Hausa Daily Post

Hausa Daily Post Hausa Daily Post is an independent newspaper that broadcasts online in Hausa +2348036060236 .

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun Ya Yi Rashin Kaninsa, Malam IbrahimAllah Ya gafarta m...
30/10/2025

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun Ya Yi Rashin Kaninsa, Malam Ibrahim

Allah Ya gafarta masa.

Daga Khalid Yusuf Sambo

Gwamnatin Tinubu taku ce, Shettima ya faɗawa dattawan Arewa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya tabbatarwa Ƙun...
30/10/2025

Gwamnatin Tinubu taku ce, Shettima ya faɗawa dattawan Arewa

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya tabbatarwa Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa "Arewa Consultative Forum (ACF)" cewa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ba ta nuna wariya ga kowanne sashi na ƙasa ba, yana mai cewa shugaban ƙasa na kowa ne.

Ya kuma roƙi mambobin ƙungiyar da su dena yarda da ƙoƙarin masu tada fitina da ke son raba ƙasar, yana jaddada cewa wannan gwamnati ta su ce.

Shettima ya yi wannan roƙon ne lokacin da ya tarbi tawagar ACF a Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja, a jiya Laraba.

Ya ce lokaci ya yi da shugabannin Arewa za su haɗa kai wajen goyon bayan ƙoƙarin gwamnati na fitar da ƙasar daga matsalolin tattalin arziki da zamantakewa.

Ya gargadi cewa wasu masu rarrabuwar kai na amfani da addini da ƙabilanci don raba ƙasar, yana mai kira ga ACF da ta ƙi amincewa da irin waɗannan makirce-makirce.

Hon. Yusuf Suleiman ya karɓi ragamar aiki a ma’aikatar ilimin firamare da sakandare ta jihar KatsinaDaga: Abdulrazak Ahm...
30/10/2025

Hon. Yusuf Suleiman ya karɓi ragamar aiki a ma’aikatar ilimin firamare da sakandare ta jihar Katsina

Daga: Abdulrazak Ahmad Jibia

Ma’aikatar Ilimin Firamare da Sakandare ta Jihar Katsina ta gudanar da bikin mika ragamar aiki tsakanin sabon kwamishina, Hon. Yusuf Sulaiman Jibia, da tsohuwar kwamishina, Hajiya Zainab Musa Musawa, a dakin taron ma’aikatar ranar Alhamis, 30 ga Oktoba, 2025.

Jaridar Hausa Daily Post ta ruwaito cewa, wannan biki ya nuna sauyin jagoranci cikin lumana da nufin ci gaba da aiwatar da sauye-sauye da shirye-shiryen ci gaban da ake gudanarwa a fannin ilimi a jihar Katsina.

A jawabinsa, sabon kwamishinan, Hon. Yusuf Sulaiman Jibia, ya bayyana kudirinsa na yin aiki tukuru tare da hadin kan dukkan ma’aikatan ma’aikatar domin ciyar da harkar ilimi gaba. Ya kuma gode wa Gwamna Dikko Umar Radda bisa amincewa da ya nuna masa, tare da alkawarin mayar da hankali kan karfafa ilimin firamare, inganta jin dadin malamai, da kuma kyautata gine-ginen makarantu a fadin jihar.

Hon. Jibia ya bukaci Hajiya Zainab Musa Musawa da ta ci gaba da bayar da shawarwari da goyon baya domin dorewar nasarorin da aka cimma.

A nata bangaren, tsohuwar kwamishina Hajiya Zainab Musa Musawa, ta gode wa shugabanni da ma’aikatan ma’aikatar bisa hadin kai da goyon bayan da s**a nuna mata a lokacin aikinta. Ta bayyana wa’adinta a matsayin lokaci mai albarka wanda ya haifar da nasarori da dama, ciki har da sabunta manhajar karatu, gyaran makarantu, da horar da malamai. Hajiya Zainab ta yi addu’ar fatan alheri ga sabon kwamishinan tare da bayyana tabbacin cewa zai ci gaba da daga darajar ilimi a jihar Katsina.

Shi ma Shugaban Hukumar Ilimin Firamare ta Jihar Katsina (SUBEB), Dr. Kabir Magaji Gafia, ya yi maraba da sabon kwamishinan, inda ya bayyana kwarin gwiwa cewa kwarewarsa da jajircewarsa za su kawo sabuwar dama ga fannin ilimi. Ya tabbatar masa da cikakken goyon bayan hukumar wajen aiwatar da manufofi da za su inganta ilimi da tabbatar da samun damar koyo ga kowane yaro a jihar.

Shugaban Karamar Hukumar Jibia, Hon. Sirajo Ado, ya taya Hon. Yusuf Jibia murna bisa wannan sabon mukami, tare da yabawa Gwamna Radda bisa hangen nesansa na daga darajar Yusuf Jibia daga matsayin mai bai wa gwamna shawara na musamman zuwa kwamishina. Ya tabbatar da cewa babu shakka, harkar ilimi za ta samu gagarumar nasara a karkashin jagorancinsa.

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, shugabannin hukumomi, ‘yan siyasa, ‘yan kasuwa, dangi, da magoya baya da s**a halarta domin taya sabon kwamishinan murna.

Da dumi'dumi: 'yan bindiga sun kashe shugabannin Kauye tare da wasu mutun biyu a jihar Sokoto. Rikicin ‘yan bindiga ya s...
30/10/2025

Da dumi'dumi: 'yan bindiga sun kashe shugabannin Kauye tare da wasu mutun biyu a jihar Sokoto.

Rikicin ‘yan bindiga ya sake dabaibaye jihar Sokoto, bayan da wasu mahara s**a farmaki kauyen da ke ƙaramar hukumar Tangaza, inda s**a kashe shugaban kauye mai rikon ƙwarya da wasu mutum biyu.

Wata majiya daga yankin ta ce, ‘yan bindigar sun shiga kauyen ne da dare, suna harbe-harbe ba kakkautawa, s**a kashe mutanen kafin su tsere cikin daji.
Rahoton ya ce, shugaban kauyen wanda aka kashe, yana cikin waɗanda s**a himmatu wajen kafa ƙungiyar tsaro ta ƙauye domin kare jama’a daga irin wadannan hare-hare.

Lamarin ya tayar da hankalin mazauna yankin, inda wasu ke barin gidajensu saboda tsoron karin farmaki.
A cewar jami’an tsaro, an tura runduna ta musamman zuwa yankin domin dawo da doka da oda.

Masu sharhi na ganin lokaci ya yi da gwamnati za ta ƙara tsaurara matakan tsaro a arewacin ƙasar, domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

“Idan shugabanni na ƙauye har suna zama abin hari, to wane ne zai tsira?” inji wani dattijo daga Tangaza da ya roƙi a ɓoye sunansa.

Hausa daily Post

Da dumi'dumi: Sen Natasha sun shirya da Sen Akpabio har ta gayyace shi buɗe ayyuka a jihar Kogi.Sanata Natasha Akpoti-Ud...
30/10/2025

Da dumi'dumi: Sen Natasha sun shirya da Sen Akpabio har ta gayyace shi buɗe ayyuka a jihar Kogi.

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta sasanta da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, bayan wata rigima da ta jima. Ta aika masa da gayyata domin halartar kaddamar da ayyuka a Ihima, Kogi State, ranar Lahadi, don murnar cika shekaru biyu a majalisa.

A baya, an dakatar da ita na watanni shida saboda sabanin ra’ayi tsakaninta da Akpabio, amma yanzu alamu sun nuna sulhu da sabuwar fahimta a tsakaninsu.

ƙarshe: Siyasa kam, yau ana gaba — gobe ana juna.

Da dumi'dumi: Sojan Sama Ya Shirya Kashe Nuhu Ribadu A Yunkurin Juyin Mulki Da gwamnatin Shugaba Bola tinubu – RahotoWan...
30/10/2025

Da dumi'dumi: Sojan Sama Ya Shirya Kashe Nuhu Ribadu A Yunkurin Juyin Mulki Da gwamnatin Shugaba Bola tinubu – Rahoto

Wani rahoto na jaridar TheCable ya bayyana cewa wani jami’in sojin sama an shirya ya kashe mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, a wani yunkurin juyin mulki da aka hana faruwa.

Rahoton ya ce jami’in, wanda ake kira SB Adamu daga jihar Jigawa, an tura shi ofishin tsaron ƙasa (ONSA) watanni uku kafin a gano wannan shiri. An ce an tsara masa aikin musamman na kashe Ribadu yayin da wasu jami’an sojoji za su kai hari ga wasu manyan jami’an gwamnati.

Wani majiya daga cikin tsaro ya bayyana cewa, Adamu yana daga cikin waɗanda aka yi amfani da su wajen tattara bayanai a ofishin tsaron ƙasa domin sauƙaƙa aiwatar da wannan makirci.

Sai dai rundunar sojin sama da hedikwatar tsaro ba su tabbatar da wannan batu ba tukuna, domin bincike yana ci gaba a sirrance.

Rahoton ya ƙara cewa, an riga an k**a wasu da ake zargin suna da hannu a cikin wannan yunkuri, kuma ana ci gaba da tambayarsu domin gano yadda aka shirya komai daga farko.

“Tsaro shi ne ginshiƙin ƙasa, kuma duk wanda ya yi wasa da shi, yana wasa da makomar jama’a.”

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Aikin Tiyatar Cutar VVF a Jihar KatsinaGwamnan Jihar Katsina, Mal  Dikko Radda , Ph.D, CON, ...
30/10/2025

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Aikin Tiyatar Cutar VVF a Jihar Katsina

Gwamnan Jihar Katsina, Mal Dikko Radda , Ph.D, CON, ya kaddamar da Aikin Tiyatar Cutar Vesico-Vaginal Fistula (VVF) wanda Ma’aikatar Lafiya ta Jiha ta shirya, tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Harkokin Mata da First Bank of Nigeria Plc.

Shirin, wanda yake ɗaya daga cikin ayyukan Corporate Social Responsibility (CSR) na First Bank, zai aiwatar da tiyata kyauta ga mata masu fama da cutar VVF, tare da samar da tallafin kayan dogaro da kai domin taimaka musu wajen murmurewa da komawa rayuwa ta yau da kullum. Mata 100 zasu amfana da wannan shirin kuma an zakulosu daga ƙananun hukumomi 34 na faɗin jihar.

Gwamna Radda ya jinjinawa First Bank bisa goyon bayan da ta ke bai wa gwamnatin jiha wajen inganta harkar lafiya, tare da tabbatar da manufofin gwamnatinsa na inganta lafiyar mata da inganta rayuwarsu a cikin al’umma

Hausa daily Post

CBN zata fitar da sabbin takardun kuɗi na N10,000 da N20,000Wani sabon rahoton tattalin arziki da Quartus Economics ta w...
30/10/2025

CBN zata fitar da sabbin takardun kuɗi na N10,000 da N20,000

Wani sabon rahoton tattalin arziki da Quartus Economics ta wallafa ta bukaci Babban Bankin Najeriya (CBN) da ya fitar da sabbin takardun kuɗi masu ƙima mafi girma k**ar N10,000 da N20,000, domin saukaka ɗaukar kuɗin naira da kuma rage tsadar gudanar da harkokin a hannu.

Rahoton mai taken “Is Africa’s Eagle Stuck or Soaring Back to Life?” ya gargadi cewa ci gaba da raguwar ƙimar naira ya sanya takardar N1,000 — wacce ita ce mafi girma a halin yanzu ta zama ba ta da amfani sosai wajen sayayya.

“Domin dawo da sauƙin amfani da kuɗin naira, Najeriya na iya fitar da sabbin takardun N10,000 ko N20,000, ko kuma ta sake ƙirƙirar tsarin ƙimar kuɗinta gaba ɗaya,” in ji rahoton.

Masana sun bayyana cewa, takardar N5,000 da aka yi shirin fitarwa a shekarar 2012 yanzu daidai take da N50,000 a darajar yau, wanda ke nuna raguwar ƙimar gaske ta naira da kashi 94 cikin 100 cikin shekaru ashirin da s**a gabata.

DA ƊUMI-ƊUMI: An bayyana Samia Suluhu a matsayin wacce ta Lashe zaɓen Shugabar ƙasar Tanzaniya.
30/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: An bayyana Samia Suluhu a matsayin wacce ta Lashe zaɓen Shugabar ƙasar Tanzaniya.

‎Jerin  Sunayen Sojojin dake tsare bisa zargin juyin Mulki .‎1. Brigadier Janar Musa Abubakar Sadiq‎‎An haife shi a rana...
30/10/2025

‎Jerin Sunayen Sojojin dake tsare bisa zargin juyin Mulki .

‎1. Brigadier Janar Musa Abubakar Sadiq

‎An haife shi a ranar 3 ga Janairu, 1974. Yana da lambar aiki N/10321. Ya fara karatun soja a NDA daga 14 ga Agusta 1992 zuwa 20 ga Satumba 1997. Ana zargin shi ne jagoran shirin juyin mulkin.

‎Dan asalin jihar Nasarawa ne, kuma mamba ne na Regular Course 44. Ya zama kolonel a 2015 sannan brigadier janar a 2019. Yana daga Infantry Corps.

‎A watan Oktoba 2024, an taba tsare shi bisa zargin karkatar da kayan tallafin palliative na shinkafa da kuma sayar da kayan aikin soja, ciki har da injinan janareta da motocin aiki. Ya taɓa zama kwamandan 3rd Brigade, Kano da kuma Garrison Commander, 81 Division, Lagos.

‎2. Kolonel M.A. Ma’aji

‎Dan asalin jihar Neja (Nupe). An haife shi a 1 ga watan Maris, 1976, yana da lambar aiki N/10668. Ya fara koyon soja a 18 ga Agusta 1995 ya kammala a 16 ga Satumba 2000.

‎Ana zargin shi da kasancewa ɗaya daga cikin masu tsara shirin juyin mulkin. Yana daga Infantry Corps, kuma ya zama kolonel a 2017.

‎Ya kasance kwamandan 19 Battalion a Okitipupa, jihar Ondo, kuma ya shiga cikin aikin soja na Operation Crocodile Smile II a 2017.


‎-3. Laftanar Kolonel S. Bappah

‎Dan asalin jihar Bauchi, mai lambar aiki N/13036. An haife shi a 21 ga Yuni, 1984.
‎Memba ne na Signals Corps, kuma ya shiga NDA daga 27 ga Satumba 2004 zuwa 4 ga Oktoba 2008.
‎Yana cikin 56 Regular Course.

‎4. Laftanar Kolonel A.A. Hayatu

‎Dan asalin jihar Kaduna, mai lambar aiki N/13038. An haife shi a 13 ga Agusta, 1983.
‎Yana daga Infantry Corps kuma mamba ne na 56 Regular Course.


‎5. Laftanar Kolonel P. Dangnap

‎Dan asalin jihar Filato, mai lambar aiki N/13025. An haife shi a 1 ga Afrilu, 1986.
‎An taba gurfanar da shi a kotun soja tare da wasu jami’ai 29 a 2015 saboda laifuka da s**a shafi yakin Boko Haram.
‎Memba ne na Infantry Corps da 56 Regular Course.

‎6. Laftanar Kolonel M. Almakura

‎Dan asalin jihar Nasarawa, mai lambar aiki N/12983. An haife shi a 18 ga Maris, 1983.
‎Yana daga Infantry Corps kuma mamba ne na 56 Regular Course.

‎7. Major A.J. Ibrahim

‎Dan asalin jihar Gombe, mai lambar aiki N/13065. An haife shi a 12 ga Yuni, 1987.
‎Yana daga Infantry Corps, kuma mamba ne na 56 Regular Course.
‎Ya zama kaptin a 2013.

‎8. Major M.M. Jiddah

‎Dan asalin jihar Katsina, mai lambar aiki N/13003. An haife shi a 9 ga Yuli, 1985.
‎Yana daga Infantry Corps kuma mamba ne na 56 Regular Course.

‎9. Major M.A. Usman

‎Dan asalin Babban Birnin Tarayya (FCT), mai lambar aiki N/15404.
‎An haife shi a 1 ga Afrilu, 1989.
‎Yana daga Infantry Corps kuma mamba ne na 60 Regular Course.

‎10. Major D. Yusuf

‎Dan asalin jihar Gombe, mai lambar aiki N/14753.
‎An haife shi a 26 ga Mayu, 1988.
‎Yana daga Ordnance Corps, kuma mamba ne na 59 Regular Course.

‎11. Major I. Dauda

‎Dan asalin jihar Jigawa, mai lambar aiki N/13625.
‎An haife shi a 26 ga Nuwamba, 1983.
‎Ya shiga soji ta Short Service Course 38, daga 5 ga Yuni 2009 zuwa 27 ga Maris 2010.

‎12. Kaptin Ibrahim Bello

‎Mai lambar aiki N/16266, an haife shi a 28 ga Yuli, 1987.
‎Memba ne na Direct Short Service Course 4

‎13. Kyaftin A.A. Yusuf
‎Shi kyaftin ne a rundunar sojin ƙasa mai lambar aiki N/16724.

‎14. Laftanar S.S. Felix
‎Laftanar ne mai lambar aiki N/18105.

‎15. Laftanar Kwamanda D.B. Abdullahi
‎Jami’in rundunar sojin ruwa ne na Najeriya, mai lambar aiki NN/3289.

‎16. Shugaban Squadron S.B. Adamu
‎Jami’in rundunar sojin sama ne, mai lambar aiki NAF/3481.

Sulhu da ƴanbindiga ba tare da karɓe mak**an su ba haɗari ne - Gwamnan Zamfara Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ti...
30/10/2025

Sulhu da ƴanbindiga ba tare da karɓe mak**an su ba haɗari ne - Gwamnan Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ti gargadi kan tattaunawar da ake yi da yan bindiga kuma su ci gaba da rike makami.

Ya ce irin wannan sulhun haɗari ne kuma amfanin da kawai shine ya na rage rashin rikici amma kuma ya na raunana ikon gwamnati.

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin da yake gabatar da jawabi a wani taro na horo kan tsaron sirri karo na 18 a jiya Laraba a Cibiyar Nazarin Tsaro ta Ƙasa da ke Abuja.

A sanarwar da kakin sa, Sulaiman Idris ya fitar, gwamnan ya nuna takaici kan irin waɗannan zaman sulhun da ya ce ba a yin su akan ƙa'ida.

An fara bada horo kan dabarun noma na zamani a fannin ban-ruwa a jihar KatsinaDaga: Abdulrazak Ahmad JibiaAn kaddamar da...
30/10/2025

An fara bada horo kan dabarun noma na zamani a fannin ban-ruwa a jihar Katsina

Daga: Abdulrazak Ahmad Jibia

An kaddamar da horo na kwanaki biyu kan hanyoyin noma na zamani a fannin ban-ruwa ga jami’an yada bayanai na harkar noma da jami’an kula da ban-ruwa a Jihar Katsina, domin ƙara samun ƙwarewa da inganta samar da ingantaccen abinci a jihar.

Horon, wanda Hukumar Raya Hanyoyin Ban-Ruwa ta Jihar Katsina (KTSIDA) ta shirya tare da haɗin gwiwar Hukumar Raya Noma da Karkara ta Jihar Katsina (KTARDA) da Kamfanin MISBAH General Services, ya tattaro mahalarta daga dukkan ƙananan hukumomi 34 na jihar domin sabunta ilimi da ƙwarewarsu kan hanyoyin noma na zamani.

Jaridar Hausa Daily Post ta ruwaito cewa, bayan kammala horon, ana sa ran mahalarta za su yada ilimin da s**a samu ga sauran jami’ai a yankunansu.

Da yake ƙaddamar da horon, Kommishinan Noma na Jihar Katsina, Alhaji Aliyu Lawal Zakari, wanda Injiniya Shamsuddeen Sulaiman ya wakilta, ya shawarci mahalarta da su mai da hankali wajen koyon darussan da aka gabatar. Ya bayyana cewa gwamnatin Dikko Umar Radda na ɗaukar matakai na musamman wajen bunƙasa harkar noma, tare da kira ga duk masu ruwa da tsaki da su ƙara jajircewa don samun ci gaba mai ɗorewa a fannin.

A cikin jawabansu daban-daban, Manajan Darakta na Hukumar Raya Ban-Ruwa ta Katsina, Injiniya Salim Isah, da Manajan Darakta na KTARDA, Alhaji Abubakar Dabo, sun bayyana horon a matsayin “mai muhimmanci”, ganin irin rawar da noma ke takawa ta hanyar ban-ruwa wajen ƙara samar da abinci da samar da ayyukan yi ga matasa. Sun jaddada muhimmancin jami’an yada bayanai da na ban-ruwa wajen bunƙasa noma a matakin ƙasa.

Shi ma Manajan Darakta na MISBAH General Services ya bayyana cewa horon ya haɗa da koyarwa ta hanyar karatu da aikace-aikace domin tabbatar da cikakkiyar fahimtar batutuwan da aka koyar. Bayar da takardu daga masana kan dabarun noma ta zamani ta hanyar ban-ruwa na daga cikin manyan abubuwan da s**a ƙunshi wannan horo, wanda ake ganin zai taimaka wajen ƙara haɓaka samar da abinci da ci gaban tattalin arzikin Jihar Katsina.

Address

Plot 528, Benson Crescent
Abuja
900211

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Daily Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa Daily Post:

Share