23/04/2025
🔴WAKILAI DAGA ƘUNGIYOYIN FULANI SUN ZIYARCI JAGORA (H)
Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)
Jagoran Harka Islamiyyah, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya karbi bakuncin wakilai daga ƙungiyoyin Fulani daban-daban a ranar Talata 24 ga Shawwal, 1446 (22/4/2025) a gidansa da ke Abuja.
A yayin jawabinsa, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya bayyana takaicinsa akan yadda aka fada wani tarkon maƙiya na bayyanar wasu mutane da sunan su Hausawa, kuma wai suna fada da Fulani, inda ya jaddada bayanin da ya saba akan cewa Hausa ba Kabila bace, face kasa ce wadda take da al’ummu da Kabilu daban-daban a cikinta, kuma Fulani bangarenta ne.
Ya bayyana takaicinsa akan yadda makiya s**a assasa rikicin Fulani tun da farko. Yace: “Da farko sun fara da (kauwana) ‘yan banga, suna bin Fulani suna kashewa, suna ƙwace shanun su. Sannan aka zo shi Bafullatani makiyayi wanda ba abin da ya sani banda kiwon shanunsa tun na gadon kakanni, yanzu an raba shi da su. Ana nan sai aka ce masa, kai kuma ga bindiga, ka rama. Shikenan sai bukata ta biya, aka fara kashe-kashe. Yanzu an ce wai Bafullatani Danta’adda ne, saboda haka in aka ganshi sai a far mashi da kisa.”
Yace: “Idan mu kaddara wani mutum sunansa Bafullatani, sai ya yi laifi. To in za ka rama gayya sai ka samu wani Bafullatanin ka rama a kansa? Sai a nemo wanda ya yi laifin ne a kai shi mahukunta (a hukunta shi). Amma ba haka ake ba, yanzu ana son a rika rigima ne kawai.”
Jagora yace: “Yanzu abinda ake kokari a kitsa mana wani manufa ne na daban, cewa wai a yi fada ne (tsakanin Hausa da Fulani), wai mu Kabilu ne, da yake da karfin tsiya ne, na san bai shiga zuciya ba.”
Ya kawo misalin yadda aka tashi garuruwa da dama da sunan wannan rikicin, musamman a garuruwan da ke yankin Funtua, Malumfashi da Giwa da sauransu, Jagora (H) ya bayyana cewa: “Shiri ne musamman na mutanen waje, da hadin bakin mahukuntan kasa, akan cewa a hana zama lafiya ne kawai a tarwatsa mutane, don su ba mutanen suke da bukata ba.”
Ya bayyana takaicinsa akan yadda ya zama duk wannan tashe-tashen hankulan da ake yi duk a Arewacin kasar nan ne. Yace: “Irin wannan kisan na rashin kangado da ake fama da shi, shi suke so a cigaba da yi a yamutsa komai, ya zama in kuka yamutse kuka rika kashe kanku, kuka talauce, ya zama yanzu babu kiwo, ba noma, babu kasuwanci, shikenan nan gaba dole ku fara tarwatsewa. Su kuma abin da suke bukata kenan, ya zama babu mutanen. Arzikin da ke karkashin kafafunmu suke so su diba. Abin da ya fi damunsu kenan.”
Shaikh Zakzaky ya bayyana cewa, sai dai a nemi mafita a wajen Allah Ta’ala. Ya kara da ba Fulanin shawarar cewa: “daidai gwargwado idan dai har mutum zai iya kauce ma inda zai fada cikin (fitinar) to ya kauce mata, ko da kuwa da barin yankin da yake ne ya je wani wuri, in fitinar ta je can, sai ya sake gaba.”
Yace: “Insha Allahu za mu fita daga rigima. Hanyar fita lafiyan shi ne kuma lallai a k**a addini, a rike addini, don mafitanmu kenan. Da shi ne muka samu daukaka, kuma da shi ne za mu samu mafita.”
Jagora (H) ya ja hankalin maziyartan akan su nisanci da’awar rarraban kawuka. “Duk wata da’awa da za a yi maka na raba ka da dan’uwanka, ko da a cikin addinin ne, ka kiyaye wannan da’awar. Duk wani wanda ya zo yace maka, yana koya maka addini ne, amma yace ka ga wancan dan uwan naka, mushiriki ne! To ka kiyaye wannan, ka yi nesa da shi, shi ma shaidan ne, yana so ya farraka mutane.”
Ya cigaba da cewa: “Da’awar rarraba ita ma sai ta shigo mana, ba na Kabila kawai ba, har a cikin addini ma sai aka shigo mana da da’awar rarraba, ana ce ma wasu, su ba Musulmi ba ne, ba za a bi su sallah ba, ba za a ci yankansu ba, ba za a aure su ba, ba za a yi kaza ba. Kai wannan irin abu! To shi wannan meye bambancinsa da na Kabilanci? Duk tafiyarsu daya ne, kuma (abin takaici ne) su yi shi da sunan addini.”
Ya jaddada musu cewa: “Duk wata da’awa da za ta raba ka da dan’uwanka, ka nesance ta, domin zumunci muhimmin abu ne.” Ya kara da cewa: “A kalamaina na baya nakan ce, an san Fulani da zumunci. To zumunci muhimmin abu ne. Wannan zumuncin ba sai na ce a rike ba, dama ana rikewa, sai in ce a cigaba da rike zumunci. Duk dan’uwanka dan’uwanka ne ko a ina yake.”
Har ila yau Shaikh Zakzaky ya neme su da su kara riko da kyawawan dabi’un da aka san Fulani da su, irin su fulako, kunya, da girmama nagaba. Yace: “Kyawawan dabi’u din nan a rike su, domin Manzon Allah (S) yana cewa: “An aiko ni ne don in cika kyawawan dabi’u.” Kuma Allah Ta’ala Ya yi masa shaida, yace; “Kai kam (wannan Manzo) kana bisa dabi’u kyawawa.” Saboda haka kyakkyawan dabi’a muhimmin abu ne; kunya, girmama na gaba, zumunci, da taimakon juna.”
Da yake tsokaci akan yadda azzalumai ke zalunci a sassa daban-daban na duniya, Shaikh Zakzaky ya tabo irin nau’in zaluncin da jami’an tsaron kasar nan suke yi a ‘yan tsakankanin nan. Yace: “Kun ji yadda kwanakin baya s**a yi niyyar za su zo su rutsa da mu a nan ko? Wai lokacin da aka yi Quds din nan, da s**a zo s**a bude mana wuta s**a kashe mutum wajen 27, shida s**a zo hannunmu, sauran k**ar 21 suna hannunsu sun ki su bayar. To kuma wai sai s**a ce, wai an harbe wani soja daga cikinsu, saboda haka wai muna da bindiga kenan. To yanzu za su zo unguwanninmu su kewaye a cikin dare da soja mota 120. Ba soja 120 ba, mota 120, za su kewaye wurare. Sai s**a ce kuma duk wanda s**a kashe za su tafi da gawar.”
Ya yi tambaya da cewa: “Don Allah in da gaske ne bindiga kuke nema, me zai sa kuce in kun kashe mutum za ku tafi da gawan? Kun zo za ku yi kisan kai ne ko?” Yace: “Wato za su zo ne su rutsa da mu su yi kisan kai su kwashe su tafi da su. Inda suke da karfi kenan wajen kashe wanda bai da komai!”
Shaikh Zakzaky yace: “Allah Ya kiyaye dai, amma ba yana nufin manufarsu na kisan kai sun bari ba ne, sai dai su canza salo. Suna nan ba su da wani tunani sai kitsa wannan. Ace sojan kasa, maimakon ya kare kasa, shi yana tunanin ya kashe mutanen kasar ne.”
Ya kara da cewa: “Kun ga yadda abin ban mamaki soja ne ya kwaci Nijar da Burkina da Mali, amma sojan Nijeriya shi lallai ba ya tunanin ya ceci kasar nan, yana tunanin ya kashe ‘yan kasar ne. Shi tunaninsa kullum ya zai yi kisan kai ne, ba tunanin ya zai yi ya ceci al’umma ba.”
Jagora ya bayyana halin da ake ciki a matsayin yanayin da bai da wata mafita in ba kiyayewar Allah Ta’ala ba. Ya bayyana fatansa ga mutane da cewa: “Fatan da muke yi, kar mutane su yarda a ingiza su izuwa kashe-kashe. Kar su yarda a ingiza su...”
Jagora (H) ya jaddadawa azzalumai cewa su sani, Allah ba azzalumin kowa ba ne. Kuma zalunci baya dauwama. Baya dauwama, ko da ya yi tsawo. Yace: “Bamu fata (zaluncin nasu) ya yi tsawo, amma dai zai kawo karshe.”
Yace: “Wani lokaci mukan nuna musu cewa za a zo karshe. Sai su ga k**ar ana musu barazana ne. Waiana musu barazana. Nace a’a, ku baku san Allah ba ne. Da kun san Allah za ku san cewa ko tarihi kuka karanta ba za ku taba ganin an taba zalunci ya dauwama ba. (Zalunci) ba ya dauwama, yana kawo karshe.”
24/Shawwal/1446
22/04/2025