16/12/2025
Da ɗumi-ɗumi: Majalisar Dattawa Ta Umarci NSA Ya Binciki Labaran Ƙarya Kan Lafiyar Sanata Akpabio.
Majalisar Dattawan Najeriya ta yanke shawarar bai wa Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro (NSA) umarnin binciken yaɗa labaran ƙarya da ke cewa Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya samu matsalar lafiya har aka garzaya da shi asibiti a Landan.
An ɗauki wannan matsaya ne a zaman Majalisar na ranar Talata, bayan Sanata Titus Zam ya miƙa point of order, inda ya yi Allah-wadai da yaɗuwar rahotannin bogi a kafafen yaɗa labarai daban-daban.
Sanata Zam ya bayyana labaran a matsayin abin da ba za a yarda da shi ba, tare da kiran hukumomi da su gano tare da gurfanar da masu hannu a yaɗa ƙaryar domin zama darasi ga sauran masu irin wannan ɗabi’a.
Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Akpabio, wanda ya jagoranci zaman, ya nuna damuwa kan yadda ake ƙara fuskantar ƙalubale wajen daidaita abubuwan da ake wallafawa a kafafen yaɗa labarai—musamman waɗanda ke shafar ’yan siyasa. Ya bayyana wasu daga cikin abubuwan da ake fitarwa a wasu dandamali da kalaman “shara a shigo da ita, shara kuma ake fitarwa,” yana mai jaddada wahalar da ke tattare da dakile ƙarya.
Wannan na zuwa ne bayan jita-jitar intanet da ta yi ikirarin cewa Akpabio ya faɗi ya kuma shiga asibiti, ikirarin da mataimakansa s**a musanta ƙwarai da gaske, suna kiran sa labaran ƙarya tsagwaron su. Malumfashi Media Concept Malumfashi Reporters