Jirgin Labarai

Jirgin Labarai Ku biyo mu domin samun labarai masu inganci wanda ke fadakarwa, ilmantarwa, da nishadantarwa.

Domin kawo mana labarai ko talla, a tuntube mu ta WhatsApp a wannan nomba: 09091131743.

Fuskokin Wasu Daga Cikin Tawagar 'Yan Wasan Jihar Kano Da S**a Ràsù Sak**akon Hadarin Mota Bayan Sun Dawo Daga Gasar Was...
31/05/2025

Fuskokin Wasu Daga Cikin Tawagar 'Yan Wasan Jihar Kano Da S**a Ràsù Sak**akon Hadarin Mota Bayan Sun Dawo Daga Gasar Wasanni ta Kasa wato National Sport Festival ta Najeriya a Jihar Ogun Da ke Kudu Maso Yammacin Kasar Bayan an Kammala Wasannin a Ranar Juma'a.

Motar da ke ɗauke da ƴanwasan Kano da masu horar da su a gasar wasanni ta ƙasa wato National Sport Festival ta Najeriya ta yi hatsarin a hanyar komawa gida, inda rahotanni s**a ce mutum 19 daga cikinsu sun rasu, sannan wasu sun jikkata.

Lamarin ya faru kimanin kilomita 50 zuwa Kano a yau Asabar bayan motar ta taso daga jihar Ogun da ke kudu maso yammacin ƙasar bayan an kammala wasannin a ranar Juma'a.

Gawawwakin da aka gano kenan daga cikin wadanda s**a rasa ransu a anbaliyar ruwa da akayi a anguwar Gangare dake garin M...
30/05/2025

Gawawwakin da aka gano kenan daga cikin wadanda s**a rasa ransu a anbaliyar ruwa da akayi a anguwar Gangare dake garin Mokwa cikin jihar Neja.

30/05/2025
Jami’an tsaro sun k**a mai garkuwa da mutane a filin jirgi yana shirin zuwa hajjiRahotanni sun ce jami’an tsaro sun k**a...
18/05/2025

Jami’an tsaro sun k**a mai garkuwa da mutane a filin jirgi yana shirin zuwa hajji

Rahotanni sun ce jami’an tsaro sun k**a wani da ake nema ruwa a jallo a sansanin mahajjata da ke Abuja.

Wata majiyar tsaro a sansanin ta tabbatar da kamen a ranar Lahadi.

Ya ce an k**a wanda ake zargin ne a lokacin da ake tantance alhazan da ke shirin zuwa Saudiyya ta jirgin sama domin aikin hajji.

Ya bayyana cewa wanda ake zargin Yahaya Zango yana zaune ne a Paikon -Kore a karamar hukumar Gwagwalada ta birnin tarayya Abuja.

Majiyar ta ce jami’an tsaro sun bayyana cewa ana nemansa ne, biyo bayan zargin sa da hannu a wasu sace-sacen mutane.

Wakilinmu ya tattaro cewa wanda ake zargin ya gudu ne bayan da jami’an tsaro s**a kaddamar da farautarsa.

ISWAP ta kashe manoma 50 a Borno'Yan ta'addar ISWAP sun kashe manoma akalla 50 a kauyen Malam Karanti da ke karamar huku...
17/05/2025

ISWAP ta kashe manoma 50 a Borno

'Yan ta'addar ISWAP sun kashe manoma akalla 50 a kauyen Malam Karanti da ke karamar hukumar Kukawa a jihar Borno.

An nakalto cewa, lamarin ya faru ne bayan da mayakan Boko Haram da ke hamayya da juna s**a yi wa manoman kwanton bauna a yankin da ISWAP ke iko da shi, mai tazarar kilomita 9 daga garin Baga a ranar Alhamis.

KASHE MAHAIFIYATA AKA YI A  ASIBITIN KOYARWA NA ABUBAKAR TAFAWA BALEWA BAUCHI (ATBUTH).Hakika duk wanda kwanansa ya kare...
13/05/2025

KASHE MAHAIFIYATA AKA YI A ASIBITIN KOYARWA NA ABUBAKAR TAFAWA BALEWA BAUCHI (ATBUTH).

Hakika duk wanda kwanansa ya kare babu mai iya kara masa ko da sekon daya, amma tabbas mutane da dama na rasa rayuwarsu a asibitoti sak**akon sakaci, musamman na wasu ma'aikatan jinya.
A ranar 6/2/2025 bayan shafe kwanaki 12 a ATBUTH Bauchi, an shiga da mahaifiyata sashen tace jini (Renal Center ) na wannan asibitin a karo na 4, kafin hakan a wannan ranar likitoci da dama sun zo sun duba ta tana zaune kan gado a hakan ni ma na dawo daga karbar sak**akon wani gwaji na same ta, a wannan lokacin muka yi hira sosai da ita, ta fadamin yadda s**a yi da likitocin da s**a duba ta sannan ta sa aka ba ni takardar da aka rubuta na zuwa tace jini. Daga nan na tafi biyan kudin wannan aikin, wanda kafin na dawo har an tafi da ita Renal Center.

Bayan na dawo sai na wuce warin Renal Center din, sai na samu dukkan yan uwana maza da mata a wari, sun ce wadda take aikin ta hana kowa zama a warinta. Ko a lokacin kuma na samu ita wannan ma'aikaciyar a waje tana ta tadi da wasu, alhali kuma ta daura maman namu kan na'urar tace jini. Ashe a wannan lokacin robar da jinin ke kai komo ta cikinta ta zare, duk jininta ya kwarare a kasa😭 ita kuwa tana waje tana tadin adashe da wasu.

Tace jinin da aka mata karo 3 na baya duk suna barin mutum daya a cikin mu ya zauna kusa da ita har a gama, amma a wannan ranar ita wannan ma'aikaciyar jinyar ta hana kowa zama acikin mu, wanda da akwai wani kusa da ita, a lokacin da hakan bai faru ba😭 Bayan ta gama zancen adashen ta koma sai ta samu maman namu cikin wani irin yanayi, daga nan sai kuma ta rugo waje neman yayun namu mata, suna shiga sai s**a iske ta a cikin wannan yanayi ga jinin a malale a kasa ana ta kokarin gogewa.

Daga nan sai s**a gaggauta mayar da ita dakin da take kwana (ward) cikin sauri. Abin mamakin ya k**ata a yi tatar jinin na tsawon a kalla awa 4 ne a wannan ranar, amma ko awa biyu bai kai ba s**a mayar da ita don sun hararo abin da zai iya faruwa kuma ba su son ta rasu a warinsu. Sannan duk tace jinin da aka mata sau 3 a baya, idan an gama sai mun jira attendant na tsawon lokaci kafin a samu a mayar da ita, amma a wannan ranar ma'aikacin jinya (nurse) da kansa ya turata a wheel chair zuwa ward din da take kwance wanda kasa da awa 1 da mayar da ita ta rasu.

Wannan dalilin ya sanya ya zama dole mu nemi hakkin mu, a kuma ba mu amsoshin wasu tambayoyi da muka mika gaban hukumar wannan asibitin.

Akwai mutane da dama da ke haduwa da ire-iren wannan sakaci na ma'aikatan jinya wanda ke zama sanadin rasa rayukansu.

Hatta likitoti da s**a duba ta a wannan rana sun yi mamakin cewa ta rasu a wannan lokacin ganin yadda s**a same ta da kuma yadda s**a bar ta a wannan lokacin. wanda muka musu bayanin abin da ya faru, s**a ce da sun yi bayanin abin da ya faru da a lokacin an nemi jini da gaggawa, Allahu Akbar, kwanan dai ya kare, amma ta sanadin sakaci na wannan ma'aikaciyar jinya wanda ba za mu taba yafewa ba.

Wallahi tsawon zamanmu, babu likita daya da zan ce ga laifinsa, suna sauraro, kulawa, mutuntawa da daraja marasa lafiya da masu jinyar su, haka kuma akwai dimbin ma'aikatan jinya masu kirki da sanin ya k**ata, Allah Ta'ala ya saka musu da alkairi.

Alhamdulillah tuni mahukuntan ATBUTH sun fara daukar mataki kan wannan lamari, muna kuma cigaba da bibiyar dukkan matakan da su ke dauka.

Babban abin damuwar shine babu wanda ya san waye irin wannan sakacin zai shafa gobe.

A karshe kuma babu abin da ke mana dadi duk da yadda muka shiga dimuwa, firgici da damuwar wannan rashin sai abuwa k**ar haka;

1. Kalmar shahadar da ta zama kalmar karshe da ta furta, wanda ba wanda suke kusa da ita ba, har wanda suke da dan tazara da ita sun shaida hakan.
2. Shaidar halayeanta da duk wanda suke alaka da ita s**a mata.
3. Yadda hatta wanda iya zaman asibitin ne ya hada mu, amma suma s**a nuna damuwa da alhininsu saboda halinta da s**a fahimta a dan karamin zaman da Allah ya hada mu da su.

A karshe ina addu'ar Allah Ta'ala ya gafarta mata ya mata rahama, ya yafe mata dukkan kura-kurenta, ya albarkaci bayanta, ya ba mu ikon koyi da halayenta, amin.

Ibrahim Abubakar Katagum
12/5/2025

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna Ya Rasu Turakin Dawakin Zazzau Kuma Mahaifin Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Alhaji Ramalan ...
12/05/2025

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna Ya Rasu

Turakin Dawakin Zazzau Kuma Mahaifin Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Alhaji Ramalan Yero Ya Rasu yau litinin.

Wannan shi ne ginin da ake zama ciki mafi girma a duniya. Yana garin Hangzhou dake kasar China. Sama da mutane dubu ashi...
12/05/2025

Wannan shi ne ginin da ake zama ciki mafi girma a duniya. Yana garin Hangzhou dake kasar China. Sama da mutane dubu ashirin ne ke zaune a ginin.

Dakarun sojin Najeriya sun yi nasarar hallaka mayakan Boko Haram masu yawa tare da kwace mak**ai jiya Lahadi a dajin Sam...
12/05/2025

Dakarun sojin Najeriya sun yi nasarar hallaka mayakan Boko Haram masu yawa tare da kwace mak**ai jiya Lahadi a dajin Sambisa dake jihar Borno.

Za mu koma aikin haƙo ɗanyen mai a arewacin Najeriya - NNPCLKimanin shekara biyu bayan ƙaddamar da aiki haƙo ɗanyen man ...
12/05/2025

Za mu koma aikin haƙo ɗanyen mai a arewacin Najeriya - NNPCL

Kimanin shekara biyu bayan ƙaddamar da aiki haƙo ɗanyen man fetur a kan iyakar jihohin Bauchi da Gombe - wanda tun daga wancan lokaci ba a ci gaba da aikin ba - a yanzu sabon shugaban kamfanin man fetur na Najeriya Bayo Ojulari ya fada wa BBC cewa za a koma kan aikin.

Aikin da aka ƙaddamar a gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da ta gabata, ya sanya al’ummar arewacin ƙasar sun fara kyakkyawar fatan cewa yankin zai bi sahun wasu yankunan ƙasar da ke samar da man fetur wanda tattalin arzikin ƙasar ya dogara a kai.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ƴan Najeriya suke cigaba da kokawa kan tsadar rayuwa, wadda ke da alaƙa tashin farashin man fetur a sanadiyar cire tallafin da gwamnati ke bayarwa a bangaren.

Tun a jawabin Shugaban Najeriya Bola Tinubu na farko bayan shan rantsuwar k**a mulki ne ya sanar da cire tallafin man fetur.

Wannan shine Kaftin Kamal wanda 'yan Boko Haram s**a kashe ranar Laraba a garin Izge dake karamar hukumar Gwoza a jihar ...
11/05/2025

Wannan shine Kaftin Kamal wanda 'yan Boko Haram s**a kashe ranar Laraba a garin Izge dake karamar hukumar Gwoza a jihar Borno.

EL-RUFAI DA PETER OBI SUN GANA A LANDAN KAN YADDA ZASU TUNKARI ZABEN 2027.
10/05/2025

EL-RUFAI DA PETER OBI SUN GANA A LANDAN KAN YADDA ZASU TUNKARI ZABEN 2027.

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jirgin Labarai posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jirgin Labarai:

Share