Malumfashi Reporters

Malumfashi Reporters Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Malumfashi Reporters, Digital creator, Abuja.

Haramun Ne Yin Taron Rasuwa, Haramun Ne Yin Taron Tsoffin Dalibai, Haramun Ne Yin Taron Daurin Aure, Haramun Ne Yin Taro...
16/12/2025

Haramun Ne Yin Taron Rasuwa, Haramun Ne Yin Taron Tsoffin Dalibai, Haramun Ne Yin Taron Daurin Aure, Haramun Ne Yin Taron Mutuwa, Haramun Ne Taron Radin Suna, Haramun Yin Hoto, Haka Kuma Haramun Ne Matarka Ta Tsugunna Ta Gaishe Ka, Cewar Ustaz Hussaini

Malumfashi Media Concept Malumfashi Reporters

Da ɗumi-ɗumi: Majalisar Dattawa Ta Umarci NSA Ya Binciki Labaran Ƙarya Kan Lafiyar Sanata Akpabio.Majalisar Dattawan Naj...
16/12/2025

Da ɗumi-ɗumi: Majalisar Dattawa Ta Umarci NSA Ya Binciki Labaran Ƙarya Kan Lafiyar Sanata Akpabio.

Majalisar Dattawan Najeriya ta yanke shawarar bai wa Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro (NSA) umarnin binciken yaɗa labaran ƙarya da ke cewa Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya samu matsalar lafiya har aka garzaya da shi asibiti a Landan.

An ɗauki wannan matsaya ne a zaman Majalisar na ranar Talata, bayan Sanata Titus Zam ya miƙa point of order, inda ya yi Allah-wadai da yaɗuwar rahotannin bogi a kafafen yaɗa labarai daban-daban.

Sanata Zam ya bayyana labaran a matsayin abin da ba za a yarda da shi ba, tare da kiran hukumomi da su gano tare da gurfanar da masu hannu a yaɗa ƙaryar domin zama darasi ga sauran masu irin wannan ɗabi’a.

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Akpabio, wanda ya jagoranci zaman, ya nuna damuwa kan yadda ake ƙara fuskantar ƙalubale wajen daidaita abubuwan da ake wallafawa a kafafen yaɗa labarai—musamman waɗanda ke shafar ’yan siyasa. Ya bayyana wasu daga cikin abubuwan da ake fitarwa a wasu dandamali da kalaman “shara a shigo da ita, shara kuma ake fitarwa,” yana mai jaddada wahalar da ke tattare da dakile ƙarya.

Wannan na zuwa ne bayan jita-jitar intanet da ta yi ikirarin cewa Akpabio ya faɗi ya kuma shiga asibiti, ikirarin da mataimakansa s**a musanta ƙwarai da gaske, suna kiran sa labaran ƙarya tsagwaron su. Malumfashi Media Concept Malumfashi Reporters

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT),  Barista Nyesom Wike, ya halarci bikin kaddamar da fara shekarar shari’a ta 2025/2...
16/12/2025

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Barista Nyesom Wike, ya halarci bikin kaddamar da fara shekarar shari’a ta 2025/2026 ta Babbar Kotun Tarayya (Federal High Court) da kuma Taron Shekara-shekara karo na 41 na Manyan Alkalai a jiya, a Abuja.

Wannan bikin a tsarin Kotun yana nuna ta shiga sabon sherar shari’a.
Malumfashi Media Concept Malumfashi Reporters

Innalillahi wainna ilaihi raji'un Allah Ya yi wa tsohon Babban Alkalin Ƙasa, Justice Ibrahim Tanko rasuwa, bayan fama da...
16/12/2025

Innalillahi wainna ilaihi raji'un

Allah Ya yi wa tsohon Babban Alkalin Ƙasa, Justice Ibrahim Tanko rasuwa, bayan fama da jiya da yayi.

Justice Ibrahim Tanko ya rasu ne bayan ya yi shekaru yana hidimar ƙasa a fagen shari’a, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da adalci, bin doka da oda, da kuma kare dimokuraɗiyya a Najeriya. A tsawon aikinsa, an san shi da rikon amana, jajircewa da tsayawa kan gaskiya ba tare da tsoro ko son rai ba.

Allah Ya gafarta masa kurakuransa, Ya sanya Aljannar Firdausi ta zama makomarsa, Ya kuma bai wa iyalansa, abokan aikinsa da al’ummar Najeriya haƙurin jure wannan babban rashi.

Malumfashi Media Concept Malumfashi Reporters

DA ƊUMI-ƊUMI: Musulma ta Farko ta lashe zaɓen Mataimakiyar Gwamna a AmurkaSanata Ghazala Hashmi ta jihar Virginia ta kaf...
10/11/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Musulma ta Farko ta lashe zaɓen Mataimakiyar Gwamna a Amurka

Sanata Ghazala Hashmi ta jihar Virginia ta kafa tarihin zama Musulma ‘yar asalin Amurka ta farko da aka zaɓa zuwa mukamin gwamnati a matakin jiha a Amurka, inda ta lashe zaɓen Mataimakiyar Gwamnan jiha.

An haife ta a shekarar 1964 a Hyderabad, India, kuma ta tashi a jihar Georgia. Hashmi tana da digirin digirgir (PhD) a fannin Adabin Turanci, kuma tana aiki a Majalisar Dokokin Jihar Georgia tun daga 2020. Ta kayar da ɗan jam’iyyar Republican, John Reid, da kashi 55.3% na kuri’un da aka kada, kuma za ta gaji Winsome Earle-Sears.

Ko da yake aikin mataimakin gwamna ba shi da nauyi sosai na doka, za ta kasance mai karya turjiya a majalisar dattijan jihar, sannan ita ce za ta fara maye gurbin gwamna idan bukatar hakan ta taso.

Daga Usman Umar Katsina

YANZU-YANZU: Sakataren Harkokin Wajen Vatican, Kardinal Pietro Parolin, ya Ƙaryata zargin kisan kiristoci a Najeriya.Kar...
26/10/2025

YANZU-YANZU: Sakataren Harkokin Wajen Vatican, Kardinal Pietro Parolin, ya Ƙaryata zargin kisan kiristoci a Najeriya.

Kardinal Parolin ya gargaɗi cewa bai dace a fassara rikicin tsaro a Najeriya a matsayin kisan Kiristoci kaɗai ba.

A cewarsa, “Ba rikicin addini ba ne. Yawancin tashin hankali dake Faruwa a Najeriya ya samo asali ne daga matsalolin zamantakewa k**ar rikicin filaye tsakanin makiyaya da manoma a yankin Arewa ta Tsakiya.

Ya ƙara da cewa: “Ya k**ata mu gane cewa da dama daga cikin Musulman Najeriya suna cikin waɗanda abin ya shafa ta irin wannan bangaren.

A cewrasa kungiyoyi masu tsatsauran ra’ayi ba sa bambance addini wajen yin zalunci, suna amfani da tashin hankali kan duk wanda s**a ɗauka a matsayin abokin gaba.”

A baya, Bishop Matthew Hassan Kukah, Bishop na Cocin Katolika ta Sokoto Diocese, ya roƙi ƙasashen duniya kada su sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ke fama da matsanancin wariyar addini (“Country of Particular Concern”), yana mai cewa hakan zai iya lalata ƙoƙarin da ake yi wajen samar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin addinai.

Da yake jawabi a bikin ƙaddamar da rahoton “Aid to the Church in Need (ACN) 2025 World Report on Religious Freedom” da aka gudanar a Vatican City A ranar Talata, Bishop Kukah ya amince cewa Najeriya tana fuskantar ƙalubale masu tsanani, amma ya jaddada cewa ƙasashen duniya su taimaka wa Najeriya, kar su bayyana Najeriya ta fuskar nan, yayin da take ƙoƙarin magance rikice-rikice da tashin hankali.

DA ƊUMI-ƊUMI: Jami'an EFCC sun k**a mutane biyu kan rashin bayyana kudi Dala 6,180 da £53,415 a Filin Jirgi na Legas kud...
12/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Jami'an EFCC sun k**a mutane biyu kan rashin bayyana kudi Dala 6,180 da £53,415 a Filin Jirgi na Legas kudancin Najeriya

Jami’an Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa (EFCC) na Ofishin Yankin Legas Directorate 2 sun k**a wasu matafiya biyu, Mamud Nasidi da Yahaya Nasidi, a Filin Jirgin Sama na Murtala Muhammed saboda tafiya da kudade ba tare da sun bayyana su ba — jimillar £53,415 da dalar Amurka $6,180 bayan isowarsu daga Dubai.

A cewar wata sanarwa da hukumar ta fitar, jami’an Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Kasa (FAAN) ne s**a k**a su, bisa zargin rashin bayyana kudaden da suke dauke da su.

Sanarwar ta kara da cewa, wadanda ake zargin suna cikin hanyarsu ta tafiya zuwa Addis Ababa daga Dubai, amma an k**a su ne yayin da s**a tsaya a tashar jirgin sama ta Legas.

Da Dumi Dumi: Naira ta ƙara Daraja zuwa N1,458/$1, wanda shi ne mafi kyawun matsayin da ta samu tun shekarar 2024, a cew...
12/10/2025

Da Dumi Dumi: Naira ta ƙara Daraja zuwa N1,458/$1, wanda shi ne mafi kyawun matsayin da ta samu tun shekarar 2024, a cewar rahoton tattalin arziƙi na yau.

GANI YA KORI JI: Tsohon shugaban kasar Afrika ta Kudu - South African, Thabo Mbeki ya zama mai daukar hoto a wajen wani ...
12/10/2025

GANI YA KORI JI: Tsohon shugaban kasar Afrika ta Kudu - South African, Thabo Mbeki ya zama mai daukar hoto a wajen wani taro.

Wane fata Saliyo masa?

Masu Haya Da Mashin A Karamar Hukumar Malumfashi Sunfara Biyan Haraji Na Naira 100 Wanda Akesanyaran za aci gaba da Ansa...
12/10/2025

Masu Haya Da Mashin A Karamar Hukumar Malumfashi Sunfara Biyan Haraji Na Naira 100 Wanda Akesanyaran za aci gaba da Ansa A Kowace Rana.

Miye Ra'ayoyinku Gameda Hakan?

Tun bayan da yan bindiga s**a fasa gidansa s**a sace shi a mahaifarsa dake Tsiga, yau General Maharazu Tsiga, ya ziyarci...
11/10/2025

Tun bayan da yan bindiga s**a fasa gidansa s**a sace shi a mahaifarsa dake Tsiga, yau General Maharazu Tsiga, ya ziyarci cikin garin nasu da ya dau watanni bai je ba, sak**akon lokacin da aka ceto shi, Abuja aka wuce da shi kai tsaye.

Jama'ar garin sun yi tururuwa a yau wajen tarbarsa, tare da cika masa gida don nuna alhininsu gare shi

Kafin dauke shi tsohon shugaban hukumar NYSC Janar Tsiga, na matuƙar ƙaunar mahaifar tasa, inda yake yawan zama garin tare da gudanar da taimakon mara ƙarfi, da kuma sauraren koken al'ummarsa.

Ya kuma yi amfani da damarsa lokacin da yana soja a matsayinsa na shugaban hukumar NYSC ya taimaki yan garin da dama sun sami aiki a hukumar NYSC da ya watsa su aiki ko'ina a fadin kasar nan

DA DUMI-DUMI: Tinubu ya yafewa Maryam Sanda, wadda aka yankewa hukuncin kisa a shekarar 2020, bayan samunta da laifin ka...
11/10/2025

DA DUMI-DUMI: Tinubu ya yafewa Maryam Sanda, wadda aka yankewa hukuncin kisa a shekarar 2020, bayan samunta da laifin kashe mijinta Bilyaminu Bello.

Address

Abuja
:1675527729733&Q=900001

Telephone

+2348066959583

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malumfashi Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Malumfashi Reporters:

Share