Hameed Karrar

Hameed Karrar Shaheed Hameed Zakzaky Is Alive tiktok.com/

BI DA BI AKE BIN JAGORA BA'A WUCE SHI KUMA KAR YA MAKA NISA.®Hameed MirrorWatarana Imam Jawad (a.s) sun hadu da wani Dan...
21/09/2025

BI DA BI AKE BIN JAGORA BA'A WUCE SHI KUMA KAR YA MAKA NISA.

®Hameed Mirror

Watarana Imam Jawad (a.s) sun hadu da wani Dan Shi'ar su Mai Suna Ahmad Bin Zakariyya a Makka yayin Aikin Hajji, Sai mutumina yake cewa Imam "Ya Imam Gomnan mu masoyin ku ne, Yana tsananin muku biyayya, amma Imam Akwai harajin Gomnati a Kaina Mai nauyi" ya cigaba da cewa ya Imam da zaku temaka mana Koda da rubutun kune domin a saukaka min wannan harajin.
Sai Imam (a.s) yake cewa "Amma Ni Kuma ban sanshi ba" mutum yace "ya Imam Amma shi masoyin ku ne na hakika tabbas in kuka bashi sako zai aikata".

Sai Imam ya Rubuta Masa Takarfa k**ar haka "Assalamu alaika Ya Kai wannan Gomna tabbas Allah (T) ya daura maka hakkokin Al'umma a kanka, ka saukaka wa Al'ummar ka, ka musu rangome domin Allah zai tambaye ka daidai da Kwayar Hatsi da ya salwanta daga Baitil Mali. Wannan Mai sakon masoyin mu ne ka masa rangome daga harajin dake kanshi.

Bayan mutumin ya nufi komawa Garin su sai Labari ya riski sarki cewa ga chan wane ba tahowa da sako daga Imam Sadiq, a take Gomnan ya mike da kafa ya tunkaro fita daga gari domin ya Tarbi wannan Dan sakon, sai da yayi tafiya mai nisa sanan s**a hadu a hanya, Yana Isa ya rungume shi Yana Maraba dashi domin yau ga sako daga imamin Zamanin shi, kafin ya Bude takardan yace Masa, menene bukatar ka na biya maka yanzu, sai yace rangome nake nema daga Harajin da aka dauramin, take sarkin yace "Daga yanzu an cire maka Harajin, sannan za'a ware maka wani albarshi daga Baitil Mali daga yau".

Darasi.

Shi Imam Bai San wannan sarkin ba, Amma daga rubuta Letter shi domin biyayyar sa ga Imamin zamin sa baiga Sarautar dake kanshi ba ya tunkari barin gari domin ya Tarbi Mai wannan sakon, wannan fa rubutun takarda ne kawai, wani irin soyayya yakewa Imam da tinkafin ya Bude takardan ya biyawa Dan sako bukatarshi?, Tom irin wannan sallamawar da Mika wuya da Muwaddah akayiwa Jagora dake shiryar da ku zuwa ga Allah, shin mun Shirya irin wannan sallamawar ga wakilin Imam Mahdi Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) to irin wadannan sune Ashab na A'imma, wadanda ba damuwar su shine dole sai Imam ya San dasu ba aa me zasuyi domin su cikawa Imam burin shi, Mai zasuyi su faranta ran Imam. Amma sai kaga Jagora yayi jawabi wai mutum na Ikrarin Shi mabiyi ne Amma ko a jikinshi b***e ya bibiya, alhalin Jin sakonnin Jagora shine hanya na shirya shine hanyar sanin ina aka dosa Kuma ana inane, Muminai a gyara ana bin Jagora sau da kafa kar a bari Jagora yayi jawabi mutum hai saurara ba.

Ina Kara jaddada bai'ar Mutuwa ga Baban Hameed Sayyid Zakzaky, Allah ka tabbatar da duga-dugan mu akan Addinin ka.

Madogara Littafin As'habul A'imma.

19/09/2025

Idan har kai adalcin ka
se wanda ka zaba zaka yiwa
to ba makawa kai azzalumu ne.
(Islam Only)

FURSUNA MAFI KARANCIN SHEKARU A NIGERIYA.Shin kun taɓa jin cewa yarinya ƙarama ce ta zama fursuna mafi ƙanƙantar shekaru...
17/09/2025

FURSUNA MAFI KARANCIN SHEKARU A NIGERIYA.

Shin kun taɓa jin cewa yarinya ƙarama ce ta zama fursuna mafi ƙanƙantar shekaru a Najeriya, ko ma a duniya baki ɗaya ?

Wannan ba labarin tatsuniya ba ne, wannan gaskiya ce da ke faruwa yanzu haka a ƙasarmu, yarinya ƙarama, marar laifi, ta tsinci kanta cikin kurkukun Suleja tare da mahaifiyarta. Laifinta kawai shi ne kasancewa cikin muzaharar Quds wanda ya gudana a Abuja a shekarar nan ta 2025 wacce aka shirya domin nuna goyon baya ga al’ummar Falasɗinu da ke ake zalunta.

A maimakon a yaba mata da mahaifiyarta saboda tsayuwa da gaskiya, sai aka cafke su aka jefa su cikin gidan yari. Tambaya ita ce:

Shin wannan ita ce hanyar da za mu gina adalci a ƙasarmu ?
Shin yara ƙanana za su fara koya cewa tsayuwa da gaskiya laifi ne ?

Shin gwamnatinmu ta manta cewa yarinya ƙarama tana da hakkin samun kariya, soyayya da kulawa, ba wai ƙullewa a kurkuku ba ?

Wannan abu yana da taba ran duk wani mai Imani ko sanin dan Adamtaka yarinya karama a Kurkuku yana nufin an hana ta damar karatu da tarbiyyar da za ta gina makomarta. An hana ta jin dadi irin na yara sa'anninta misalin wasa, walwala da farin ciki.

An tilasta mata ta sha wahala da ciwon zuciya da bai k**ata ta sani a wannan shekarun na rayuwarta, a daidai wannan lokacin da sauran yara ke shiryawa domin zuwa makaranta da jin dadin iyaye, ita kuma tana shan iska mai daci a Kurkuku tare da mahaifiyarta.

Wannan ba batun siyasa ba ne, batune na adalce wanda masu son gaskiya ya k**ata su yi duba akai. Wannan ba maganar siyasa bace, wannan magana ce ta yan Adam magana ce ta adalci, magana ce ta kare marasa laifi. Duk wanda ke da zuciya ya k**ata wannan lamari ya taba shi.

Idan muka yi shiru akan wannan yarinya ƙarama, gobe ko wasu yara nawa za a maimaita musu irin wannan ?

Muna kira ta babbar murya akan Gwamnati ta gaggauta sakin wannan yarinya karama wacce aka k**a tare da mahaifiyarta wadanda basu aikata laifin komai ba. Kuma muna kara fadi da babbar murya akan ba za mu amince da azabtar da yara kanana ba saboda tsayuwa akan gaskiya ba laifi ba ce.

Wannan rubutu yana bukatar a yada shi, a yi magana akai, a kawo sauyi. Yarinya karama tana kurkuku ba wai kawai abin takaici ba ne wannan abin kunya ne ga kowanne dan Adam da ke da Imani da adalci.

-Sani Hamisu.
-25 Rabi'Al-Awwal 1447
17 September 2025.

RANAR HAIHUWAR SA DAYA DA IMAM ALI, HAKA RANAR SHAHADA DAYA, SALON SHADA DAYA. KAMAR YADDA AKA SARI IMAM ALI (A,S)  HAKA...
15/09/2025

RANAR HAIHUWAR SA DAYA DA IMAM ALI, HAKA RANAR SHAHADA DAYA, SALON SHADA DAYA. KAMAR YADDA AKA SARI IMAM ALI (A,S) HAKA AKA CAKA MASA WUKA A GOSHI"

®️Hameed Mirror.

" Hameed Baya Barci Da Dare Karatu Kawai Yake Don Da Dare Yayi Koda Suna Tare Da Yara Zaka Ga Ya Sallame Su Yace Kowa Ya Kwanta Sai Ya Kashe Lantarkin Dakin, Can Da Dare Idan Ka Duba Zaka Ga Karatu Kawai Yake, Don Babu Wani Fanni A Littafi Ko A Intanet Wanda Ya Shafi Fannin Kera Jirgin Sama(Aeronautic Engineering) Da Hameed Bai Karanta Ba"

"Malam Yakara Da Cewa; Daga Cikin Baiwowin Da Allah Ya Masa Babu Wani Abu Da Hameed Bai Iya Kera Shi Ba, Matukar Kayi Masa Bayani Komai Kankantar Bayanin, Indai Hameed Ya K**a Gashin Kansa To An Gama(Zai Kera Shi) Kawai"

Wata Karin Baiwa Da Akayi Wa Sayyid Hameed Shi Ne, Haihuwar Shi A Ranar 13 Ga Rajab Ranar Da Aka Haifi Sarkin Muminai Imam Ali(As) Haka Ma Ranar Shahada Iri Daya Har Da Salon Shahada Iri Daya, An Caka Wa Wuka A Goshin Hameed K**ar Yanda Aka Sari Imam Ali(As) Da Wuka A Goshi

Allah Ka Kara Aminci Ga General Hamid Ibrahim Zakzaky(H) Da Sauran Shuhada Ka Bamu Ikon Riskarsu A Matsayin Shuhada Alfarmar Sayyida Zahra(As)

ADDININ ALLAH ZAI TABBATA 03®Hameed Mirror -Daga bakin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)"Kuma ba abinda zai zama Adalci illa a...
13/09/2025

ADDININ ALLAH ZAI TABBATA 03

®Hameed Mirror

-Daga bakin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

"Kuma ba abinda zai zama Adalci illa a koma nizamin gabashi Duniya Wanda ake cewa gurguzu kokuma Cominisanci, lokacin duk wanda ka samu Qungiyan masu neman ko 'yanci ne ko kasashen Africa ko kasashen da ake cema masu tasowa, ko Qungiyan kawo sauyi ne, harma Anan nahiyar tamu wadan da suke Kiran kansu wayayyu cigababbu a jami'o'i Basu da wata da'awa illa cewa ana amfani da nizamine Mai zalunci nizamin yammacin Duniya, saboda haka Babu wani nizami za'a koma a Sami Adalci illa nizamin gurguzu, to shikkenan sai Allah (T) ya rugurguza gurguzu, da gurguzu ya rugurguje sai ya zamana wanda yake ganin gurguzu zai fansheshi yanzu me zai ce maka Kuma."

"Da nizamin gurguzu Allah (T) ya rugurguza shi sai ya zamana wato kenan Muna ganin tamkar somin tabi ne ga ainihin nizamin na yammacin Duniya, Wanda shima da sannu insha allahul Azimi shima zai ruguje to Kuma sai Mukaga har wala yau nizaminnan na yammacin Duniya, shima ya shiga kiloli, wato wannan yanuna kenan a sarari in mutum ya duba da kyau zaiga cewa abinda ya mamayi Duniyan musulmi yashiga tsakanin su da Addinin su ya fara gushewa, Kuma zamuga a wannna ma in ya maka Nisa to zan iya cewa ai anan Abubuwan dake iko sun fara subutowa, Wanda akasan cewa sarakai suna da iKon rayuwa da Mutuwa kan mutane, yayin da aka rabasu da iKon rayuwa da Mutuwa sai ya zama an Basu ikon shuka, Kuma suna iya kwatan Wanda s**aso su murje, shikkenan yau da kullum anaji ana gani sai Allah (T) ya kawo karshen iKon sarakuna, ya zamana aka wayi gari su sarakuna basa iya cewa Koda azo a share musu kofar gida ba."

"Wato Kuma Babu wani Mai jin tsoron wani ba sarake to ana nan Kuma iko Wanda ake ganin misali masu Bindiga suna da shima ya fara kawo Karshe wato ikon Yan Bindiga (Soja kenan) to kenan yanzu bazasu iya nuna bindigan nan su firgita wani ba, Kuma ma Babu wani Wanda yake Jin abinda suke a Kai daidai ne, k**ar yanda jiya nake tambaya a mafara nake cewa "wanene yakejin cewa mutanan nan da ake cewa shuwagabanni wayake Jin cewa abinda sukeyi dai-dai ne? Sai kowa yake cewa Babu, su kansu sun San mutane basu ganin abinda sukeyi dai-dai ne suma kansu sun Sha tsayawa a matsayoyi da Dama su yankewa kawukan su hukunci akan cewa su Kam abinda sukeyi ba dai-dai bane."

"Alal misali k**ar abinda ya faru kwanakin baya a Abuja a taron majalisan da ake cewa wai masu rubuta Sabon tsarin mulkin, sai aka Dan Yan wani Committee na wani abune wai su biyar sai wani ya kawo s**a ga kawo sunayen wadannan mutane biyar din, yace AI wadanan mutanan da aka bayar da sunayen su barayi ne, shikkenan sai ya mike yace AI sunan duk cikansu barayi ne daya daga cikinan yace shi ba barawo bane, Wanda yake nuna dukkan su menene kenan? Yawwa barayi kawai Wato su a kansu sun yanke da cewa su barayi ne."

Jawabin Sayyid Ibraheem Zakzaky a shekarun baya garin Gusau.

11/09/2025

In kana Nan Ba Liman📌

Jagoran Juyin Juya Halin addinin Musulunci a fadin Afrika Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) tare da shugaban Jamhuriyar Musulu...
08/09/2025

Jagoran Juyin Juya Halin addinin Musulunci a fadin Afrika Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) tare da shugaban Jamhuriyar Musulunci ta Iran yau Litinin.

Supreme Leader Allahma Sayyid Ibraheem Zakzaky (H).
08/09/2025

Supreme Leader Allahma Sayyid Ibraheem Zakzaky (H).

WANENE MATASHI?koda akache matashi ba ana nufin kowanne mai shekaru 15-40 yazam lazim yazam matshiba idan munyi tinani a...
07/09/2025

WANENE MATASHI?

koda akache matashi ba ana nufin kowanne mai shekaru 15-40 yazam lazim yazam matshiba idan munyi tinani a ma'anar kalmar ta sirri.

Matasantaka yafi k**a da resisting wanda idan muka dau ma'anar resisting kaga tana da fadi da hanyoyi.

Meyasa Nigeria ke durkushews dukda dunbin matasan da take da?.

Matasan nigeria kala ukune3.

1. Matasa masu kishi cikinsu akwai yan gwahwarmaya da masu wankakken tinani.

2. Yan ta more mafiya yawa koda suna da ilimi zakaga crawd suke ana sasu ayyuka k**ar bangar siyasa ko kashe wani ko dakatarda wani abu mai muhimmanchi misali (Zaria) ana yawan turamusu crawd suyi sare-sare.

3.Komarori(comds) iyayen iyayine da nuna an iya amma basusan The way out ba sunfi kawo ciwon kai saboda suna da ilimi amma bana amfaniba iliminsu yafi amfani ne wajen tallata yan siyasa da zama celebrity.

Dukkan wadannan matasane sai de kaso na daya ke amsa kalmar. Kaso na biyu ababi na hankali su mahaukatane. kaso na uku sam basu da hadafin rayuwa za'a iya kiransu yan duniya masu son sharholiya wanda tunaninsu idan wuta tabar kaina tafada kan uban kowama.

Idan kaso 70 na daga matasa 2 da 3 ne to babu yadda zaka samu cigaba.

Misali: matashi zai gama makarantar likitanchi amma wallahi bai iya jan ruwan alluraba amma ya iya rike tsitaka.

Kaga engineer amma baimason tayadda zaifara kirkirba.

WAYE MATASHI?

Mai fadi tashi da ya tsayu da kawo gyara wa kansa da al'ummarsa domin gobensu, Fahimtarkai da baiwarka sune zasu tallafi wannan yunkuri na matshi zuwa cimma hadafinsa, ka iya gano mai ka iya ko ka kware ko yake burgeka wanda baka gajiya da yinsa.

Matsahi bazai iya kawo gyaraba sai ya saita rayuwarshi da zamanishi.

ALBISHIRIN KU! ADDININ ALLAH ZAI TABBATA 02 ®Hameed Mirror Wato abinda nake kokarin cemana shine inda bazaiyiwu a aikata...
04/09/2025

ALBISHIRIN KU! ADDININ ALLAH ZAI TABBATA 02

®Hameed Mirror

Wato abinda nake kokarin cemana shine inda bazaiyiwu a aikata Addini ba wato za'a samu wani zamani da bazaiyiwi Sam ayi Addini ba to da Zamu Bukatu ya zuwa wani Addini Mai aikatuwa, Wanda wani Manzo zaizo dashi Manzon zamani, munsan ba wani Manzo da zaizo Kuma munsan cewa addininnan Mai aikatuwa ne, in Kuma ba haka ba Allah ba zai Nememu da ainihin mu aikata shi ba, Kuma in muka aikata, sannan ya azurtamu akai zai zama k**ar ya zalunci mu ne, to munsan Kuma Allah baya zalunci munsan Kuma Allah (T) baya kallafawa Rai sai abinda take iyawa. Wato Ina kokarin in nuna mana cewa tinda abin hakane, wanan ya nuna wannan Addinin Mai yiwuwa ne a Kowanne zamani har I zuwa ranar da za'ayi hurin kaho.

Sanna kuma wani Abu na Biyu Mukaga cewa an kwashe shekaru kusan shekaru Dari wannan Karinin da ya kawo Karshe Nasara da Yahudu sukuma s**a mamayi Duniya s**a tabbatar da mulkin su Harda wannan nahiya tamu to Muna nan Muna nan, sai Mukaga shi nizamin da yafi Kowanne gallazawa musulmai shine nizamin Cominisamci (Comenies) sai Allah T ya kawo ajalin sa kuma musulmin da ake ma danniya a karkashin nizamin Cominisamci sai s**a samu Huriyya.

Wanda zaka samu Dattijo Dan shekara sabai'in Yana koyon fatiha dom a duk shekarunna ba'a yarda ya iya ba, Bai iya fatiha ba!. KO ya koyi alwala don duk baisan wannan ba saboda anihin nizamin Cominisamci ya dankara mishi wani Abu wanda ya haramta Masa sanin Addini Mai yiwuwa kila wasun kuma sun Dan Karanta ko sunji lokacin da nake Bada goro, kokuma nace tsaraba na Rasha bayan da naje bara, aciki har nake cewa Akwai wani yanda da suke daukar ma matakai na gano wanene yake koyawa dansa Addini ta hanyar rubuta harufan arabiyya a allo su tambayi Yara wane yasan wannan? In yaro ya mike yace alif, baa,Taaa, sai a Nemo baban sa ya bace kenan wanna ya Nuna Yana koyawa yaransa Addini a boye, to Amma wannan sai yayi Kai Kuma nan kafin fadiwar tarayyar Sobiet ana Nuna mana cewa nizamin da ake amfani dashi Wanda yake an aroshi ne daga turawan yammacin Duniya nizamin Mai zalunci.

Jawabin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) Jaula Gusau

02/09/2025

Ya Sahibuzzaman 🥺😭

IDAN AKWAI ABINDA ZAMUYI ALFAHARI DASHI TO SHINE MUSULUNCI.®Hameed Mirror Da chan inda kuke ganin shi Sahara dinnan inda...
02/09/2025

IDAN AKWAI ABINDA ZAMUYI ALFAHARI DASHI TO SHINE MUSULUNCI.

®Hameed Mirror

Da chan inda kuke ganin shi Sahara dinnan inda ya hada da Hamada din Niger Libia ai da wurine Mai ruwa, ba gashi ana tottono abubuwa ba ana tono su Khado su Dynaso, da chan wurin ruwa ne ana Kuma Noma ana zaune Lafiya da ya bushe mutane s**a yo nan s**ayi yamma, asalin Mutanen sun barbazu kenan, saboda haka masu Da'awar Kabilanci ba za kuje ko ina da Kabilanci ba, shi Dan Adam Mutum halittan Allah ne, Allah ne ya hallicce shi shi ya dorashi a doron kasa.

inda abinda ya k**ata yayi tinkaho yayi Alfahari dashi shine yace ni Musulmi ne!, sabida ina bin abinda Allah yake so ayi, yayini ne don in Bauta Masa, ya dorani a doron kasa ne don in Bauta Masa Kuma ya aiko da Manzon ya saukar da Littafi (Qur'ani) Alhamdulillah nagodewa Allah nabi wannan Manzon nayi Imani da wanan Al-Qur'ani Kuma a kanshi nake, yawwa sannu Dan kasa Kaine cikakken Dan kasa, Kaine cikakken Dan Asali Wanda ka dace da abinda aka yi ka domin shi ba tinkahon jini ba da Kabila ba.

Fadin Manzon Allah (s.a.w) ``Laisa Minna man katala Ta'asuban".``Laisa Minna Manidda'a Ta'asuban" Wanda yayi Da'awar Ta'asubanci (Kabilanci) baya daga cikin mu Inji Manzon Allah (s.a.w). Wanda Kuma yayi fada don Ta'asubanci bashi daga cikin mu, Wanda ya mutu cikin Ta'asubanci bashi a cikin mu, duk fadin Manzon Allah (s.a.w) kaga Mai Da'awar Kabilanci in yaje Lahira in akace ina Yan Al'ummar Annabi Bai Isa yaje nan ba sai yaje na Kabilan su.

Saboda haka in kaga mutum yana fada dasu Shehu Yana fada da Musulunci ne malamin, da yazo ya koyar da Addini yayi Da'awar Addini ya Kafa Addini kace zakayi fada dashi da sunan Kabila munsan abinda kake fada Musulmi kakeso kayi fada dashi, ko ka ce mishi Bafulatani mun Gane Bafulatanin Musulmi kake nufi, su Turawa haka suke Basu taba cewa musulmi Musulmi ba ai, yanzu a Surbawa dinna su Turkawa suke ce musu, haka suke duk inda kagan su sai su dauko Kabila su jinginawa Addini, to shikenan suma Turkawa abinda s**ayi kenan s**a b***e s**ayi nasu Addinin s**ace waccan Addinin na Rumawa ne Sukace Church of England nasu na kabilarsu s**a b***e daga Church din Rum suna Rumawa sun musu mulkin malla kaga Kabilanci kenan ko, kaga shima Kabilan akayi Addinin shi nanma Akwai masu bin Addinin England shine Englican Church shine Chochin Ingila, har wasu ma sun fara African Church Basu yarda da na Church din England ba kowa yayi nashi Oho dai mu bamu da wani Chochi ma, yanzu anan ana Masallacin su wane ko, mu abinda muka sani massalaci wajen Bautar Allah ne.

Jawabin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na Mu'utamar din Mauludi.

Address

Abuja

Telephone

+2349044427020

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hameed Karrar posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hameed Karrar:

Share