A R N Hausa

A R N Hausa A R N jarida ce da take yaɗa labarai da rahotanni gami da muhimman bayanan da s**a shafi nahiyar Africa.
(1)

🔴Ga manyan labaran da s**a fi daukar hankali a Afrika a yau, 29 ga Afrilu, 2025.
29/04/2025

🔴Ga manyan labaran da s**a fi daukar hankali a Afrika a yau, 29 ga Afrilu, 2025.

🔴WAKILAI DAGA ƘUNGIYOYIN FULANI SUN ZIYARCI JAGORA (H)Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)Jagoran Harka Islamiyyah, ...
23/04/2025

🔴WAKILAI DAGA ƘUNGIYOYIN FULANI SUN ZIYARCI JAGORA (H)

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Jagoran Harka Islamiyyah, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya karbi bakuncin wakilai daga ƙungiyoyin Fulani daban-daban a ranar Talata 24 ga Shawwal, 1446 (22/4/2025) a gidansa da ke Abuja.

A yayin jawabinsa, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya bayyana takaicinsa akan yadda aka fada wani tarkon maƙiya na bayyanar wasu mutane da sunan su Hausawa, kuma wai suna fada da Fulani, inda ya jaddada bayanin da ya saba akan cewa Hausa ba Kabila bace, face kasa ce wadda take da al’ummu da Kabilu daban-daban a cikinta, kuma Fulani bangarenta ne.

Ya bayyana takaicinsa akan yadda makiya s**a assasa rikicin Fulani tun da farko. Yace: “Da farko sun fara da (kauwana) ‘yan banga, suna bin Fulani suna kashewa, suna ƙwace shanun su. Sannan aka zo shi Bafullatani makiyayi wanda ba abin da ya sani banda kiwon shanunsa tun na gadon kakanni, yanzu an raba shi da su. Ana nan sai aka ce masa, kai kuma ga bindiga, ka rama. Shikenan sai bukata ta biya, aka fara kashe-kashe. Yanzu an ce wai Bafullatani Danta’adda ne, saboda haka in aka ganshi sai a far mashi da kisa.”

Yace: “Idan mu kaddara wani mutum sunansa Bafullatani, sai ya yi laifi. To in za ka rama gayya sai ka samu wani Bafullatanin ka rama a kansa? Sai a nemo wanda ya yi laifin ne a kai shi mahukunta (a hukunta shi). Amma ba haka ake ba, yanzu ana son a rika rigima ne kawai.”

Jagora yace: “Yanzu abinda ake kokari a kitsa mana wani manufa ne na daban, cewa wai a yi fada ne (tsakanin Hausa da Fulani), wai mu Kabilu ne, da yake da karfin tsiya ne, na san bai shiga zuciya ba.”

Ya kawo misalin yadda aka tashi garuruwa da dama da sunan wannan rikicin, musamman a garuruwan da ke yankin Funtua, Malumfashi da Giwa da sauransu, Jagora (H) ya bayyana cewa: “Shiri ne musamman na mutanen waje, da hadin bakin mahukuntan kasa, akan cewa a hana zama lafiya ne kawai a tarwatsa mutane, don su ba mutanen suke da bukata ba.”

Ya bayyana takaicinsa akan yadda ya zama duk wannan tashe-tashen hankulan da ake yi duk a Arewacin kasar nan ne. Yace: “Irin wannan kisan na rashin kangado da ake fama da shi, shi suke so a cigaba da yi a yamutsa komai, ya zama in kuka yamutse kuka rika kashe kanku, kuka talauce, ya zama yanzu babu kiwo, ba noma, babu kasuwanci, shikenan nan gaba dole ku fara tarwatsewa. Su kuma abin da suke bukata kenan, ya zama babu mutanen. Arzikin da ke karkashin kafafunmu suke so su diba. Abin da ya fi damunsu kenan.”

Shaikh Zakzaky ya bayyana cewa, sai dai a nemi mafita a wajen Allah Ta’ala. Ya kara da ba Fulanin shawarar cewa: “daidai gwargwado idan dai har mutum zai iya kauce ma inda zai fada cikin (fitinar) to ya kauce mata, ko da kuwa da barin yankin da yake ne ya je wani wuri, in fitinar ta je can, sai ya sake gaba.”

Yace: “Insha Allahu za mu fita daga rigima. Hanyar fita lafiyan shi ne kuma lallai a k**a addini, a rike addini, don mafitanmu kenan. Da shi ne muka samu daukaka, kuma da shi ne za mu samu mafita.”

Jagora (H) ya ja hankalin maziyartan akan su nisanci da’awar rarraban kawuka. “Duk wata da’awa da za a yi maka na raba ka da dan’uwanka, ko da a cikin addinin ne, ka kiyaye wannan da’awar. Duk wani wanda ya zo yace maka, yana koya maka addini ne, amma yace ka ga wancan dan uwan naka, mushiriki ne! To ka kiyaye wannan, ka yi nesa da shi, shi ma shaidan ne, yana so ya farraka mutane.”

Ya cigaba da cewa: “Da’awar rarraba ita ma sai ta shigo mana, ba na Kabila kawai ba, har a cikin addini ma sai aka shigo mana da da’awar rarraba, ana ce ma wasu, su ba Musulmi ba ne, ba za a bi su sallah ba, ba za a ci yankansu ba, ba za a aure su ba, ba za a yi kaza ba. Kai wannan irin abu! To shi wannan meye bambancinsa da na Kabilanci? Duk tafiyarsu daya ne, kuma (abin takaici ne) su yi shi da sunan addini.”

Ya jaddada musu cewa: “Duk wata da’awa da za ta raba ka da dan’uwanka, ka nesance ta, domin zumunci muhimmin abu ne.” Ya kara da cewa: “A kalamaina na baya nakan ce, an san Fulani da zumunci. To zumunci muhimmin abu ne. Wannan zumuncin ba sai na ce a rike ba, dama ana rikewa, sai in ce a cigaba da rike zumunci. Duk dan’uwanka dan’uwanka ne ko a ina yake.”

Har ila yau Shaikh Zakzaky ya neme su da su kara riko da kyawawan dabi’un da aka san Fulani da su, irin su fulako, kunya, da girmama nagaba. Yace: “Kyawawan dabi’u din nan a rike su, domin Manzon Allah (S) yana cewa: “An aiko ni ne don in cika kyawawan dabi’u.” Kuma Allah Ta’ala Ya yi masa shaida, yace; “Kai kam (wannan Manzo) kana bisa dabi’u kyawawa.” Saboda haka kyakkyawan dabi’a muhimmin abu ne; kunya, girmama na gaba, zumunci, da taimakon juna.”

Da yake tsokaci akan yadda azzalumai ke zalunci a sassa daban-daban na duniya, Shaikh Zakzaky ya tabo irin nau’in zaluncin da jami’an tsaron kasar nan suke yi a ‘yan tsakankanin nan. Yace: “Kun ji yadda kwanakin baya s**a yi niyyar za su zo su rutsa da mu a nan ko? Wai lokacin da aka yi Quds din nan, da s**a zo s**a bude mana wuta s**a kashe mutum wajen 27, shida s**a zo hannunmu, sauran k**ar 21 suna hannunsu sun ki su bayar. To kuma wai sai s**a ce, wai an harbe wani soja daga cikinsu, saboda haka wai muna da bindiga kenan. To yanzu za su zo unguwanninmu su kewaye a cikin dare da soja mota 120. Ba soja 120 ba, mota 120, za su kewaye wurare. Sai s**a ce kuma duk wanda s**a kashe za su tafi da gawar.”

Ya yi tambaya da cewa: “Don Allah in da gaske ne bindiga kuke nema, me zai sa kuce in kun kashe mutum za ku tafi da gawan? Kun zo za ku yi kisan kai ne ko?” Yace: “Wato za su zo ne su rutsa da mu su yi kisan kai su kwashe su tafi da su. Inda suke da karfi kenan wajen kashe wanda bai da komai!”

Shaikh Zakzaky yace: “Allah Ya kiyaye dai, amma ba yana nufin manufarsu na kisan kai sun bari ba ne, sai dai su canza salo. Suna nan ba su da wani tunani sai kitsa wannan. Ace sojan kasa, maimakon ya kare kasa, shi yana tunanin ya kashe mutanen kasar ne.”

Ya kara da cewa: “Kun ga yadda abin ban mamaki soja ne ya kwaci Nijar da Burkina da Mali, amma sojan Nijeriya shi lallai ba ya tunanin ya ceci kasar nan, yana tunanin ya kashe ‘yan kasar ne. Shi tunaninsa kullum ya zai yi kisan kai ne, ba tunanin ya zai yi ya ceci al’umma ba.”

Jagora ya bayyana halin da ake ciki a matsayin yanayin da bai da wata mafita in ba kiyayewar Allah Ta’ala ba. Ya bayyana fatansa ga mutane da cewa: “Fatan da muke yi, kar mutane su yarda a ingiza su izuwa kashe-kashe. Kar su yarda a ingiza su...”

Jagora (H) ya jaddadawa azzalumai cewa su sani, Allah ba azzalumin kowa ba ne. Kuma zalunci baya dauwama. Baya dauwama, ko da ya yi tsawo. Yace: “Bamu fata (zaluncin nasu) ya yi tsawo, amma dai zai kawo karshe.”

Yace: “Wani lokaci mukan nuna musu cewa za a zo karshe. Sai su ga k**ar ana musu barazana ne. Waiana musu barazana. Nace a’a, ku baku san Allah ba ne. Da kun san Allah za ku san cewa ko tarihi kuka karanta ba za ku taba ganin an taba zalunci ya dauwama ba. (Zalunci) ba ya dauwama, yana kawo karshe.”






24/Shawwal/1446
22/04/2025

🔴MATALAR TSARO A NIGERIA | Ana kukan targaɗe; Wata sabuwar ƙungiyar ƴan ta'adda mai ikirarin jihadi da ake kira Mahmudu ...
23/04/2025

🔴MATALAR TSARO A NIGERIA | Ana kukan targaɗe; Wata sabuwar ƙungiyar ƴan ta'adda mai ikirarin jihadi da ake kira Mahmudu ta ɓulla a Nijeriya

Wata ƙungiyar masu iƙirarin jihadi da ake kira Mahmuda tana ci gaba da kafuwa da ƙara ƙarfi tare da addabar jama'a a wasu garuruwa na ƙananan hukumomin Kaiama da Baruten na jihar Kwara.

Bayanai sun ce ƴan ƙungiyar sun sami mafaka ne a gandun dajin Kainji Lake National Park, kuma daga can ne suke kai hare-hare a garuruwan da ke makwabtaka da dajin har ma da wasu sassa na jihar Neja.

Yanzu haka dai mutanen garuruwan da abin ya shafa suna ta yin hijira zuwa wasu wurare, domin guje wa ƙwazzabar ƴan ƙungiyar ta Mahmuda.

Mazauna yankin sun ce dama can ƴan ƙungiyar ta Mahmuda ta taɓa kafa sansani a ƙananan hukumomin Kaiama da Baruten, inda s**a nuna cewa babu ruwansu da mutanen gari kuma hakan ya sa mutanen s**a saki jiki da su.

Wani mazaunin yankin ya ce daga baya ne Mahmudawan s**a fara yawo da mak**ai suna k**a mutanen gari da kuma yanke masu hukunci har ma da kashe wasu. ''Sun fi shekara 3 da fara bayyana''

Ya ƙara da cewa a wannan karon da s**a dawo ''Daga gabas da gari zuwa yamma, mutum baya da halin zuwa gona mai nisan kilomita biyu haka. Gaba ɗaya na tsorata, kashi 50 cikin ɗari na mutanen gari sun gudu''

Haka nan kuma ƙungiyar ta Mahmuda ta haramta wa mutanen Kaiama da Baruten noma ''Kashi 95 cikin 100 na mutanen um manoma ne, to yanzu sun ce bamu da damar yin noman ka ga dai yanzu mutuwa ta fuskance um, ba ma yunwa ba.''

Dokta Kabir Adamu, shuagaban kamfanin Beacon mai nazari da bincike kan harkar tsaro a Najeriya da yankin Sahel, ya ce a fahimtarsu wannan ƙungiya ta Mahmuda tana da alaka da kungiyar ISWAP: ''Kusan aƙidar su da abubuwan da suke ƙoƙarin yi y azo ɗaya. Mu a yadda muke kallon abin bai canza komai ba''

Ya yi bayanin cewa dama can akwai irin waɗannan ƙungiyoyi a dajin wannan yanki na jihar Kwara, amma sojoji suna fatattakar su, kuma wasu na sake ɓulla.

''Idan ba za ka manta ba a kwanakin baya akwai wata ƙungiya da ake cewa Darussalam, wadda ta yi ƙarfi sosai kafin daga baya sojoji s**a fattake ta daga yankin.''

Masanin tsaron yana ganin wajibi ne a tashi tsaye wajen yin amfani da ''dabarun bincike da amfani da ƙarfin soji ko kuma hanyar laluma, da kuma amfani da dokokin da s**a dace wajen zartar da hukunci a kan masu hannu a ciki'' domin ganin an murkushe wannan nau'i na ƙalubalen tsaro a Najeriya.

Katsina Daily News
A R N Hausa | A R N English
23/04/2025

🔴YANZU-YANZU | Ku kasance da sashin English na Jaridar A R N domin samun labarai da rahotanni gami da muhimman bayanan d...
17/04/2025

🔴YANZU-YANZU | Ku kasance da sashin English na Jaridar A R N domin samun labarai da rahotanni gami da muhimman bayanan da s**a shafi nahiyar Africa cikin harshen turanci.

Latsa shuɗin rubutun dake ƙasa domin zuwa ga shafin. ?A R N EnglishshshOmg

A R N Hausa | A R N English
17/04/2025

Kuyi Follow na A R N HAUSA | A R N English domin samun Ingantattun Labarai Duniya




Ten Unknown Facts About

1. Founding and History: BMW, Bayerische Motoren Werke AG, was founded in 1916 in Munich, Germany, initially producing aircraft engines. The company transitioned to motorcycle production in the 1920s and eventually to automobiles in the 1930s.

🔴DA ƊUMI-ƊUMI | Ministan Tsaron Saudiyya Khalid bin Salman ya gana da Shugaban Addini na Iran Sayyid Ali khamna'e yau a ...
17/04/2025

🔴DA ƊUMI-ƊUMI | Ministan Tsaron Saudiyya Khalid bin Salman ya gana da Shugaban Addini na Iran Sayyid Ali khamna'e yau a birnin Tehran dake Jamhuriyyar Musulunci ta Iran.

A R N Hausa | A R N English
17/04/2025

🔴LABARI | Wannan bawan Allahn ba ɗan shi'a bane kawai yaje Banex ne siyan Takalmi Ranar Jumu a sai kuma akayi daidai lok...
17/04/2025

🔴LABARI | Wannan bawan Allahn ba ɗan shi'a bane kawai yaje Banex ne siyan Takalmi Ranar Jumu a sai kuma akayi daidai lokacin ne Ranar Quds daga lokacin da akayi waqi'a ba a qara jin labarinsa ba sai kuma wani vedio yafita ashe yana cikin waðanda sojoji s**a k**a a ranar

Toh shekaranjiya ranar monday munje ziyarar yen'uwa a gidan yarin kuje zamu shiga kenan sai ga ɗan uwan wannan bawan Allahn sai yamin sallama yakirani gefe yake faɗamin Yazo duba ƴan uwansa ne tun lokacin da abin yafaru ba a ga ƴan uwan nasu ba kuma yaje duk inda ake tunanin ankai yen uwa yaje Sars da asibitoti da prisons duka amma babu labari shine yakarɓi number na yaturamin da hoton nasa yace dan Allah idan nasamu wani bayani insanar dashi nace toh insha Allah

Bayan yaturomin nikuma nasamu ðan uwa Muhammad Qasim naturamasa namasa bayani yace insha Allah duk abinda annan za a bincika

Sai gashi yanzunnan yamin text Ansamu GAWAR ɗan uwansa a gwagwalada Abin takaici da Ransa aka k**asu zakuga a vedion ma daqafarshi yashiga mota bayan ank**ashi ashe tafiya s**ayi s**a Harbe su gabaɗayansu s**a wurgar dasu Ansameshi ne a asibitin gwagwalada

Sunan sa babio Bello amma ana kiransa da Abdullahi bello

Daga Baqeer Naseer
A R N Hausa | A R N English
17/04/2025

🔴SUDAN | Tarayyar Turai da Birtaniya za su kara taimakon agaji ga SudanBirtaniya za ta shirya wani taro don magance riki...
15/04/2025

🔴SUDAN | Tarayyar Turai da Birtaniya za su kara taimakon agaji ga Sudan

Birtaniya za ta shirya wani taro don magance rikicin da ke faruwa a Sudan, duk da cewa gwamnatin Khartoum ta soki wannan taron saboda rashin gayyatar wakilan bangarorin da ke da hannu a rikicin.

A R N Hausa | A R N English
15/04/2025

🔴TAKARDAR BINCIKETake: Tasirin Yaƙin Gabas ta Tsakiya ga NajeriyaRubutawa: Hukumar gudanarwa ta gidan Jaridar A R N sash...
15/04/2025

🔴TAKARDAR BINCIKE

Take: Tasirin Yaƙin Gabas ta Tsakiya ga Najeriya

Rubutawa: Hukumar gudanarwa ta gidan Jaridar A R N sashin binciken muhimman bayanai.

Gabatarwa: Yaƙin da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya – musamman tsakanin Isra'ila da Falasdinu, da kuma rikice-rikicen da ke shafar kasashen Iran, Syria, da Yemen – na da tasiri mai zurfi ga kasashe da dama, ciki har da Najeriya. Wannan bincike zai bayyana manyan fannoni guda biyar da yaƙin ke yi wa Najeriya tasiri: tattalin arziki, tsaro, siyasa, jin kai, da addini.

1. Tasirin Tattalin Arziki: Najeriya na dogaro da man fetur a matsayin babban tushen kudin shiga. Yayin da rikice-rikice a Gabas ta Tsakiya ke faruwa, farashin danyen mai a kasuwannin duniya na hauhawa. Wannan kan haifar da hauhawar farashin kaya a gida, musamman kayayyakin man fetur da abinci. Hakan yana shafar rayuwar yau da kullum ta ‘yan Najeriya da kuma manufofin gwamnati na farfaɗo tattalin arziki.

2. Tasirin Tsaro: Kungiyoyin ta'addanci da ke aiki a Najeriya k**ar Boko Haram da ISWAP na iya samun tallafi kai tsaye ko na ruhaniya daga kungiyoyi masu ra'ayin jihadi a Gabas ta Tsakiya. Rikicin da ke can na iya zame wa masu ta'addanci a Najeriya wata hanyar samun kwarin gwiwa, fasaha, da dabarun yaki. Wannan yana kara dagula matsalar tsaro da ake fuskanta a Arewa maso Gabas da wasu sassan kasar.

3. Tasirin Siyasa: Rikicin Isra'ila da Falasdinu ya taba zamantakewa da ra'ayoyin jama'a a Najeriya. Yana janyo rarrabuwar ra'ayi tsakanin Musulmai da Kiristoci, wanda kan haifar da rikice-rikicen siyasa da addini a wasu lokuta. Hakazalika, gwamnati na shiga cikin kalubale wajen daidaita matsayi tsakanin goyon bayan jin kai da kuma tsare martabar diflomasiyya.

4. Tasirin Jin Kai: Yayin da rikice-rikice ke kara tsanani a Gabas ta Tsakiya, kasashen duniya da kungiyoyin agaji kan karkata hankalinsu zuwa can, suna barin Najeriya da karancin tallafi. Wannan yana da tasiri musamman a yankunan da ke fama da matsalar ‘yan gudun hijira da talauci, musamman Arewa maso Gabas.

5. Tasirin Addini da Al'adu: Saboda dimbin Musulmai da Kiristoci da ke Najeriya, rikicin Gabas ta Tsakiya na motsa jin daɗi da fushi a zukatan mutane. Wannan yana iya kawo baraka a tsakanin al'ummomi daban-daban idan ba a gudanar da shirye-shiryen wayar da kai da kwantar da hankali ba.

Kammalawa: Yaƙin Gabas ta Tsakiya na da tasiri kai tsaye da wanda ba kai tsaye ba a Najeriya. Don haka, yana da muhimmanci a samar da manufofi da matakan da za su taimaka wajen rage tasirin wannan rikici ga rayuwar ‘yan kasa. Wannan ya hada da karfafa tsaro, bunkasa tattalin arziki mai dogaro da kai, da kuma kokarin cusa zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin al'ummomi daban-daban.

A R N Hausa | A R N English
15/04/2025

🔴BABBAR MAGANA | Uwar gidan malamin ta baiyana hakan ne a yayin wani jawabin ta da ta gabatar ranar Alhamis ɗin da ta ga...
15/04/2025

🔴BABBAR MAGANA | Uwar gidan malamin ta baiyana hakan ne a yayin wani jawabin ta da ta gabatar ranar Alhamis ɗin da ta gabata, a wurin taron Mu'utamar na ƙasa da ƙasa da Harkar Musulunci ƙarƙashin jagorancin Shaikh Ibaraheem Zakzaky (H) ta shirya a birnin Kano dake Arewacin Nigeria, taro wanda shi ne ya kasance karo na huɗu, malama Zeenatuh ta ja kunnan gwamnatin Nigeria kan yunkurin kashe Shaikh Zakzaky (H) ta kowanne hali, ta cigaba da cewa zaman lafiyar Shehin malamin shi ne zaman lafiyar gwamnatin.

A R N Hausa | A R N English
15/04/2025

🔴HATSARIN MOTA | WANI MUTUM YA KONE KURMUS SAKAMAKON HATSARIN MOTA A JIHAR BAUCHI. Lamarin ya rutsa ne da waani mutum ma...
13/04/2025

🔴HATSARIN MOTA | WANI MUTUM YA KONE KURMUS SAKAMAKON HATSARIN MOTA A JIHAR BAUCHI.

Lamarin ya rutsa ne da waani mutum mai suna Usman Magaji dan kimanin shekaru 23 da haihuwa ya rasa ransa yayin da wasu mutum biyu s**a samu mabambamtan raunuka biyo bayan hatsarin manyan motoci guda biyu a garin Magama Gumau da ke karamar hukumar Toro a jihar Bauchi.

Da yake karin bayani cikin sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi, kakakin rundunar 'yan sandan jihar Bauchi CSP Muhammad Ahmad Wakil ya ce daya daga cikin manyan motocin makare da farar kasa kuma tana dauke da mutane hudu ta yi karo da wata motar ta dabam da ta lalace akan hanya wanda hakan ya jawo tashin wuta tare da kone dukkanin motocin biyu.

A R N Hausa | A R N English
13/04/2025

Ku kasance da sashin English na Jaridar A R N domin samun labarai da rahotanni gami da muhimman bayanan da s**a shafi na...
13/04/2025

Ku kasance da sashin English na Jaridar A R N domin samun labarai da rahotanni gami da muhimman bayanan da s**a shafi nahiyar Africa cikin harshen turanci.

Latsa shuɗin rubutun dake ƙasa domin zuwa ga shafin. 👇👇👇

https://www.facebook.com/share/1ANd7x9x8S/?mibextid=qi2Omg

A R N Hausa | A R N English
13/04/2025

🔴A yau Lahadi Jagoran Harkar Musulunci Sayyid Zakzaky (H) zai gabatar da jawabin kammala babban taron Mu'utamar na ƙasa ...
13/04/2025

🔴A yau Lahadi Jagoran Harkar Musulunci Sayyid Zakzaky (H) zai gabatar da jawabin kammala babban taron Mu'utamar na ƙasa da ƙasa da ake gabatarwa tun daga ranar Alhamis data gabata a garin Kano.

A R N Hausa | A R N English
13/04/2025

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when A R N Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share