tafiye-tafiye nan ina ne a Najeriya?
30/10/2025

Ina masu tafiye-tafiye nan ina ne a Najeriya?

DA ƊUMI-ƊUMI: Farashin Kayan Abinci Na Ƙara Sauƙi A Nijeriya Yayin Da Gwamnati Ke Samun Cigaba A Fannin Tattalin ArzikiR...
30/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Farashin Kayan Abinci Na Ƙara Sauƙi A Nijeriya Yayin Da Gwamnati Ke Samun Cigaba A Fannin Tattalin Arziki

Rahotanni daga jihohin Arewa maso Yamma na nuna cewa farashin kayan abinci ya fara raguwa a kasuwanni sak**akon girbin damina mai albarka da manoma s**a samu a bana. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnati ke ci gaba da aiwatar da manufofin tallafawa harkar noma da kuma tabbatar da wadatar abinci a ƙasar.

A jihohin Kaduna, Kano da Katsina, manoma sun tabbatar da cewa an samu kyakkyawan girbi na hatsi, tumatir, dawa, gero da shinkafa, abin da ya janyo farashin kayan abinci ya ragu sosai idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

A kasuwannin Kaduna misali, buhun shinkafa na kilo 50 da ake sayarwa a kan Naira 100,000 a baya, yanzu ya koma tsakanin Naira 50,000 zuwa Naira 63,000. Haka kuma farashin kwandon tumatir ya sauka daga Naira 120,000 zuwa Naira 35,000.

Wani ɗan kasuwa a Dawanau, Alhaji Bala Ali, ya tabbatar da cewa “yawan amfanin gona daga kauyuka ya ƙaru sosai, abin da ya taimaka wajen daidaita farashin abinci da kuma tabbatar da wadatar kayan masarufi a kasuwa.”

A jihar Kano, rahotanni sun ce yawancin manoma sun samu gagarumin girbi saboda yanayin ruwan sama da ya yi daidai da lokacin noma. Wasu manoma ma sun yaba da shirin Special Agro-Industrial Processing Zone (SAPZ) da s**a ce ya taimaka wajen samun iri da dabarun noma na zamani.

Wani manomi a Bebeji, Malam Audu Muzammil, ya ce, “Ruwan sama ya yi wadata kuma kwari sun yi ƙasa matuƙa. Daman abinda ya rage mana shi ne adana kayanmu yadda ya k**ata. Amma girbi ya yi albarka sosai.”

A jihar Katsina kuwa, duk da cewa wasu manoma sun koka da tsadar takin zamani, suna murna da cewa farashin kayan abinci ya ragu, abin da ya sa mutane da dama ke iya siyan abinci cikin sauƙi.

Malam Kabir Sabiu, wani manomi daga Katsina, ya ce “duk da cewa mun yi asara saboda farashi ya fadi, muna godewa Allah saboda jama’a da dama yanzu suna iya siyan abinci cikin rahusa. Wannan ma wata ni’ima ce.”

Masana tattalin arziki na cewa wannan saukin farashin abinci alama ce ta daidaituwar kasuwa da kuma nasarar da ake samu daga manufofin gwamnati na inganta noma, samar da kayan aikin gona da kuma rage dogaro da abinci daga ƙasashen waje.

Gwamnati dai ta bayyana cewa za ta ci gaba da tallafawa manoma ta hanyar samar da kayayyakin ajiyar amfanin gona, rarraba iri da takin zamani a farashi mai rahusa da kuma inganta tsaro a yankunan karkara domin karfafa noman cikin gida.

Da dama daga cikin ‘yan kasa sun bayyana farin ciki da saukar farashin kayan abinci, musamman bayan dogon lokaci da ake fama da hauhawar farashi.

“Yanzu muna ganin canji a zahiri,” in ji wata magidanciya a Kano, Hajiya Fatima Sani.

“Tumatir, shinkafa, wake, duk sun yi sauƙi. Allah ya kara albarka ga manoma da gwamnati.” Inji ta.

Masu lura da al’amuran tattalin arziki na cewa idan gwamnati ta ci gaba da wannan tsarin, akwai yiwuwar farashin abinci zai ci gaba da daidaituwa kuma hakan zai taimaka wajen rage matsin tattalin arziki ga ‘yan ƙasa.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Arewa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Arewa:

Share

Category