24/7

24/7 Wannan shafi mun kirkira ne domin kare martabar addinin musulunci da musulmai dake duniya baki daya.

Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa (FRSC) ta tabbatar da mutuwar mutane 35 sak**akon mummunar gobarar da ta tashi daga tanka...
22/10/2025

Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa (FRSC) ta tabbatar da mutuwar mutane 35 sak**akon mummunar gobarar da ta tashi daga tankar mai da ta yi hatsari a kan hanyar Bida zuwa Lafai, bayan an wuce Badegi, a ranar Talata.

Rahotanni sun nuna cewa waɗanda abin ya rutsa da su sun kone kurmus har lahira, yayin da suke ƙoƙarin kwasar mai daga tankar da ta yi hatsari.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar a yammacin Talata, FRSC ta bayyana damuwa kan wannan masifa wacce ta faru sak**akon rashin bin ƙa’idoji, son kai, da watsi da gargadin kiyaye lafiya.

Hukumar ta ce tawagar agajin gaggawa ta isa wurin da lamarin ya faru da misalin ƙarfe 12:15 na rana, lokacin da tankar mai ɗauke da fetur ta subuce saboda munin hanya, ta kuma hantsila.

Jim kaɗan bayan hatsarin, mazauna yankin s**a taru suna ƙoƙarin kwasar mai daga cikin tankar da ta fadi, sai dai nan take ta k**a da wuta wacce ta hallaka mutane 35 tare da jikkata wasu 46.

19/10/2025
Shin kuna ganin za'a saki Mlm Abduljabar?
03/10/2025

Shin kuna ganin za'a saki Mlm Abduljabar?

Najeriya ta zama ƙasa ta biyu mafi yawan talakawa a duniya – Yemi KaleNajeriya ta zama ƙasa ta biyu a duniya da ta fi ya...
03/10/2025

Najeriya ta zama ƙasa ta biyu mafi yawan talakawa a duniya – Yemi Kale

Najeriya ta zama ƙasa ta biyu a duniya da ta fi yawan mutane da ke rayuwa cikin talauci, in ji Yemi Kale, tsohon shugaban hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS).

Kale ya bayyana cewa sama da mutane miliyan 89, wato kusan kashi 40 cikin 100 na ‘yan Najeriya, na rayuwa a ƙasa da matakin talauci. Ya ce kawai Indiya ce ta fi Najeriya yawan talakawa a duniya.

Tsohon shugaban na NBS ya yi wannan jawabi ne a wani taro na musamman da aka shirya domin bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ‘yancin kai, mai taken The Platform Nigeria’s Independence Day event, a birnin Legas.

A cewarsa, jinkirin ɗaukar matakan gyara da kuma wasu manufofin tattalin arziki marasa inganci sun jefa ƙarin mutane cikin wahala. Ya ce hauhawar farashi, tsadar rayuwa da ƙarancin aikin yi na daga cikin manyan dalilan da ke sa talauci ƙaruwa a ƙasar.

Yemi Kale ya ce duk da cewa gwamnati ta fara aiwatar da wasu gyare-gyare masu wahala, k**ata ya yi a yi su tun sama da shekaru goma da s**a gabata. “Mun rasa damar da ta k**ata a yi amfani da ita kafin al’amura su ta’azzara,” in ji shi.

Ya yi gargadin cewa waɗannan gyare-gyaren kada su tsaya kawai a ɓangaren tattalin arziki, sai dai a haɗa su da tsare-tsaren tallafin jama’a domin rage radadi ga marasa galihu.

“Gaskiya, bayyana abubuwa yadda suke, da kuma amincewa da gaskiya wajen aiwatar da matakai ne kadai za su iya sa Najeriya ta farfaɗo daga wannan mummunar matsala,” in ji Kale.

An nada Oluremi Matar  Tinubu mukamin Sarauniyar Yakin Kumo a jihar Gombe
02/10/2025

An nada Oluremi Matar Tinubu mukamin Sarauniyar Yakin Kumo a jihar Gombe

Shugaban kasar Columbia PETRO ya Mayar wa da Donald trump Martani"America ta kwace Visa ta domin shiga America to ni Ban...
02/10/2025

Shugaban kasar Columbia PETRO ya Mayar wa da Donald trump Martani

"America ta kwace Visa ta domin shiga America to ni Ban damu ba Hasali ma bana bukatar sake shiga America.

Ni mutun Ne Mai cikakken iko (Ba irin larabawa ba) bansan amfanin shiga America ba (Dole mu Fadi zaluncin America da Isra'ila)

02/10/2025

Jirgin yakin America Mafi Girma wat B-2 Ya dauki kayan yaki ya nufi Gabas Ta Tsakiya

An ruwaito cewa Akwai yiyuwar Iran Ce Target

Address

Abuja

Opening Hours

Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when 24/7 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share