Hausa News Site

Hausa News Site Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Hausa News Site, Media/News Company, Maitama Street, Abuja.

An zargi shugaban PDP na Giade da karya dokar Hukumar zabe — ana kira ga jam’iyya ta dauki mataki AkansaDaga Comr. Mas’u...
22/10/2025

An zargi shugaban PDP na Giade da karya dokar Hukumar zabe — ana kira ga jam’iyya ta dauki mataki Akansa

Daga Comr. Mas’ud Ibrahim

Ana kira ga jam’iyyar PDP ta jihar Bauchi da ta dauki matakin gaggawa kan shugaban jam’iyyar a karamar hukumar Giade, bisa zargin karya dokokin hukumar zabe ta kasa (INEC) ta hanyar shirya rabon bilbord guda 10,000 da ke dauke da hoton Kwamishinan Kudi na jihar Bauchi, Dr Yakubu Adamu,

Rahotanni sun bayyana cewa an shirya rabon wadannan bilbord din ne a mako mai zuwa, kuma a halin yanzu suna jibge a ofishin jam’iyyar PDP na karamar hukumar Giade, abin da ke nuna cewa an kammala duk wasu shirye-shirye kafin lokacin da doka ta amince da fara kamfen Hakan ya sabawa ka'ida.

“IPAC ta gargadi jam’iyyun siyasa da su guji duk wani kamfen kafin lokacin da doka ta tanada. Amma abin takaici, sai ga shugaban PDP na karamar hukumar Giade yana shirya taruka da ayyukan kamfen, alhali kuwa hukumar zabe ba ta bada izini ba,” in ji majiyar.

A halin yanzu, ana kira ga uwar jam’iyyar PDP ta jihar Bauchi da ta sanya idanu a kan wannan al’amari, domin tabbatar da cewa shugabanni a dukkan matakai suna bin doka da ka’idoji, tare da guje wa aikata duk wani abu da zai iya janyo wa jam’iyyar hukunci daga hukumar zabe ta kasa (INEC).

Umar Lauya Ya Ayyana Neman Shugabancin NYCN, Na ƙasa. Ya Yi Alkawarin Hada Kan Matasa Don Gina KasaA wani gagarumin taro...
14/08/2025

Umar Lauya Ya Ayyana Neman Shugabancin NYCN, Na ƙasa. Ya Yi Alkawarin Hada Kan Matasa Don Gina Kasa

A wani gagarumin taron manema labarai da ya ja hankalin shugabanni, kungiyoyin matasa da masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na ƙasar, Comrade Umar Alhaji Lauya Hardawa ya ayyana aniyarsa ta tsayawa takarar Shugaban Ƙasa na National Youth Council of Nigeria (NYCN), inda ya yi alkawarin kawo ƙarshen rabuwar kai a ƙungiyar tare da mayar da hankali kan ci gaban matasa a fadin Najeriya.

Da yake jawabi a cibiyar taro da ke 17 Tougcourt Street, Wuse Zone 2, Abuja, Lauya ya yi kira da cewa lokaci ya yi da za a tashi tsaye domin sake farfaɗo da ƙungiyar matasa, yana mai jaddada taken sa na “Gina Matasa, Gina Ƙasa!”

“Idan ka gina matasa, ka gina ƙasa; idan ka lalata matasa, ka lalata ƙasa,” in ji shi, yana mai bayyana cewa manufarsa ba wai siyasar yau da kullum ba ce, illa makomar da za ta haɗa Matasa ɗaya da ƙasa ɗaya.

Tarihi da Ƙwarewa

An haife Lauya a Fadar Masarautar Hardawa, Misau, Jihar Bauchi, inda ya kammala karatun digiri a fannin Gudanar da Filaye (Estate Management) a Jami’ar Benin. Duk da damar bin sahun sana’a, ya sadaukar da rayuwarsa wajen inganta rayuwar matasa ta hanyar shirye-shiryen tallafin karatu, koyon sana’a, samar da ayyukan yi da shirye-shiryen zaman lafiya.

A matsayinsa na tsohon Shugaban NYCN Jihar Bauchi da kuma Shugaban Majalisar Tattaunawa ta Matasa ta jihar, Lauya ya kasance kan gaba wajen aiwatar da tsare-tsaren da s**a taɓa dubban rayuka a sassa daban-daban na jihar.

Kalubalen Da Ke Gaban Matasa

Ya yi nuni da rahotannin Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) da s**a nuna cewa kodayake rashin aikin yi a tsakanin matasa ya sauka zuwa kashi 6.5% a zangon biyu na shekarar 2024, sama da kashi 53% na matasa suna aiki a yanayi da ba zai iya ɗaukar nauyin rayuwarsu ba. Haka kuma, sama da matasa miliyan 18 a Najeriya ba sa zuwa makaranta, galibinsu saboda talauci, rashin tsaro da ƙarancin damar ilimi.

Ya kuma tabo matsalolin rashin tsaro da karancin abinci musamman a jihohin Arewa k**ar Katsina, da matsalolin tattalin arziki a kudancin ƙasar da ke tilasta matasa shiga laifi ko barin makaranta.

Shirin Sauyi

Lauya ya bayyana shirin sa na gyara NYCN daga cikin ta, yana mai cewa babban matakin farko shi ne haɗa kan ɓangarorin ƙungiyar ta hanyar tattaunawa bisa doka da tsarin mulki. Ya gabatar da manyan tsare-tsarensa guda shida da s**a haɗa da:

1. Ƙarfafa Matasa ta Hanyar Ayyuka da Sana’o’i

2. Wasanni a Matsayin Hanyar Haɗin Kai

3. Inganta Masana’antar Kirkire-kirkire da Nishaɗi

4. Farfaɗo da Shugabancin Dalibai

5. Tallafin Ilimi da Rancen Karatu

6. Rushe Ganuwar Ƙabilanci da Addini

Ya ƙara da cewa ƙwarewar sa a kwamitocin ƙasa da na ƙasa da ƙasa k**ar Kwamitin Yaƙi da Ta’addanci na ECOWAS da Shirin Shugaban Ƙasa na NEDC za su taimaka masa wajen juya waɗannan tsare-tsare zuwa aiki a aikace.

Kiran Goyon Baya

“Wannan ba nawa bane kaɗai, namu ne gaba ɗaya. Ina neman amincewarku ba wai kawai don in jagoranci ba, amma don in warkar da NYCN da sake gina ta,” in ji Lauya, yana mai jaddada cewa ƙungiyar matasa za ta zama mai ɗorewa da inganci, wadda za ta ba da cikakken gudunmawa wajen samar da sak**ako.

Ya rufe jawabin nasa da addu’o’i ga Najeriya da matasanta, yana jaddada cewa lokaci ya yi na haɗa ƙarfi da ƙarfi domin gina ƙasa mai cike da fata.

Umar Lauya
Falakin Hardawa
Ɗan takarar Shugaban Ƙasa NYCN

Gwamantin Jihar Borno A ƙarƙashin Jagorancin Kwamishinan mata Ta Jihar Borno Ta Shigar da ƙara A Kotu domin nemawa yarin...
22/03/2025

Gwamantin Jihar Borno A ƙarƙashin Jagorancin Kwamishinan mata Ta Jihar Borno Ta Shigar da ƙara A Kotu domin nemawa yarinyar da aka zalunta hakkin ta k**ar yadda doka Ta tanada

Gwamnatin Jihar Borno ta dau matakin gaggawa na shigar da kara a kan Mamman Sheriff da matarsa, wadanda aka k**a a faifan bidiyo suna azabtar da wata yarinya a Pompomari Bypass, Maiduguri. Bidiyon, wanda ya karade kafafen sada zumunta Bayan Ahmed Baba Dikwa ya wallafa shi, ya nuna Mamman Sheriff yana dukan yarinyar da karfi, Tare da goyon bayan matarsa. Rahotanni sun tabbatar da cewa an ci zarafin yarinyar ne kawai don ta shiga harabar Gidansu domin daukar mangoro bayan dawowa daga makaranta.

Bayan samun labarin lamarin, Hukumar Tsaro ta NSCDC, reshen Jihar Borno, ta gaggauta cafke Mamman Sheriff da matarsa, kafin daga bisani ma’aikatun da abin ya shafa su shiga cikin lamarin. Gwamnatin Jihar Borno ta tabbatar da cewa an dau matakin shari’a, inda aka hada gwiwa da Ma’aikatar Harkokin Mata da Cigaban Al’umma, Ma’aikatar Ilimi, da kuma Ma’aikatar Shari’a don tabbatar da adalci.

Ko da yake tana wajen gari, Kwamishiniyar Harkokin Mata da Cigaban Al’umma, Hon. Zuwaira Gambo, ta hanzarta tura tawaga karkashin jagorancin jami’ar kula da jin dadin al’umma, Asabe Muhammad (Yar Bauchi), don bibiyar lamarin. Tawagar ta ziyarci Hedikwatar NSCDC reshen Jihar Borno, inda s**a gana da Mataimakin Kwamandan Hukumar, Obi Ndubisi, da jami’in bincike, Peter, domin tabbatar da cewa ana tafiyar da shari’ar bisa doka.

An tabbatar da cewa Ma’aikatar Shari’a ta karbi shari’ar don gurfanar da wadanda ake zargi, yayin da Ma’aikatar Ilimi ta dau matakan da s**a dace dangane da lamarin. Hukumar NSCDC ta ba da tabbacin cewa za a tabbatar da hukunci mai tsanani ga wadanda s**a aikata wannan danyen aiki, domin adalci ya tabbata.

A gefe guda kuma, Gwamnatin Jihar Borno ta samar da taimakon gaggawa ga yarinyar da iyalanta. A halin yanzu tana samun kulawar lafiya a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), inda Dr. Lawan Bukar Alhaji ke daukar nauyin jinyarta. Bugu da kari, Hon. Zuwaira Gambo ta bayar da umarnin raba kayan tallafi ga iyayenta, wanda ya hada da **Dignity Kit, buhun shinkafa mai nauyin 25kg, buhu biyu na garri mai nauyin 25kg kowanne, da tallafin kudi.**

Iyayen yarinyar sun nuna matukar godiyarsu ga Gwamnatin Jihar Borno, Hukumar NSCDC, da ma’aikatun da s**a sa hannu wajen daukar mataki cikin gaggawa. Sun jinjinawa Gwamna Babagana Umara Zulum bisa jajircewarsa wajen kare hakkin yara da duk masu rauni a jihar, tare da tabbatar da cewa duk wanda ya aikata laifi irin wannan ba zai tsira ba.

Wannan matakin da Gwamnatin Jihar Borno ta dauka ya kara tabbatar da manufarta na rashin amincewa da cin zarafin yara, tare da aikawa da sako mai karfi cewa duk wanda ya aikata hakan ba zai kubuta ba. A karkashin jagorancin Mai Girma Gwamna Farfesa Babagana Umara Zulum, adalci zai ci gaba da tabbata a jihar.

KBC Hausa

Day 3Daga Karamar Hukumar Shira Cikin Garin Shira An cigaba Da Rabon Abincin Buda Baki Amadadin Alh Bala Wunti Maijama'a...
13/03/2025

Day 3

Daga Karamar Hukumar Shira Cikin Garin Shira An cigaba Da Rabon Abincin Buda Baki Amadadin Alh Bala Wunti Maijama'a Karkashin Jagorancin Hon Nura Usman Ganaru Wanda Alh Zaharaddeen Aminu Abubakar Dujiman Glade Ya ɗauki nauyi Yauma Kamar Kullum Mutane Da dama Ne S**a Samu Wannan Abincin.

Muna rokon Allah ya saka wa .Dr. Bala Wunti Maijama’a.da alkhairi, ya ba shi lada mai yawa bisa wannan aikin jin ƙai. Haka nan, muna mika godiya ta musamman ga Alhaji Zahraddeen Aminu Abubakar (Dujiman Giade)bisa kulawa da jajircewarsa a wannan gagarumin shiri. Allah ya ƙara daukaka.

Shugaban ma'aikatan Fadar Gwamnatin  Jihar Kaduna, Mallam Sani Liman Kila, ya samu gagarumar kyauta ta girmamawa a taron...
28/02/2025

Shugaban ma'aikatan Fadar Gwamnatin Jihar Kaduna, Mallam Sani Liman Kila, ya samu gagarumar kyauta ta girmamawa a taron GURARA TV Digital Summit and Awards da aka kammala kwanan nan.

An Gabatar da kyautar ne a ranar Asabar, 22 ga Fabrairu, 2025, a Arewa House, Kaduna, Inda manyan baki Daga ciki da wajen jihar s**a halarta.

Da yake karɓar kyautar a madadin Kakakin Gwamna, Manajan Daraktan Hukumar Inganta Harkokin Kasuwanci ta Jihar Kaduna (KADEDA), Hon. Iliya Anthony Timbuark, Ya jinjinawa Gurara TV bisa wannan Girmamawa. Ya jaddada cewa Kakakin Gwamna Mallam Sani Liman Kila ya sadaukar da kansa domin ci gaban Jihar Kaduna mai albarka.

Ɗaukar Nauyi Wallafa wa Daga Babban Mataimaki na Musamman kan Hulda da Jama'a na Gwamnan Jihar Kaduna Mal Uba Sani, MS Ustaz Mesittin

Address

Maitama Street
Abuja

Telephone

+2347067289098

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa News Site posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share