Jaridar Arewa

Jaridar Arewa Jarida ce ta Online da zata kawo maku ingantattun labarai na cikin gida Nijeriya, da ƙasashen ƙetare. 👉 +2349124099064.
(2)

Yadda Gwamnan jihar Nasarawa Abdullahi Sule da jiga-jigan Gwamnati s**a gudanar da wasan sada zumunci na kwallon kafa a ...
01/10/2025

Yadda Gwamnan jihar Nasarawa Abdullahi Sule da jiga-jigan Gwamnati s**a gudanar da wasan sada zumunci na kwallon kafa a filin wasa na Lafia Townshi, a ranar bikin cika shekaru 65 da samun ‘Yancin kan Nijeriya.

Wasan ya tattaro jiga-jigan ‘yan siyasa da kuma sarakunan gargajiya ciki har da Mai Shari’a Sidi Bage Muhammad I, Sarkin Lafia da kuma shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Nasarawa, da dai sauransu.

HOTUNA: Sarki Sunusi na biyu a wajen bikin murnar cika shekaru 65 da samun 'yancin kan Najeriya yau a birnin Kano.
01/10/2025

HOTUNA: Sarki Sunusi na biyu a wajen bikin murnar cika shekaru 65 da samun 'yancin kan Najeriya yau a birnin Kano.

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Kano ta dakatar da Malam Lawan Triumph daga yin wa'azi Majalisar Shura da gwamnatin Kano ta kafa...
01/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Kano ta dakatar da Malam Lawan Triumph daga yin wa'azi

Majalisar Shura da gwamnatin Kano ta kafa ya sanar da dakatar da Malam Lawan Shuaibu Triumph daga yin wa'azi.

A wani taron manema labarai da Sakataren majalisar, Alhaji Shehu Wada Sagagi ya yi a yau Laraba, ya ce an dakatar da Malam Lawan ne domin bashi damar ya zo gaban majalisar ya kare kan sa daga zarge-zargen da ake yi masa na yin kalaman ɓatanci ga Ma'aiki.

A cewar Sagagi, an dakatar da Malam Lawan har sai an kammala bincike da jin ta bakin sa a matakin Majalisar ta shura.

Ya kuma yi kira ga ƴan siyasa da su guji tsoma baki a batun, inda ya bukaci da a kyale kwamitin ya kammala aikin sa.

Sagagi ya tabbatar da cewa Majalisar za ta yi aiki tsakani da Allah ba tare da don rai ko rashin adalci ba.

Daily Nigerian

01/10/2025

Yaron da ya lashe gwarzon ranar samun ‘yancin kai a Nijeriya, a jihar Kano.

🎥: Sardauna

01/10/2025

TIRƘASHI: Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya buƙaci Shugaba Tinubu ya cire Kwamishinan ‘yansandan jihar Kano.

01/10/2025

𝗞𝗮𝗺𝗳𝗮𝗻𝗶𝗻 𝗗𝗮𝘁𝗮 N𝗮 𝗦𝗺𝗮𝗿𝘁𝘀𝘂𝗯 𝗛𝗮𝗿 𝗬𝗮𝗻𝘇𝘂 𝗦𝘂𝗻𝗮 𝗕𝗮𝗱𝗮
𝗠𝗧𝗡 𝗦𝗠𝗘𝟮
𝟭𝗚𝗕 ₦𝟰𝟱𝟬 𝗩𝗔𝗟𝗜𝗗 𝟯𝟬𝗗𝗔𝗬𝗦
𝟮𝗚𝗕 ₦𝟭𝟬𝟬𝟬 𝗩𝗔𝗟𝗜𝗗 𝟯𝟬𝗗𝗔𝗬𝗦

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga shugaba Tinubu da ya cire Kwamishinan ƴansanda na jihar Kano Gwamnan Jihar K...
01/10/2025

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga shugaba Tinubu da ya cire Kwamishinan ƴansanda na jihar Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta cire Kwamishinan Ƴansanda na jihar, Ibrahim Adamu Bakori.

Yusuf ya yi wannan kira ne a lokacin faretin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai, inda ya nuna rashin jin daɗinsa kan matakin kwamishinan na janye jami’an tsaro daga faretin ana daf da farawa a filin wasa na Sani Abacha a yau Laraba.

Gwamnan ya bayyana wannan mataki a matsayin wanda bai dace ba, tare da gargadin cewa hakan na iya zama barazana ga tsaro da zaman lafiya a lokacin da ake gudanar da muhimmin bikin kasa.

Ƙarin bayani na nan tafe...

Babban dattijo kuma jigon siyasa, Alhaji Tanko Yakasai, ya jaddada cewa Najeriya ta fi zama cikin yanayi mai kyau a yau ...
01/10/2025

Babban dattijo kuma jigon siyasa, Alhaji Tanko Yakasai, ya jaddada cewa Najeriya ta fi zama cikin yanayi mai kyau a yau fiye da yadda take kafin samun ’yancin kai, inda ya dage cewa ƙasar ta samu “ci gaba mai ban mamaki” a tsawon shekaru.

Yakasai ya bayyana haka ne a wata hira da aka yi da shi a shirin The Morning Show na tashar Arise Television a ranar Laraba, inda ɗan siyasar mai shekara 99 ya ce goyon bayansa ga gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ya samo asali ne daga jajircewar gwamnati wajen aiwatar da shirinta na gyara.

“A ganina, har zuwa yanzu abin yana tafiya da kyau, ina ganin gaba ɗaya mutane za su amince da ni cewa ya cimma abubuwa masu yawa a cikin lokacin da yake jan ragamar ƙasar,” in ji Yakasai.

Da aka tambaye shi dalilin da yasa har yanzu wasu ’yan Najeriya ke kallon rayuwar da ta gabata da sha’awa, idan har yanayin ƙasar a yanzu ya fi kyau kamar yadda ya bayyana, Yakasai ya ce sai waɗanda s**a rayu a ƙarƙashin mulkin mallaka ne za su fi fahimtar ci gaban da Najeriya ta samu.

INA ‘YAN KISHIN ƘASA: Ku turo mana hotunanku na bikin murnar cika shekaru 65 da samun ‘Yancin kan Nijeriya.
01/10/2025

INA ‘YAN KISHIN ƘASA: Ku turo mana hotunanku na bikin murnar cika shekaru 65 da samun ‘Yancin kan Nijeriya.

Najeriya @65: Mun samu gagarumin ci gaba a fannoni daban-daban cikin shekaru biyu da s**a gabata — TinubuShugaba Bola Ah...
01/10/2025

Najeriya @65: Mun samu gagarumin ci gaba a fannoni daban-daban cikin shekaru biyu da s**a gabata — Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ce gwamnatinsa ta samu gagarumin ci gaba a fannoni daban-daban cikin shekaru biyu da s**a gabata, duk da kalubalen tattalin arziki da tsaro da kasar ta fuskanta.

A jawabin da ya gabatar yayin bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai, shugaban ya ce manufofi da matakan da aka dauka sun fara sauya akalar tattalin arzikin kasar.

Karuwar kudaden shiga da rage bashi

Shugaba Tinubu ya bayyana cewa gwamnati ta samu karin kudaden shiga daga albarkatun da ba na man fetur ba, inda a bana kadai aka tara fiye da Naira tiriliyan 20. A cewar sa, adadin da ake kashewa wajen biyan bashin da ake ci ya ragu daga kusan kashi 97% zuwa kasa da 50%.

Farfaɗowar Tattalin arziki

Rahoton hukumar kididdiga ya nuna cewa tattalin arzikin Najeriya ya samu karuwar kashi 4.23% a zangon biyu na shekarar 2025, wanda ya zarce hasashen IMF na kashi 3.4. Haka kuma, hauhawar farashin kayayyaki ya sauka zuwa kashi 20.12% a watan Agusta, mafi karanci cikin shekaru uku.

Ci gaban masana’antu da kasuwanci

Shugaban ya ce Najeriya ta koma “net exporter”, wato tana sayar da kaya ga ƙasashen waje fiye da yadda take saya daga garesu. A cewar sa, kayayyakin da aka kera a gida Najeriya sun karu da kashi 173%, kuma kusan rabin abin da ake fitarwa yanzu ba man fetur ba ne.

Ya kara da cewa samar da danyen mai ya karu daga ganga kasa da miliyan daya a rana a shekarar 2023 zuwa ganga miliyan 1.68, yayin da a karon farko cikin shekaru 40 aka fara tace man fetur a cikin gida.

Asusun ajiyar ƙada da darajar Naira

Shugaba Tinubu ya ce asusun ajiyar kasar ya karu zuwa dala biliyan 42.03, mafi girma tun 2019. Ya kuma ce Naira ta farfado bayan rikicewar da ta shiga a 2023–2024, inda gibin farashin gwamnati da na kasuwar bayan-fage ya ragu sosai.

Shirye-shiryen tallafi ga talakawa

Gwamnati ta raba Naira biliyan 330 ga iyalai miliyan takwas a karkashin shirye-shiryen tallafin zamantakewa. Haka kuma, matasa sama da 153,000 sun amfana da lamunin Credicorp, yayin da daruruwan dubban dalibai s**a samu lamunin karatu ta ƙarƙashin shirin NELFUND.

Ababen more rayuwa

A bangaren gina kasa, gwamnati ta ce ta ci gaba da manyan ayyuka kamar layin dogo na Kaduna–Kano da Kano–Katsina–Maradi, titin Lagos–Calabar Coastal Highway, da kuma titin Sokoto–Badagry.

Tsaro

Shugaban ya ce jami’an tsaro na ci gaba da nasara a yaki da Boko Haram a Arewa maso Gabas da IPOB a Kudu maso Gabas. Ya ce zaman lafiya ya fara dawowa a wasu sassan da rikice-rikice s**a daɗe suna addabawa.

Matasa da kirkire-kirkire

Tinubu ya jaddada cewa gwamnati na cigaba da zuba jari a matasa ta hanyar shirye-shiryen inganta kirkire-kirkire da fasaha, ciki har da shirin iDICE programme, wanda zai tallafa wa masu fara sana’o’i ta intanet da kere-kere.

“Lokacin sabuwar Najeriya ya zo”

Shugaban ya ce duk da radadin da ’yan Najeriya s**a fuskanta sakamakon gyare-gyaren tattalin arziki, sakamakon ya fara bayyana.

“Ina tabbatar muku da cewa lokaci ya yi da Najeriya za ta zama kasa mai dogaro da kanta, mai arziki, da alfahari da kanta,” in ji shi.

YANZU-YANZU: Tura ta kai bango, Dangote da Kungiyar PENGASSAN sun cimma matsaya bayan kai ruwa Rana.Ga jerin abubuwa da ...
01/10/2025

YANZU-YANZU: Tura ta kai bango, Dangote da Kungiyar PENGASSAN sun cimma matsaya bayan kai ruwa Rana.

Ga jerin abubuwa da A cimma bayan zaman tattaunawa tsakanin Kamfanin Dangote da Kungiyar PENGASSAN.

1. Ɗangote zai dawo da ma'aikata da ya kora a kamfaninsa.

2. PENGASSAN za ta janye yajin aikin da ta yi niyyar shiga.

3. Ɗangote zai bar ma'aikatasa su shiga kungiyar.

4. Dole Ɗangote zai kare 'yancin ma'aikatasa.

HOTUNA: Bikin samun 'yancin kai na farko a Najeriya a ranar 1 ga Oktoba 1960, wanda aka gudanar a Tace Course dake Legas...
01/10/2025

HOTUNA: Bikin samun 'yancin kai na farko a Najeriya a ranar 1 ga Oktoba 1960, wanda aka gudanar a Tace Course dake Legas wanda yanzu aka sauya masa suna da Tafawa Barewa Square (TBS).

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Arewa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Arewa:

Share

Category