A R N Hausa

A R N Hausa A R N jarida ce da take yaɗa labarai da rahotanni gami da muhimman bayanan da s**a shafi nahiyar Africa.

Jibwis Nigeria Sun Miƙa Saƙon Ta'aziyyar Rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi Ƙungiyar ta wallafa a shafin ta cewa "A mada...
27/11/2025

Jibwis Nigeria Sun Miƙa Saƙon Ta'aziyyar Rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Ƙungiyar ta wallafa a shafin ta cewa "A madadin kungiyar Izala, Shugaba Sheikh Dr. Imam Abdullahi Bala Lau, na miƙa ta'aziyya ga ƴan uwa da iyalan Shehu Ɗahiru Bauchi da al-ummar jahar Bauchi dama ƙasa baki ɗaya, bisa rasuwar Shehu Ɗahiru Usman Bauchi.

Allah ka gafarta masa kura-kuransa, ka baiwa iyalansa dangana. Ameen."

Wallafar wacce ta sami sahalewar Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau
Shugaban JIBWIS Nigeria.

A R N Hausa



Rasuwar Sheikh Usman Ɗahiru Bauchi: Shaikh Ibraheem Zakzaky Ya Miƙa Ta'aziyyaDuniya ta yi jimami kan rasuwar babban mala...
27/11/2025

Rasuwar Sheikh Usman Ɗahiru Bauchi: Shaikh Ibraheem Zakzaky Ya Miƙa Ta'aziyya

Duniya ta yi jimami kan rasuwar babban malami Sheikh Usman Ɗahiru Bauchi (R), wanda ya rasu a yau, 06/Jimada 11/1447. Sheikh Bauchi ya kasance daya daga cikin fitattun malamai da dalibai da malamai da dama s**a amfana da iliminsa.

Jagoran Harkar Musulunci a Nigeria Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya mika sakon ta’aziyya ga iyalai da ɗaliban marigayin, yana mai roƙon Allah Ya saukar da rahamarsa, Ya sanya aljanna ta zama makomarsa, sannan Ya ba wa iyalansa da masoya haƙuri da juriyar wannan babban rashi.

Masoya da mabiyan Sheikh Bauchi sun nuna alhini kan rasuwar wannan babban malami, wanda ya yi fice wajen ilmantar da al’umma da tafiyar da harkokin addini.

A R N Hausa



Mulkin Soja Ya Ɗauki Iko: Guinea-Bissau Ta Shiga Sabon Yanayi na Tsaka-Mai-WuyaGuinea-Bissau na cigaba da kasancewa ciki...
27/11/2025

Mulkin Soja Ya Ɗauki Iko: Guinea-Bissau Ta Shiga Sabon Yanayi na Tsaka-Mai-Wuya

Guinea-Bissau na cigaba da kasancewa cikin yanayi na tsaka-mai-wuya bayan rundunar sojin ƙasar ta karɓi mulki, ta dakatar da ayyukan gwamnati kuma ta kafa sabuwar majalisar soja wadda ta karɓi ikon gudanar da al’amuran ƙasa. Wannan na zuwa ne bayan rikice-rikicen sak**akon zaɓen da ya haifar da tashin hankali a babban birnin Bissau.

Rundunar sojin ta sanar da Janar Horta N’Ta Na Man a matsayin shugaban rikon-gadin ƙasar, tare da rufe manyan ofisoshin gwamnati da shimfiɗa dokar hana fita yayin dare. Titunan Bissau sun kasance a cece-kuce, inda shaguna da bankuna s**a kasance rufe, yayin da dakarun soja ke sintiri domin hana duk wata zanga-zanga ko tashe-tashen hankula.

Duk da fara rufe iyakoki tun bayan kifar da mulkin, rahotanni sun tabbatar da cewa an sake buɗe su a yau domin sauƙaƙa zirga-zirgar hajoji da taimakon jinƙai. Sai dai har yanzu mutane na cikin fargaba, musamman ganin cewa an dakatar da fitar da sak**akon zaɓe da ake sa ran gabatarwa a yau.

Ƙasashen duniya da ƙungiyoyi k**ar AU da ECOWAS sun yi Allah-wadai da matakin sojojin, suna kiran a dawo da tsarin mulki da gaggawa. Har yanzu ba a bayyana tsawon lokacin da gwamnatin soja za ta yi a mulki ba, lamarin da ya bar makomar ƙasar cikin duhu.

Gidan jaridar A R N na cigaba da bibiyar ci gaban lamarin.

A R N Hausa



Fitacccen malamin addinin Musulunci a Nigeria, Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi ya rasu a cikin daren da ya gabata, k**ar yadd...
27/11/2025

Fitacccen malamin addinin Musulunci a Nigeria, Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi ya rasu a cikin daren da ya gabata, k**ar yadda wata majiya mai tushe ta tabbatar. Majiyar ta ce za a sanar da lokacin gudanar da jana'izar Sheshin malamin nan kusa.

A R N Hausa


Rahama Abdulmajid na Shirya Fim Kan Rayuwar Nana Asma’uRahama Abdulmajid, marubuciya kuma mai fafutuka a fannoni daban-d...
26/11/2025

Rahama Abdulmajid na Shirya Fim Kan Rayuwar Nana Asma’u

Rahama Abdulmajid, marubuciya kuma mai fafutuka a fannoni daban-daban, na shirin shirya fim mai taken “Nana Asma’u”, wanda ke magana ne kan rayuwar ɗiyar Mujaddadi Shehu Usmanu Danfodiyo. Wannan aikin ya zama wata gudunmawa ga al’umma wajen ilmantarwa da nishadantarwa, musamman a lokacin da ake fuskantar ƙalubale kan hakkin mata wajen karatu da kuma matsalolin sace su daga makarantu.

Rahama ta bayyana cewa: “Alhamdulillah, Mai Alfarma Sarkin Musulmi ya ba mu cikakken izini mu kammala aikin da muka fara shekaru hudu da s**a wuce. Haka nan, Masarautar ta ba mu shaida da halaccin fim ɗin, kuma Ma’aikatar Zuba Jari da Kasuwanci ta tabbatar da wannan izini a rubuce. Muna roƙon addu’o’in al’umma don samun nasara a aikin.”

Fim ɗin zai kasance wata hanya ta tunasar da mutane game da tarihin mata masu tasiri a rayuwar Musulunci, da kuma nuna irin gudunmawar da Nana Asma’u ta bayar wajen ilmantarwa da wayar da kan jama’a a zamaninta.

A R N Hausa


Ƴan uwa Musulmi, almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), sun gudanar da gangamin nuna adawa da yunkurin Amurka na rura wu...
26/11/2025

Ƴan uwa Musulmi, almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), sun gudanar da gangamin nuna adawa da yunkurin Amurka na rura wutar matsalar tsaro a Najeriya. Gangamin ya gudana a bakin ofishin Hukumar Kare Hakkin Bil’adama ta Kasa, dake Maitama, babban birnin tarayya Abuja. Masu zanga-zangar sun dauki wannan mataki ne domin bayyana rashin amincewarsu da tasirin kasashen waje kan harkokin tsaro a Najeriya.

A R N Hausa


Matasa Sun Yi Kira Ga Gwamnati Kan Matsalar Tsaro a Arewacin NigeriaAbuja, Najeriya – Daga Majalisar Dattawa, wasu matas...
26/11/2025

Matasa Sun Yi Kira Ga Gwamnati Kan Matsalar Tsaro a Arewacin Nigeria

Abuja, Najeriya – Daga Majalisar Dattawa, wasu matasa masu tasiri a social media sun yi kira ga Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan matsalar tsaro da ke addabar Najeriya, musamman a arewa. Sun yi amfani da kafafen sada zumunta wajen jawo hankalin gwamnati da al’umma, suna neman daukar gaggawa matakai domin kare rayuka da dukiyoyi.



A R N Hausa


Tirkashi: A Zariya dake jihar Kaduna Nigeria, wasu harsasai na bindiga sun fado daga wani buhu da ya zube daga mota a ku...
26/11/2025

Tirkashi: A Zariya dake jihar Kaduna Nigeria, wasu harsasai na bindiga sun fado daga wani buhu da ya zube daga mota a kusa da Jami’ar Ahmadu Bello Zariya (ABU), lamarin da ya tayar da hankalin jama’a a yankin.
Ganau sun ce direban motar ya ƙi tsayawa duk da ƙoƙarin da mutane s**a yi na nuna masa cewa kayansa sun fado. Da aka duba buhun, sai aka tarar da ƙananan al-burushi (bullets) ne a cikinsa.

Hukuma ba ta fitar da sanarwa ba tukuna, yayin da ake tambayar ina ake kai kayan? kuma na wanene su?

A R N Hausa


Juyin Mulki a Guinea-Bissau26 Nuwamba 2025An samu sabon rikicin siyasa a ƙasar Guinea-Bissau bayan da wani sashen sojin ...
26/11/2025

Juyin Mulki a Guinea-Bissau
26 Nuwamba 2025

An samu sabon rikicin siyasa a ƙasar Guinea-Bissau bayan da wani sashen sojin ƙasar ya k**a Shugaba Umaro Sissoco Embaló, lamarin da ya haifar da ruɗani tare da tunzura tashin hankali a babban birnin ƙasar.

Rahotanni daga cikin ƙasar sun tabbatar da cewa an ji harbe-harbe a daren Laraba kusa da fadar shugaban ƙasa da kuma ofishin hukumar zaɓe, alamar cewa sojoji sun ɗauki matakin da ya kai ga fatattakar jami’an tsaro da ke gadin wuraren gwamnati.

A cewar majiyoyi, shugaban ƙasar da wasu manyan jami’an gwamnati — ciki har da shugaban ma’aikatan tsaro, mataimakinsa da ministan cikin gida — sun shiga hannun sojoji ba tare da tsayayya ba. Embaló ya bayyana abin da ya faru da shi a matsayin “juyin mulki”, yana mai cewa an k**a shi ne saboda tashin hankali da ya biyo bayan zaben da aka gudanar ranar 23 Nuwamba 2025.

Wannan na zuwa ne a lokacin da ake zaman jiran sak**akon hukuma na zaben shugaban ƙasa, wanda ya gamu da cece-kuce tun kafin a kada kuri’a. Rashin tabbas kan wa’adin Embaló da ƙalubalen siyasa daga manyan jam’iyyu sun ƙara tayar da kura tun watanni kafin zabukan.

Guinea-Bissau dai na daga cikin ƙasashen yammacin Afirka da s**a fi fama da juyin mulki, ko ƙoƙarin yin hakan, tun bayan samun ’yancin kai. Wannan sabon rikici ya sake jefa ƙasar cikin yanayin da ba a san makomarsa ba, yayin da sojoji ba su fitar da cikakkiyar sanarwa kan matsayin ikon mulki ba tukuna.

A halin yanzu, ana ci gaba da samun tsoro da firgici a cikin al’umma, yayin da ake jiran wani bayani daga rundunar soji ko hukumomin ƙasar game da ko an kafa sabuwar gwamnati ko kuma za a komawa tsarin farar hula.

A ƙarshe. Lamarin ya bar Guinea-Bissau cikin yanayin rashin tabbas, inda ake ci gaba da sa ido kan yadda za a warware rikicin, musamman bayan k**a shugaban ƙasa da manyan jami’ansa. Gidan jaridar mu zai ci gaba da bin al’amuran domin kawo muku sabbin bayanai da zarar sun fito.

Hoton dake ƙasa, hoton ƙirƙira ne.

A R N Hausa


DALIBAN GGSS MAGA SUN KUƁUTAA yau an samu gagarumar nasara a Jihar Kebbi, bayan da wasu daga cikin daliban GGSS Maga da ...
25/11/2025

DALIBAN GGSS MAGA SUN KUƁUTA

A yau an samu gagarumar nasara a Jihar Kebbi, bayan da wasu daga cikin daliban GGSS Maga da aka sace s**a bayyana cikin tsaro.

A hoton da ya fito a safiyar yau, an ga ’yan matan suna cikin mota, cikin natsuwa da alamun farin ciki, wanda ke tabbatar da cewa sun kuɓuta daga hannun masu garkuwa.

Har yanzu ba a samu wata sanarwa daga jami’an tsaro, gwamnati ko mazauna yankin ba game da yadda aka ceto su ko halin da sauran dalibai suke ciki. Haka kuma ba a fayyace hanyar kubutarsu ba tukuna.

Duk da haka, bayyanar hoton ya kawo sauƙi da kwanciyar hankali ga mutane da dama, musamman iyaye da al’umma da s**a shafe kwanaki a cikin damuwa tun bayan sace su.

Ana jiran ƙarin bayani daga hukumomi a cikin sa’o’i masu zuwa.

A R N Hausa


Masu Garkuwa Sun Sace Mutum 10 A KanoA yau, 25 ga Nuwamba 2025, jihar Kano ta sake shiga damuwa bayan wani sabon harin m...
25/11/2025

Masu Garkuwa Sun Sace Mutum 10 A Kano

A yau, 25 ga Nuwamba 2025, jihar Kano ta sake shiga damuwa bayan wani sabon harin masu garkuwa da mutane a karamar hukumar Tsanyawa, inda rahotannin Leadership s**a tabbatar da cewa mutane 10 ne aka sace a daren jiya.

Wadanda s**a gani da idonsu sun bayyana cewa maharan sun shigo yankin da bindigogi, inda s**a tilasta wa mazauna shiga cikin tsoro, sannan s**a yi awon gaba da mutane goma daga gidajensu. Har yanzu ba a tabbatar da ko an samu jikkata ba, amma mazauna yankin sun ce harbe-harben ya daɗe kafin jami’an tsaro su isa.

Majiyar tsaro ta tabbatar da lamarin, tana mai cewa an tura karin jami’ai domin farautar maharan da kuma tabbatar da tsaron al’ummar yankin. Gwamnatin jihar Kano ta ce tana kan bibiyan lamarin tare da hukumomin tsaro na ƙasa domin ganin an kubutar da wadanda aka sace cikin koshin lafiya.

Harin ya kara tayar da hankalin jama’a musamman ganin cewa Tsanyawa na daga cikin yankunan da ake fama da matsalar satar mutane a cikin watannin baya-bayan nan.

Za mu ci gaba da bibiya, tare da kawo sabon bayani da zarar wani abu ya ƙara bayyana.

A R N Hausa


Yadda aka mayar da dandazon ɗalibai gidan iyayensu a jihar Bauchi, bayan Gwamnatin jihar ta rufe Makarantu sak**akon mat...
25/11/2025

Yadda aka mayar da dandazon ɗalibai gidan iyayensu a jihar Bauchi, bayan Gwamnatin jihar ta rufe Makarantu sak**akon matsalolin tsaron da ke addabar Arewacin ƙasar.

A R N Hausa


Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when A R N Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share