Munam Africa News

Munam Africa News Munam Africa News: Follow our page for 100% factual news.

Fitaccen Malami Kuma Limamin da Ya Ceto Kiristoci 300 a Jihar Filato Ya RasuFitaccen limamin Musulunci, Malam Abdullahi ...
16/01/2026

Fitaccen Malami Kuma Limamin da Ya Ceto Kiristoci 300 a Jihar Filato Ya Rasu

Fitaccen limamin Musulunci, Malam Abdullahi Abubakar, wanda ya shahara sanadiyyar ceto Kiristoci sama da 300 a yayin rikicin jihar Filato a shekarar 2018, ya rasu yana da shekaru 92. Marigayi Abdullahi Abubakar shi ne babban limamin garin Nghar da ke karamar hukumar Barikin Ladi, inda ya shafe shekaru yana hidimtawa al’umma da kuma karantar da zaman lafiya da hadin kai.

Limamin ya yi fice ne lokacin da rikici ya barke a wasu sassan Jihar Filato, inda wasu ‘yan bindiga s**a kai hare-hare. A lokacin tashin hankalin, ya bude kofar masallacinsa da gidansa, ya ba da mafaka ga daruruwan Kiristoci da ke guduwa domin tsira da rayukansu, ba tare da la’akari da bambancin addini ba.

Jarumtaka da tausayi irin na Malam Abdullahi Abubakar sun jawo masa yabo daga cikin gida da wajen Najeriya, inda aka rika daukarsa a matsayin abin koyi na zaman lafiya tsakanin addinai. Bayan rasuwarsa, jama’a da dama sun bayyana bakin cikinsu, tareda ambata shi a matsayin gwarzon bil’adama da ya fifita kare rayukan mutane fiye da komai.

Jerin Kasanshe 75 da Amurka ta Dena Basu Bisa
16/01/2026

Jerin Kasanshe 75 da Amurka ta Dena Basu Bisa

Gwamnatin Tarayya Zata Kashe Naira Biliyan 113.7 Don Tallafin Karatu da Ciyar da DalibaiCikakken Rahoton na Comment Sect...
16/01/2026

Gwamnatin Tarayya Zata Kashe Naira Biliyan 113.7 Don Tallafin Karatu da Ciyar da Dalibai

Cikakken Rahoton na Comment Section 👇

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na II ze Koma Jami'ar Northwest Domin Karantar Shari'aJami’ar Northwest da ke Jihar Kano ta...
16/01/2026

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na II ze Koma Jami'ar Northwest Domin Karantar Shari'a

Jami’ar Northwest da ke Jihar Kano ta sanar da amincewa da karɓar Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi na II, a matsayin ɗalibi na musamman a bangaren karatun shari’a. Jami’ar ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa a hukumance da shugaban sashen jarabawa da bayar da gurbin karatu, Jafaru Sule Muhammad, ya rattaba wa hannu a madadin Rajistara, Isyaku Adamu.

A cewar sanarwar wadda ke ɗauke da kwanan wata 12 ga Janairu, 2026, an ba Sarkin wannan gurbi ne bayan jami’ar ta tabbatar da cewa ya cika dukkan sharuddan da ake buƙata domin bayar da gurbin karatu na musamman. Sanarwar ta kuma bayyana cewa Sarkin Kano zai yi karatu ne a fannin Shari’ar Musulunci da ta zamani a matakin aji biyu.

'Yan kasar Uganda na ci gaba da jiran sakamakon zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki bayan da aka samu jinkiri mai...
16/01/2026

'Yan kasar Uganda na ci gaba da jiran sakamakon zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki bayan da aka samu jinkiri mai tsawo a rumfunan zabe sakamakon matsalolin fasaha, yayin da Shugaba Yoweri Museveni ke neman sake komawa kan karagar mulki bayan shafe Kudan shekaru 40 Yana mulkar Kasar.

A wurare da dama na fadin kasar, an samu jinkirin fara kada kuri’a na tsawon awanni bayan an makara wajen kawo akwatunan zabe, sannan kuma na’urorin tantance masu zabe ta hanyar bayanan halitta sun kasa aiki yadda ya kamata. Wasu masu jefa kuri’a sun danganta matsalolin da katsewar intanet da gwamnati ta yi a ranar zaben.

Gwamnatin Uganda ta ce katsewar intanet din ya zama dole ne domin hana yaduwar labaran karya da ka iya tayar da hankulan jama'a yayin zabe. Duk da matsalolin da aka fuskanta, Hukumar Agajin Gaggawa ta Red Cross a Uganda ta ce zaben ya gudana cikin lumana, tare da kasancewar jami’an tsaro na ‘yan sanda da sojoji a ko’ina domin tabbatar da tsaro.

Shugaba Museveni da kansa ya amince cewa ya fuskanci matsala wajen amfani da na’urar tantance masu zabe. Ya ce na’urar ta kasa karbar yatsunsa har sai da aka yi amfani da hoton fuskarsa kafin ya samu damar kada kuri’a, yana mai alkawarin bincike kan matsalolin da aka samu.

Museveni, wanda ke takara da fitaccen mawaki da ya koma siyasa, Bobi Wine mai shekaru 43, na fuskantar wannan gasa ne shekaru biyar bayan fafatawarsu ta farko a zaben shugaban kasa na 2021. Idan aka sanar da sakamakon, za a san ko Shugaban kasar zai sake samun wa’adi ko kuwa za a samu sabon shugabanci a Uganda.

Ficewar ɗana daga jam’iyyar PDP zuwa APC zaɓi ne na kansa, wanda ya shafi maslahar siyasarsa kai tsayeTsohon Mataimakin ...
16/01/2026

Ficewar ɗana daga jam’iyyar PDP zuwa APC zaɓi ne na kansa, wanda ya shafi maslahar siyasarsa kai tsaye

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa matakin da dansa, Abba Abubakar, ya dauka na ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa APC zabi ne na kansa, ba tare da wani matsin lamba daga gare shi ba. Ya ce a tsarin dimokuradiyya, irin wannan mataki ba sabon abu ba ne, ko da siyasa ta hadu da alakar iyali.

Atiku ya jaddada cewa a matsayinsa na mai kishin dimokuradiyya, ba ya tilasta wa ‘ya’yansa ko ‘yan Najeriya ra’ayi a harkokin siyasa. Sai dai ya nuna damuwa kan abin da ya kira gazawar shugabancin jam’iyyar APC, yana cewa mulkinta ya jefa ‘yan Najeriya cikin tsananin talauci.

Ya kara da cewa zai ci gaba da aiki tare da masu kishin kasa domin dawo da kyakkyawan shugabanci a Najeriya, tare da samarwa Shuwagabannin da zasu Dora Kasar kan turbar data dace.

Shekaru 60 da Rasuwar Tafawa Balewa: Yadda aka Kashe Firayi Ministan Najeriya na Farko Juyin Mulki na 1966A yau, 15 ga w...
15/01/2026

Shekaru 60 da Rasuwar Tafawa Balewa: Yadda aka Kashe Firayi Ministan Najeriya na Farko Juyin Mulki na 1966

A yau, 15 ga watan Janairu, Najeriya take tunawa da cika shekaru 60 da rasuwar Firayim Ministanta na farko, marigayi Sir Abubakar Tafawa Balewa, wanda aka hallaka a juyin mulkin soji na ranar 15 ga Janairu, 1966. Wannan rana ta kasance mai cike da bakin tarihi, domin ita ce ranar da aka rasa manyan jagororin Arewa, ciki har da Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto.

A safiyar ranar juyin mulkin, wasu sojoji s**a kaddamar da farmaki a manyan biranen kasar, inda s**a sace Sir Abubakar Tafawa Balewa daga gidansa da ke Legas. Bayan sace shi, ba a sake ganinsa ba har sai bayan wasu 'yan kwanaki, lokacin da aka tsinci gawarsa a gefen hanyar Legas zuwa Abeokuta. Daga nan ne aka kai gawarsa zuwa mahaifarsa Bauchi, inda aka binne shi bisa al’adar Musulunci da karramawa.

Juyin mulkin na 1966 ya kasance daya daga cikin manyan al’amuran da s**a sauya akalar siyasar Najeriya, domin ya kawo karshen gwamnatin farar hula ta farko, tare da bude kofar mulkin soja a kasar. Mutuwar Tafawa Balewa ta bar babban gibi a shugabanci, kuma ya haifar da rashin tsakanin 'yan Arewa da Kuma 'yan kudu.

Marigayi Tafawa Balewa ya shahara da kishin kasa, hakuri da kokarinsa na gina Najeriya mai hadin kai bayan samun ‘yancin kai. Yayin da ake tunawa da rasuwarsa bayan shekaru 60, al’ummar Najeriya na ci gaba da tuna darussan rayuwarsa, tare da yi masa addu’ar Allah Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya kuma saka masa da Aljannatul Firdaus, tare da dorewar zaman lafiya da hadin kai a kasar.

Hauhawar farashi a Nijeriya ya karu da kaso 15 cikin 100, karon farko cikin watanni takwas.Cikakken Rahoton Na Comment S...
15/01/2026

Hauhawar farashi a Nijeriya ya karu da kaso 15 cikin 100, karon farko cikin watanni takwas.

Cikakken Rahoton Na Comment Section 👇

Shugabar Hukumar Zabe ta kasar Uganda ta sanar da tsawaita lokacin kada kuri’a da awa guda, inda za a rufe rumfunan zabe...
15/01/2026

Shugabar Hukumar Zabe ta kasar Uganda ta sanar da tsawaita lokacin kada kuri’a da awa guda, inda za a rufe rumfunan zabe da karfe 5:00 na yamma agogon kasar, sakamakon matsalolin na’urori da kuma wasu kalubalen dabaru da s**a haifar da jinkiri a farkon zaben.

Shugaban Hukumar Zaben, Mai shari’a Byabakama Simon, ya bayyana cewa matakin ya zama dole domin bai wa masu kada kuri’a damar kammala zaben su bayan jinkirin da aka samu a wasu rumfunan zabe. Ya jaddada cewa tsawaita lokacin zai taimaka wajen tabbatar da adalci da gaskiya a tsarin zaben.

Sai dai hukumar ta bayyana cewa ‘yan kasa da ke tsaye a layukan rumfunan zabe zuwa karfe 5:00 na yamma ne kawai za a bari su kada kuri’arsu, yayin da wadanda s**a zo bayan wannan lokaci ba za su samu damar yin zabe ba. Wannan sanarwa na zuwa ne yayin da ake ci gaba da gudanar da zaben a sassan kasar Uganda.

Bankin Duniya ya nuna cewa tattalin arzikin Nijeriya na tafiya kan hanyar samun ci gaba mafi girma cikin sama da shekaru...
15/01/2026

Bankin Duniya ya nuna cewa tattalin arzikin Nijeriya na tafiya kan hanyar samun ci gaba mafi girma cikin sama da shekaru goma, bayan da ya kara hasashen bunkasarsa zuwa kashi 4.4 cikin 100 a shekarun 2026 da 2027. Wannan sabon hasashe na nuni da kyakkyawan fata game da makomar tattalin arzikin kasar.

An bayyana wannan ci gaba ne a cikin sabon rahoton Bankin Duniya kan tattalin arzikin kasashen duniya, wanda aka fitar a ranar Talata. Rahoton ya jaddada cewa Nijeriya na daga cikin kasashen da ake sa ran za su samu ingantaccen ci gaban tattalin arziki a nan gaba.

Sabon hasashen ya zarce wanda aka fitar a watan Yuni da ya gabata, lokacin da Bankin Duniya ya kiyasta cewa tattalin arzikin Nijeriya zai bunkasa da kashi 3.7 cikin 100 a shekarar 2026 da kashi 3.8 cikin 100 a 2027. Wannan karin kashi na nuna yadda hasashen ke kara inganta idan aka kwatanta da na baya.

Dangote da BUA sune Manyan Attajiran Afirka da Dukiyarsu Ke Kara Habaka a 2026Attajirin Afirka mafi kudi, Aliko Dangote,...
15/01/2026

Dangote da BUA sune Manyan Attajiran Afirka da Dukiyarsu Ke Kara Habaka a 2026

Attajirin Afirka mafi kudi, Aliko Dangote, ya fara shekarar 2026 da gagarumin karin dukiya, inda dukiyarsa ta karu da dala miliyan 451 cikin makonni biyu na farko na shekarar, ta kai dala biliyan 30.4. Wannan ci gaba ya tabbatar da shi a matsayin mutum mafi arziki a Afirka, sannan na 79 a jerin attajiran duniya, kamar yadda rahoton Bloomberg zuwa 15 ga Janairu, 2026 ya nuna.

A gefe guda kuma, wani dan kasuwa daga Nijeriya, Abdul Samad Rabiu, shi ma ya samu karin dukiya da ta kai dala miliyan 328 a cikin lokaci guda, inda adadin dukiyarsa ya kai dala biliyan 10.8. Hakan ya sanya Rabiu ya zama mutum na hudu mafi arziki a Afirka kuma na 337 a duniya, inda shi ma tare da Dangote dukkansu ‘yan asalin birnin Kano ne a Arewacin Nijeriya.

Sauran attajiran Afirka da dukiyarsu ta karu tun farkon shekarar 2026 sun hada da Johann Rupert daga Afirka ta Kudu, wanda dukiyarsa ta karu da dala miliyan 70.9 ta kai dala biliyan 19.5. Rahoton ya nuna cewa duk da kalubalen tattalin arziki a duniya, manyan ‘yan kasuwa a Afirka na ci gaba da habaka dukiyarsu.

Manyan Ayyuka da Abdul Samad Rabiu ya aiwatar a Arewacin Nijeriya(daga 2023 zuwa yanzu)1. Ginin dakin laccoci (Lecture T...
15/01/2026

Manyan Ayyuka da Abdul Samad Rabiu ya aiwatar a Arewacin Nijeriya
(daga 2023 zuwa yanzu)

1. Ginin dakin laccoci (Lecture Theatre) na Naira miliyan 350
– Jami’ar Jihar Adamawa (2025)

2. Cibiyar kirkire-kirkire da fasaha (Innovation Centre) ta Naira biliyan 1
– Jami’ar Maiduguri (2023)

3. Ginin dakunan kwanan dalibai (Students’ Hostel) na Naira miliyan 310
– Jami’ar Tarayya ta Fasaha, Minna – FUT Minna (2025)

4. Asibitin kula da ‘yan sanda (Police Reference Hospital) na Naira biliyan 4
– Abuja (2024)

5. Hadin gwiwa kan ayyukan kiwon lafiya tare da USAID

Address

Karu, Abuja Nigeria �
Abuja
900013

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Munam Africa News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Munam Africa News:

Share