26/11/2024
Abubuwa Guda 5 Idan Allah Ya Sa Yarinya Ta Mallake Su To Da Wuya Ta Bayar Da Ciwon Kai A Alaka Ta Mu'amalar Neman Aure Ko Bayan Aure
Daga Zoohrah Oummu Deederht
1) Saukin Hali da kwantar da kai da Tawadi'u (Jin ita ba komai bace kamar kowa take), da girmamawa, gami da qarancin Buri da hange hangen abin da bata da shi.
2) Tarbiyya irin ta Islama (ta kunshi komai me tsarki Halattacce).
3) Furuci: Harshe me sauki, wata akwai kaifin harshe, idan ta yi wata maganar ko barci sai da kyar.
4) Ilimin sanin Allah gwargwado da kokarin aiki da shi (wannan yana wiya, sai me rabo).
5) Iya zama da mutane wato mu'amala.
Na zauna da yara ýan mata da yawa, kuma duk inda na rayu da su, su shaida ne bana taba yin shiru kan abin da na ga zai cutar da yarinya a rayuwar ta na dabi'a, na kan so inga mace ta sauke duk wani hayaki da kuwwar shaiďan da take buga ta, na san ta haka ne kaďai za a ji dadin zama da ita duk inda ta shiga a duniya, don bata san inda Allah zai kai ta ta rayu ba, ba ta san kalar rayuwar da za ta tarar ba, ba ta san kalar mutanen da za ta rayu da su ba, ta haka ne za a ji daďin mu'amala da ita ta kusa ko ta nesa, kuma zaman ya yi karko.
Amma idan kina jin Ki very High! Wanna ciwo ne babba wanda idan ba'a sauke ba akwai damuwa a gaba.
Yana da kyau .ace da Aji na sosai, amma ba kyau mace da taurin kai da girman kai da ďagawa, akwai banbanci.
Allah Ya shirya mana zuri'a kan hanya madaidaiciya. Amin.