Arewa For Asiwaju

Arewa For Asiwaju Relief Is Coming.....
(1)

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gy...
02/08/2025

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gyara Jam’iyya Cikin Gaskiya

Ofishinmu na Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) yana bayyana damuwarsa matuka kan yadda wasu sarakunan gargajiya ke kiran waya da nufin matsin lamba ga Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar, Alhaji Nafiu Bala Gombe, domin ya sauya matsayinsa na kare tsarin dimokuradiyya da doka na jam’iyyar.

Wannan barazana da kuma kiran da ake yi ga wasu mambobin Kwamitin Zartaswa na Kasa (NWC) domin su ja da baya daga goyon bayan shugabansu, abin takaici ne kwarai, musamman ganin cewa sarakuna sun bar turbarsu ta raya al’adu da zaman lafiya, sun rungumi muradin wasu 'yan siyasa masu son karbe jam’iyya ta kowane hali.

MAKIRCI NA BAYA-BAYAN NAN

Bayanan sirri daga majiya mai karfi na nuni da cewa wasu manyan ’yan siyasa da s**a hada da Janar David Mark da Mallam Nasir El-Rufai da wasu gungun mutane sun hada wata kungiya da ke shirin tura dattawa su je Gombe domin matsawa mahaifiyar Shugaban rikon kwarya da nufin tilasta masa mika jam’iyyar da nufin cinma burinsu na siyasa a shekarar 2027.

Wannan yunkuri na ziyarar mahaifiyar Shugaban jam’iyyar abu ne da ba za mu lamunta da shi ba. Hakan na nuna cewa wasu sun sadaukar da dimokuradiyya ga son zuciya da yin coge don biyan muradinsu na 2027.

1. Muna da tabbaci daga bayanen sirri masu inganci cewa wadannan sarakuna na kokarin tilasta Alhaji Nafiu Bala Gombe ya mika jam’iyya ga 'yan siyasa masu matasanancin kwadayin mulki ta hanyar matsa masa da kiraye-kiraye a wayarsa tare da shisshigi a boye. Wadannan sarakuna ba su kyauta ba, saboda suna neman rage kima da martabar al'adunmu masu nagarta ta hanyar neman zama 'yan koren masu mayatar son mulkin siyasa a shekarar 2027. Wannan abin jimami ne ga dukkan mai kishin martabar masarautinmu.

2. Wannan kuskure ne mai muni daga bangaren sarakuna, wadanda ya k**ata su tsaya a gefe su kasance iyayen kasa masu kima.

3. Mu na kara fayyacewa: Sarakuna ba su da hurumin shiga harkokin jam’iyyar ADC ko zama 'yan gada-gadar 'yan siyasa. Wannan ba shekarar 1983 ba ce; yanzu idon kowa a bude yake. ADC ba ta sayarwa ba ce!

4. Alhaji Nafiu Bala Gombe ba zai ja da baya ba, yana da cikakken goyon bayan dokokin jam’iyya da mambobinta masu kishin kasa.

5. Wadanda suke fakewa da cewa suna hidimar “sasantawa”, yaudarar jama'a suke, da nufin biyan muradin 'yan cogen Hadaka ta Zaben 2027. Su sani cewa za mu bayyana sunayensu da cikakken bayani game da boyayyiyar manufarsu, in bukatar yin hakan ta taso.

6. Ga wadanda suke matsayin sarakuna amma s**a tsunduma siyasa da goyon bayan hargitsi, muna ba ku shawara: ku koma ku kula da masarautunku. Kada ku sayar da martabarku da al'adunmu masu nagarta don biyan bukatun 'yan siyasan da s**a shahara wajen yaudarar al'umma shekara da shekaru.

MATSAYARMU A KAN WANNAN KATSALANDAN:

Jam’iyyar ADC ba ta sayarwa ba ce. Ba za mu bar makircin wasu mayaudaran 'yan siyasa ya kassara mulkin dimokuradiyyan kasar nan ba, ko ya lalata alkiblar jam’iyyar ADC ba. Kuma za mu fallasa kowane mai hannu a ciki — ko saraki ne shi ko dan bangar siyasa.

In kunne ya ji, jiki ya tsira.

Sanya hannu:
Dr. Aminu Sani Alhassan
Mai Baiwa Shugaban Rikon Kwarya Shawara kan Harkokin Jama’a
Jam'iyyar African Democratic Congress (ADC)
Abuja

Cikin Hotuna:Yadda membobin taron Progressive Digital Media Summit na kwanaki biyu ke shiga layi domin shiga babban Ɗaki...
31/07/2025

Cikin Hotuna:Yadda membobin taron Progressive Digital Media Summit na kwanaki biyu ke shiga layi domin shiga babban Ɗakin taro na fadar mulki ta Aso-Villa dake nan Abuja, domin karin kumallo da fara gabatar da taron nan take.

Arewa for Asiwaju za ta ci gaba da kawo muku yadda taron zai gudana a yau Asabar rana ta biyu na taron kuma rana ta ƙarshe da za a kammala.

Karya Ce Tsagwaronta: Muhammad Babangida Bai Ƙi Nadin Da Shugaba Tinubu Yayi Masa Ba Wasu mutane masu ƙazamin nufi sun b...
21/07/2025

Karya Ce Tsagwaronta: Muhammad Babangida Bai Ƙi Nadin Da Shugaba Tinubu Yayi Masa Ba

Wasu mutane masu ƙazamin nufi sun bazu da wani labari mara tushe a kafafen sada zumunta da ke cewa Muhammad Babangida, ɗan tsohon shugaban kasa Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya ƙi amincewa da nadin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya masa na chairman BOA.

Mun tabbatar da cewa wannan labarin ƙarya ne tsagwaronta, domin ba Muhammad Babangida bane ya fitar da sanarwar da ke yawo ba. Lambar da ke jikin takardar da aka yaɗa da kuma sa hannun da ke cikinta duk ba nasa ba ne.

Wannan wata makirci ce ta ɓatanci da ƙoƙarin jefa shakku a tsakanin shugaban ƙasa da manyan 'yan Najeriya, musamman waɗanda ke da sunaye da martaba a cikin al'umma.

Muhammad Babangida bai fito ya musanta nadin ba, kuma babu wata cikakkiyar shaida daga gare shi ko daga hannunsa da ke nuna ya ƙi karɓar kujerar. Wannan yana nuni da cewa an ƙirƙiri wannan labari ne domin yaudarar jama'a da haddasa ruɗani.

Muna kira ga 'yan Najeriya da su yi hattara da labaran ƙarya da ake yawan yaɗawa, su nemi gaskiya daga ingantattun majiyoyi kafin yarda da kowace irin sanarwa.

Allah ya ƙara haɗin kanmu da cigaban ƙasar nan.

Kada Ku Sake Yin Amfani da Mutuwar Buhari Don Cimma Manufarku Ta Siyasa — Matasan Arewa Sun Gargadi Atiku da El-RufaiKun...
19/07/2025

Kada Ku Sake Yin Amfani da Mutuwar Buhari Don Cimma Manufarku Ta Siyasa — Matasan Arewa Sun Gargadi Atiku da El-Rufai

Kungiyar Matasa Ta Arewa (Northern Youth Frontiers) ta bayyana damuwarsu kan yadda wasu 'yan siyasa ke ƙoƙarin amfani da rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari domin yaudarar mutane da neman samun goyon bayansu.

A cewar kungiyar, Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai sun nuna k**ar su abokai ne na Buhari domin su karɓi ƙaunar jama'a, alhali sun shafe shekaru suna adawa da akidu da manufofin Buhari tun yana raye.

Wannan abin da suke yi ruɗi ne, karya ce, kuma cin fuska ne ga marigayin shugaban da ya sadaukar da rayuwarsa ga ƙasar nan.

Kungiyar ta ce waɗannan 'yan siyasa ba su taɓa goyon bayan Buhari ba, kuma yanzu suna ƙoƙarin nuna soyayya ta bogi domin su karɓi ra'ayin mutanen Arewa — musamman bayan mutuwar sa.

“Matasan Arewa ba za su bari a ci zarafin Buhari ba.”

Matasan sun ce ba za su yarda a yi amfani da mutuwar Buhari a matsayin hanyar da za a fake domin yaudarar al’umma ba. Sun kuma roƙi jama’ar Arewa da su yi hankali da siyasar ruɗu da wasu ke ƙoƙarin kawowa a cikin lokaci mai muhimmanci na jimami da girmamawa.

Mutuwar Buhari ba siyasa bace. Lokaci ne na tunani da haɗin kai, ba na neman karɓuwa da nuna ƙarya ba.”

Kungiyar ta ƙara da cewa Atiku da El-Rufai su dakata da wannan salon siyasa, su girmama Buhari, su kuma bar mutanen Arewa su zaɓi gaskiya da amintattu, ba masu nuna soyayya ta ɗan lokaci ba.

Ku dakata da fakewa da mutuwar Buhari. Mutumin da kuka ƙi a raye, ba ku da ikon fakewa da shi bayan ya rasu.

✍️ Northern Youth Frontiers
Sakon Gargaɗi daga Matasan Arewa

Ba Za Mu Lamunci Atiku Da El-Rufai Su Siyasantar Da Mutuwar Buhari Ba, Tare Da Cin Moriyar Mutuwar A Wajen Zaman Makokin...
18/07/2025

Ba Za Mu Lamunci Atiku Da El-Rufai Su Siyasantar Da Mutuwar Buhari Ba, Tare Da Cin Moriyar Mutuwar A Wajen Zaman Makokinsa Ba, Cewar Kungiyar DWI

Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta bayyana matuƙar ɓacin ranta da yadda Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai s**a nuna halayen son zuciya da ƙaŕaiŕàyi a lokacin jana’izar tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari. A yayin da mutane ke cikin alhini, su kuma sun sauya jana’izar zuwa wata dama ta siyasa don yaudarar jama’a da neman tagomashi.

Atiku da El-Rufai sun nuna kansu k**ar su ne masoyan Buhari na hakika, alhali tarihi ya tabbatar da cewar sun sha s**a da yakar manufofinsa da akidunsa. Wannan yunkuri nasu, ba wai kawai rashin gaskiya ba ne, har ma da rashin mutunta irin gudunmawar da Buhari ya bayar ga ƙasa, da kuma wulakanta ra’ayin al’umma da ke makoki.

Ya k**ata a tuna cewa Atiku ya fara zama babban abokin adawar Buhari tun shekarar 2003, inda ya tsaya takara da shi a zaɓuka da dama. A tarihi, Atiku yana canza jam’iyya bisa la’akari da ribar kansa, ba don wata akida ba. Ya bar PDP ya koma APC lokacin da Buhari ke da tasiri, sannan ya sake komawa PDP da zarar Buhari ya ci zaɓe. Wannan yana nuna halin rashin gaskiya da son zuciya da ke tattare da siyasar Atiku.

A gefe guda kuwa, El-Rufai wanda ya dade yana jinƙayar Buhari da jama’arsa, ya bayyana a jana’iza yana kokarin nuna wata tsantsar goyon baya da ba ta taɓa kasancewa da shi ba. Wannan hanya ce ta neman amincewa da mutanen Arewa cikin lokaci mai rauni da radadi.

Kungiyar DWI tana kira ga al’ummar Najeriya musamman ‘yan Arewa da su kasance masu hankali da fahimta. Kada mu bari wasu yan siyasa su ci moriyar makokinmu da tarihin mutanen kirki k**ar Buhari. Ya k**ata a tuna da makircin da waɗannan mutane s**a aikata a baya da kuma yadda s**a kasance masu son kansu da rashin kishin kasa.

DWI tana nan daram a kan matsayinta na cewa siyasar yaudara ba za ta samu karbuwa ba. Muna roƙon kowa da kowa da ya mutunta rayuwa da gado da Buhari ya bari – rayuwar gaskiya, tsantseni da kishin kasa.

A ƙarshe, muna tir da yunkurin Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai na sauya jana’izar Buhari zuwa dandamalin siyasa. Muna kira da a ci gaba da tuna irin gudunmawar Buhari ba tare da bari wasu su yi amfani da sunansa don biyan bukatunsu na siyasa ba.

Democracy Watch Initiative

Shekaru Biyu A Gwamnatin Da Ta Dawo Da Martabar Jihar  KanoA lokacin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya hau karagar mulki a r...
04/06/2025

Shekaru Biyu A Gwamnatin Da Ta Dawo Da Martabar Jihar Kano

A lokacin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya hau karagar mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023 al’ummar Kano sun fara ganin sauyi na gaske. Sauyin da ya tabbatar da aiki, tsare-tsare, da kula da lafiyar al’umma da tattalin arziki wannan ba mulki ba ne na alkawari kawai, wannan mulki ne mai cike da aiki da cika alkawari.

A cikin shekaru biyu kacal, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tabbatar da cewa mulki nagari ba a magana ba ne, aiki ne da kishin al'umma

A bangaren noma da ban ruwa, sama da hectare dubu an samar da su domin noman rani, tare da gine-ginen dam-dam a kananan hukumomi fiye da goma sha biyu.

A fannin lafiya, an cire dubban masu rijista na bogi, an dauki matakan inganta kulawa da marasa lafiya, tare da shigar da dubban talakawa cikin tsarin lafiya kyauta.

Gwamnatin Abba ta kawo karshen matsalar rashin magunguna a asibitoci, ta kafa cibiyoyi na musamman da samar da injinan iskar oxygene masu amfani da hasken rana.

An ba da kulawa ta musamman ga yara da mata masu fama da cututtuka ta hanyar shirin ABBACARE, tare da tallafawa masu sikila da marasa galihu.

Tsarin rajista da kididdiga na zamani (EMR) ya kara inganta tsarin lafiya da sarrafa bayanai a asibitoci fiye da goma.

Gaskiya ce, Gwamna Abba Kabir Yusuf yana aiki tukuru, yana gina jihar Kano bisa gaskiya, adalci da amana. Wannan gwamnatin ba ta yi alkawarin da ba ta cika ba cikin shekara biyu da fara mulkin jihar Kano!

ABAISWORKING
📅 29th May, 2025
Wanda ya shuka nagarta, shi zai girbi tagomashi

AJAM Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Nasarorin Da Ta Cimma Wajen Dawo da Zaman Lafiya a ArewaGamayyar Kungiyar Ayyukan ...
01/06/2025

AJAM Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Nasarorin Da Ta Cimma Wajen Dawo da Zaman Lafiya a Arewa

Gamayyar Kungiyar Ayyukan Arewa (AJAM) ta jinjina wa Gwamnatin Tarayya bisa manyan nasarori da ta samu wajen dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin Arewa, wanda da can ya kasance cike da matsalolin ta’addanci da miyagun laifuka.

Kungiyar ta bayyana musamman rawar da Ma'aikatar Tsaro ke takawa wajen aiwatar da manyan ayyukan tsaro masu amfani da fasahar zamani a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa maso Tsakiya.

A cikin wata sanarwa da mai jagorantar kungiyar, Lauretta Bako ta fitar a ranar Alhamis, AJAM ta bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba a fannin tsaro a yankin, wanda hakan ya biyo bayan dabarun rundunonin tsaro da gwamnatin ke aiwatarwa.

"A yau muna rayuwa a wani sabon yanayi na tsaro fiye da da, inda aka kore Boko Haram zuwa matsugunan duhu, yayin da shugabannin masu garkuwa da mutane da ‘yan bindiga s**a hallaka ko s**a tsere."

"Nasarorin da aka samu wajen kawar da ‘yan bindiga, ‘yan ta’adda da kuma sarkakiyar hanyoyin aikata laifi, tare da farfado da tattalin arzikin yankuna, ya nuna ingancin wannan tsari."

A cewar AJAM, daya daga cikin ginshikan wannan nasara shine Operation FANSAR YAMMA, wanda ya samu nasarori da dama, ciki har da hallaka sanannen shugaban ‘yan bindiga, Kachalla Dogo Isah, tare da wasu ‘yan ta’adda 44 a jihar Zamfara.

Sanarwar ta kara da cewa, “Kashe fitattun masu aikata laifi ciki har da masu sayar da mak**ai da shugabannin ‘yan bindiga ya tarwatsa manyan hanyoyin aikata laifi, tare da isar da sako ga sauran masu laifi cewa gwamnati ba za ta yarda da rashin tsaro ba.”

Tasirin wadannan matakan tsaro ya wuce kidayar alkaluma kawai; yana da tasiri kai tsaye ga rayuwar yau da kullum ta ‘yan kasa. Hanyoyi k**ar hanyar Kaduna-Abuja, wanda da can aka fi jin tsoro, yanzu sun fi aminci ga matafiya, hakan kuma yana taimakawa wajen kasuwanci da zirga-zirga.

Kasuwanni a wurare irin su Giwa, Birnin Gwari da Jibia suna samun sabuwar rayuwa, inda shugabannin al’umma da jama’a ke tabbatar da ingancin tsaro. Farfadowar harkokin kasuwanci na da nasaba kai tsaye da nasarorin da sojoji s**a samu tare da samar da yanayi mai kyau ga kasuwanci.

Gina Brigade na National Mission Force a Samaru Kataf shima ya taka rawa wajen warware matsalolin tsaro a Kudu ta Kudancin Kaduna, wanda ya haifar da ingantattun yanayin zamantakewa da tattalin arziki. A cikin watanni ukun farko na shekarar 2025 kadai, an hallaka ‘yan ta’adda 122 kuma an k**a fiye da 1,000 daga cikin masu laifi.

A matsayinmu na Arewa Joint Action Movement, muna tare da kokarin da Ma’aikatar Tsaro ke yi wajen kare al’ummominmu da dawo da fata a zukatan jama’a. Muna fahimtar cewa har yanzu akwai kalubale, amma nasarorin da aka samu sun haskaka mana hanya. Zamu ci gaba da goyon bayan manufofi da matakan da za su kawo zaman lafiya, tsaro da cigaba mai dorewa a Arewarmu.

Peter Obi Ya Karyata Jita-Jitar Zama Mataimakin Atiku A Zaben 2027 – Inji Obidient MovementDaga Comr Haidar H Hasheem Ob...
19/05/2025

Peter Obi Ya Karyata Jita-Jitar Zama Mataimakin Atiku A Zaben 2027 – Inji Obidient Movement

Daga Comr Haidar H Hasheem

Obidient Movement ta bayyana cewa rahoton da ke yawo a kafafen yada labarai na cewa tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP a zaben 2023 Mr. Peter Obi ya amince ya zama mataimakin Alhaji Atiku Abubakar a wani sabon hadin gwiwar siyasa da ake kokarin kafa wa gabanin zaben 2027, karya ne kuma babu gaskiya a cikin rahotan.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Nana Kazaure, Daraktar Sadarwa da Tsare-Tsare ta kungiyar, ta fitar a ranar 19 ga Mayu, 2025, inda ta bayyana cewa rahoton ya kasance kirkirar wasu marubuta ne kawai, kuma hakan yana iya janyo rudani da kuskuren fahimta a tsakanin jama'a.

Ta ce ko da yake ana ci gaba da gudanar da tattaunawa cikin lumana da wasu manyan ‘yan siyasa da masu ruwa da tsaki don samar da hadakar da za ta ceto Najeriya, babu wata tantama cewa Mr. Obi bai amince da mukamin mataimaki ba, kuma babu wata yarjejeniya da ta shafi hakan.

Sanarwar ta bayyana cewa manufar Mr. Obi da Obidient Movement ita ce samar da cikakken hadin kai don yaki da mulkin rashin nagarta, cin hanci da rashawa, yunwa, talauci, matsalar kiwon lafiya, da karancin ilimi ga yara ba siyasar karbar mukami kawai ba.

Kungiyar ta sake jaddada cewa Mr. Obi har yanzu na cikin jam’iyyar Labour Party, kuma idan zai sauya sheka ko jam’iyya a nan gaba, zai bayyana hakan da kansa.

Daga karshe, Obidient Movement ta bukaci 'yan Najeriya da kafafen yada labarai da su kauce wa yada jita-jita da rahotannin da ka iya tada tarzoma saboda rashin tushe, su maida hankali wajen taimakawa tare da gina Najeriya mai inganci da adalci.

Ranar: 19/05/2025
Sa hannu: Nana Kazaure, Daraktar Sadarwa da Tsare-Tsare, Obidient Movement

05/05/2025

Ikon Allah!

Katafaren ginin gidan alfarma kenan da Kauran Bauchi ya ginawa kansa don jindadinsa da samun kwanciyar hankalinsa.

Ministan Tsaron Nigeria, Mohammed Badaru Abubakar, Ya Karɓi Baƙuncin Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya Kan Harkokin Jinƙai...
30/04/2025

Ministan Tsaron Nigeria, Mohammed Badaru Abubakar, Ya Karɓi Baƙuncin Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya Kan Harkokin Jinƙai

A ranar Talata, 29 ga Afrilu 2025, mai girma Ministan Tsaro na Ƙasa, H.E. Mohammed Badaru Abubakar, CON, mni, ya karɓi baƙuncin Mr. Mohamed Malick Fall, wanda shi ne Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya a Najeriya kuma mai kula da harkokin jinƙai.

Tattaunawar wanda aka gudanar a ofishin Ministan dake Ship House, Abuja, ta mayar da hankali ne kan yadda Najeriya za ta ƙara tallafawa ayyukan jinƙai da Majalisar Ɗinkin Duniya ke gudanarwa a ƙasar.

Me za ku ce kan ajiye mukamin da Dr Hakeem Baba Ahmed yayi?Dr Hakeem Baba Ahmed, shine tsohon mai magana da yawun kungiy...
04/04/2025

Me za ku ce kan ajiye mukamin da Dr Hakeem Baba Ahmed yayi?

Dr Hakeem Baba Ahmed, shine tsohon mai magana da yawun kungiyar Dattawan Arewa, shine za kuji kullum yana kalubalantar Gwamnati a duk inda tayi kuskure a gidajen Rediyo da Television da kafofin sada zumunta.

Tun ranar da Tinubu ya bashi mukamin mai bashi shawara ya turashi Ofis din Kashim aka daina jin duriyarshi, ya daina cewa komai akan sha'anin kasar.

Yasha caccaka da shagube iri-iri a wurin al-umma, yau da safe kwatsam sai ga sanarwar ya ajiye mukaminshi a jaridar Daily Trust.

ƊAN BELLO ƘATON MAƘARYACI NE KUMA AZZALUMI.Sanarwa daga Jibwis Nigeria ✍️Na kalli Video da Dan Bello yayi yana zargin Sh...
01/04/2025

ƊAN BELLO ƘATON MAƘARYACI NE KUMA AZZALUMI.

Sanarwa daga Jibwis Nigeria ✍️

Na kalli Video da Dan Bello yayi yana zargin Sheikh Abdullahi Bala Lau da kungiyar Izala da karban kudi a hanun Gwamnatin tarayya da sunan gina ajujuwa, kuma yake cewa wai an cinye kudin ba'ayi aikin ba.

Abunda ya bani mamaki shine yanda tsananin son ɓata sunan Malamai ya rufewa Dan Bello ido ya gagara gane description na aikin gine-ginen ajujuwan da yake magana akai, wanda duk wanda yake da ilimi kuma ya sanya nutsuwa zai gane meye abun yake nufi cikin sauki.

Aiyyukan ginin ajujuwa da Dan Bello ya nuna, CONSTITUENCY PROJECTS na HON. MUKHTAR ALIYU BETARA, Dan Majalisar tarayya mai wakiltar Bayo/Biu/Kwaya-Kusar... Federal Constituency a Majalisar Wakilai.

Yanda description na aikin yake shine, Hon. Mukhtar Betara ya saka zai gina ajujuwa wa kungiyar Izala da Sheikh Bala Lau yake jagoranci, wacce itace ake cewa "IZALA KADUNA", haka nan zai gina ajujuwa a makarantun kungiyar Izala da Sheikh Muhammad Sani Yahaya Jingir yake jagoranci, wacce ita ake nufi a takaddar da cewa IZALA JOS, kuma zai ginawa yan Darika ma har bangarori biyu, dukka za'ayi wannan gini ne a Kwaya-Kusar LGA Borno State, k**ar yanda yake jikin screenshot da nayi attaching a kasa.

Sunan JOS da KADUNA da akayi amfani dashi ba anyi ne don bambancewa tsakanin Izala 1&2, ba wai aiyyukan a JOS da KADUNA suke ba, k**ar yanda shi Dan Bello ya fada.

Haka nan abunda Dan Bello ya saka na cewa an ware kudade domin ginin ajujuwa a JIBWIS Collage of Education Jega, Kebbi State, shima Constituency projects ne na Senator da yake wakiltar yankin a Majalisar dattijai, Senator Muhammad Adamu Aliero, kuma Senator Aliero shi ya gudanar da aikinsa da kansa, ba kungiyar Izala aka turawa kudi ba k**ar yanda Dan Bello ya fada.

Shima wannan aikin daƙiƙi Dan Bello yace wai ba'ayi ba, kuma karya ne Senator yayi aikin k**ar yanda yayi alkawari a wani taron kaddamar da Collage din (Akwai hoton allon kaddamar da ginin da Sunan Senator Aliero, da kuma hotunan makarantar a kasa).

Wallahi tallahi na jima da gane cewa abubuwa da yawa da Dan Bello yake fada shaci-faɗi ne kawai, yana samun karbuwa ne a wajen mutane kawai saboda yana attacking shugabanni ne, sak**akon rashin jituwa da take tsakanin talakawa da shugabanni.

Duk wanda yake son fahimtar gaskiya kan abunda na fada, ya nutsu ya sake kallon video Dan Bello with an open and objective mind.

Lalle Ɗan Bello ya tabka kuskure a wannan bincike da yace yayi, wanda ke ciki da sharri da cin mutunci ga shugaban mu, wannan kuma ya kara tabbatar mana da cewa akwai waɗanda suke ɗaukar nauyin sa da bashi bayanan ƙarya, domin biyan buƙatar kan su.

Da farko dai yace Sheikh Abdullahi Bala Lau Yana da akawun sunfi guda talatin, wannan ƙarya ne tsagworanta, zamu so ya kawo mana cikekken bayani akan waɗannan akawun guda talatin da ya faɗa ɗaya bayan ɗaya.

Duk waɗannan zarge-zarge da Ɗan Bello yayi basu da alaƙa da Sheikh Bala Lau ko ofishin sa a matakin ƙasa, kuma bai san da su ba.

A ƙusa da ƙarshe Ɗan Bello ya bada adireshin wani office a garin Lau dake jahar Taraba, wannan ƙarya ne, Sheikh Bala Lau bayi da wani office dake zama a Lau mallakar sa, in banda gidansa wanda in yaje garin yake sauƙa da iyalansa.

A ƙarshe Ɗan Bello ya ƙarƙare da cin mutuncin shugaban mu da ƙiransa da suna na ƙasƙanci.

Matsayar mu: Da farko dai mun kai ƙararsa wajen Allah, tare da addu'ar Allah ya nuna misali da shi, shi da dukkan masu aiki irin nasa, su girbi abun da s**a shuka tun anan duniya.

Abu na biyu, zamu je kotu da shi domin yazo ya bada dukkan bayanan abun da ya faɗa, musamman yadda ya samo BVN tunda munsan ko hukuma ce zatayi bincike irin haka, sai ta nemi izini daga mahukunta, Insha Allah da Ɗan Bello da waɗanda suke temaka masa da labaran ƙarya ƙarshenku yazo, domin sai gaskiya ta bayyana Insha Allah.

Sannan akwai buƙatar Ɗan Bello yasan waye shugaba Sheikh Abdullahi Bala Lau a ɓangaren kasuwanci tun kafin ya zama shugaban JIBWIS, yafi ƙarfin waɗannan kuɗin da yake ambatawa. ~Jibwis Nigeria

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa For Asiwaju posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa For Asiwaju:

Share