Arewa For Asiwaju

Arewa For Asiwaju Relief Is Coming.....

Matasa Daga Arewacin Najeriya Sun Bukaci Tinubu Ya Sallami Ministan Tsaro Bello MatawalleƘungiyar Northern Christian You...
19/12/2025

Matasa Daga Arewacin Najeriya Sun Bukaci Tinubu Ya Sallami Ministan Tsaro Bello Matawalle

Ƙungiyar Northern Christian Youth Coalition (NCYC) ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya sallami Ministan Ƙasa na Tsaro, Dr. Bello Muhammed Matawalle, sakamakon zarge-zargen da suke nuna cewa yana da alaƙa da ta'addanci wanda tsohon hadiminsa Musa Kamarawa yayi ikirari.

A cikin wata sanarwa da Babban Kwamishinan ƙungiyar, Jeremaid Hudso Bako, ya fitar, ƙungiyar ta ce kira da take yi na nufin ƙarfafa gaskiya, riƙon amana, da dawo da amincewar jama’a ga gwamnati, musamman a bangaren tsaro.

Ƙungiyar ta yaba wa Shugaba Tinubu kan tsige tsohon Shugaban Hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed, tana mai cewa hakan alama ce ta ƙoƙarin gwamnati wajen yaƙi da cin hanci da rashawa. Sai dai ta ce ya dace a yi adalci iri ɗaya ga kowa, ciki har da Matawalle.

NCYC ta jaddada cewa zarge-zargen da ake yi wa Matawalle suna da nauyi sosai, musamman ganin cewa suna da alaƙa da tsaron ƙasa da rayukan al’umma, don haka bai dace a yi shiru a kansu ba.

Ƙungiyar ta ce idan har gwamnatin Tinubu na son a san ta da gaskiya, adalci da shugabanci nagari, to ya zama dole ta ɗauki mataki cikin gaggawa kan duk wani jami’i da ake zargi da aikata abubuwan da za su iya lalata amincin ƙasa tare da sauke ƙaramin ministan da kuma gudanar da binciken gaggawa a kansa.

Odua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan Matawalle....Zargin alaƙa da ‘yan bindiga bara...
16/12/2025

Odua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan Matawalle
....Zargin alaƙa da ‘yan bindiga barazana ce ga tsaron Najeriya.

Ƙungiyar Odua People’s Assembly (OPA) ta nuna damuwa matuƙa kan zargin da ake yi wa Ministan Tsaron Ƙasa (State), Bello Matawalle, dangane da alaƙa da ‘yan bindiga. Ƙungiyar ta ce zargin yana da hatsari ga tsaron ƙasa da amincewar jama’a.

OPA ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta gudanar da bincike mai zaman kansa, tare da sanya gaskiya kuma ba tare da son kai ba, domin fayyace gaskiyar lamarin. Ta ce rashin daukar mataki zai ƙara raunana amincewar jama’a da hukumomin gwamnati, musamman a lokacin da Najeriya ke fama da matsanancin matsalar tsaro.

Ƙungiyar ta ce bayyanar wani bidiyo da ke nuna Bello Turji, shugaban ‘yan bindiga, yana kare Matawalle abin tayar da hankali ne, domin yana nuna yiyuwar haɗin kai tsakanin jami’an gwamnati da masu laifi.

OPA ta bayyana cewa duk wata alaƙa, kai tsaye ko a kaikaice, tsakanin jami’an gwamnati da ‘yan bindiga cin amanar ‘yan Najeriya ne, musamman waɗanda s**a sha wahala sakamakon rashin tsaro.

A matsayin mataki na dawo da amincewar jama’a, OPA ta buƙaci a sauke Matawalle daga muƙaminsa nan take, tare da kafa cikakken tsari na bincike mai zaman kansa. Ta kuma gargadi cewa rashin daukar mataki mai tsauri zai ƙarfafa ‘yan bindiga tare da ƙara ta’azzara rashin tsaro.

Ƙungiyar ta bukaci ‘yan Najeriya su kasance masu faɗakarwa, su kuma riƙa kira ga alhakin shugabanni, tana jaddada cewa yaƙi da ‘yan bindiga ya zama na bai ɗaya, ba tare da la’akari da siyasa ko yanki ba.

Sa Hannun
Sunday Daniel
Mai magana da yawun Odua People’s Assembly

Yakamata Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Bincike Na Gaggawa Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga Da Musa Kamarawa Yayi Ga ...
15/12/2025

Yakamata Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Bincike Na Gaggawa Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga Da Musa Kamarawa Yayi Ga Bello Matawalle
.... Dole a gaggauta binciken Musa Kamarawa da kuma Ƙaramin Ministan Tsaron kan alaƙa da yan bindiga domin tabbatar da tsaron al'ummar Arewacin Najeriya.

Ni, Comr. Haidar H. Hasheem, ɗan Arewa kuma mai kishin zaman lafiya da tsaron ƙasa, ina bayyana damuwa mai tsanani kan manyan zarge-zargen da ke yawo a fili, musamman ikirarin da tsohon mataimaki na musamman ga tsohon Gwamnan Zamfara, Musa Kamarawa, ya yi a faifan bidiyo dangane da Ministan Tsaron Ƙasa na yanzu, Bello Matawalle.

Waɗannan zarge-zarge sun haɗa da alaƙa da ’yan bindiga, zargin tura kuɗaɗe ga fitaccen shugaban ’yan bindiga Bello Turji, sayen motocin Hilux ga yan ta'adda, da kuma tallafawa da dukiya kamar gidaje, saya musu dusa da sauran kayan more rayuwa, tare da zargin cewa wasu ’yan siyasa daga Zamfara da maƙwabtanta sun taka rawa a hakan.

Waɗannan ba ƙananan maganganu ba ne. Zarge-zarge ne masu nauyi da ke nuna yiwuwar alaƙa mai zurfi tsakanin wasu masu rike da madafun iko da ’yan bindiga, abin da ke iya rushe ƙoƙarin jami’an tsaro tare da ƙara jefa rayukan al’umma cikin haɗari.

Ina da cikakken ra’ayi cewa musantawa kawai ba za ta wadatar ba. Idan ba a yi cikakken bincike ba, shakku zai ci gaba da ƙaruwa, kuma amincewar jama’a ga gwamnati da hukumomin tsaro za ta ƙara raguwa.

Haka kuma, matakin kai ƙara kan Sheikh Murtala Asada yana iya fassaruwa a idon jama’a a matsayin yunƙurin tsoratarwa da hana faɗin gaskiya, maimakon kare mutunci. Ina kira ga Sheikh Asada da ya fito da duk wata hujja da ke hannunsa, domin gaskiya ita ce ginshiƙin adalci, haka kuma bayyana dukkan gaskiyarsa gaban kotu zai taimaka don tabbatar da kare tsaron ƙasa.

A bayyane yake cewa babu wanda ya fi ƙarfin doka, kuma duk wani yunƙurin kare masu hannu a ta’addanci yana raunana tsaro tare da cin zarafin mutanen Arewa da Najeriya baki ɗaya.

Saboda haka, ina kira da a gaggauta kafa bincike mai zaman kansa, marar son zuciya, wanda Majalisar Ƙasa, hukumomin tsaro, da Ofishin Babban Lauyan Ƙasa za su jagoranta, domin binciken kuɗaɗe, kayan aiki, sadarwa da duk wata hulɗa da ka iya taimaka wa ’yan bindiga.

Dole ne a kare masu fallasa gaskiya, kuma duk jami’in gwamnati da aka samu da laifi ya fuskanci hukunci ba tare da la’akari da matsayinsa ko ƙarfin ikonsa ba.

Arewa ta sha wahala ƙwarai sakamakon ’yan bindiga. Wannan lokaci ne na fuskantar gaskiya, ba na ɓoyewa ba. Lokacin shiru ya wuce. Lokacin gaskiya, adalci da ɗaukar mataki ya yi.

Ɗan'uwanku
Comr. Haidar H. Hasheem
Ɗan Arewa Mai Kishin Tsaro Da Tabbatar Da Adalci

Dole A Gaggauta Binciken Ƙaramin Ministan Tsaro Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga ~ Cewar CNG..... Gamayyar Kungiyoyin Are...
14/12/2025

Dole A Gaggauta Binciken Ƙaramin Ministan Tsaro Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga ~ Cewar CNG
..... Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Buƙaci A Gaggauta Bincike Mai Zurfi Kan Zargin Da Ake Yiwa Matawalle Da Alaƙa Da Yan Bindiga

Ƙungiyar Coalition of Northern Groups (CNG) ta bayyana damuwa mai tsanani kan ikirarin da Musa Kamarawa, tsohon mataimaki na musamman ga tsohon Gwamnan Zamfara kuma Ministan Tsaron Ƙasa na yanzu, Bello Matawalle, ya yi a wani faifan bidiyon da yake nuna Matawallen na da alaƙa da tallafawa yan bindiga.

CNG ta ce zargin ya shafi tura kuɗi kai tsaye ga fitaccen shugaban ‘yan bindiga Bello Turji, sayen motocin Hilux da dama ga ƙungiyoyin ta’addanci, da kuma bayar da tallafin kayan aiki kamar gidaje, shanu da sauran dukiya, wanda ake zargin ‘yan siyasa daga Zamfara da maƙwabtanta s**a taimaka wajen aiwatarwa.

A cewar CNG, waɗannan ikirari suna nuna yiwuwar alaƙa mai zurfi tsakanin wasu manyan jami’an gwamnati da ‘yan bindiga, lamarin da ka iya rusa ƙoƙarin sojoji tare da ƙara jefa al’umma cikin haɗari.

Ƙungiyar ta ce irin waɗannan zarge-zarge ba za a iya watsi da su ta hanyar musantawa kawai ba, domin hakan na ƙara haifar da shakku cewa ana ɓoye gaskiya.

CNG ta kuma soki matakin Ministan na kai ƙara kan Sheikh Murtala Asada, tana mai cewa hakan na iya zama yunƙurin hana faɗin gaskiya, maimakon kare mutunci. Ta bukaci Sheikh Asada da ya fito da dukkan hujjojin da ke hannunsa ba tare da tsoro ba.

Ƙungiyar ta jaddada cewa babu wanda ya isa ya fi karfin doka, kuma ɓoye masu hannu a ta’addanci na raunana tsaro da amincewar jama’a.

Saboda haka, CNG ta nemi bincike mai zaman kansa, binciken da babu son zuciya, wanda Majalisar Ƙasa, hukumomin tsaro da Ofishin Babban Lauyan Ƙasa za su jagoranta, domin binciken kuɗaɗe, kayan aiki, sadarwa da duk wata shawara da ka iya taimaka wa ‘yan bindiga.

Ta ce dole a kare masu fallasa gaskiya, kuma duk jami’in gwamnati da aka samu da laifi ya fuskanci hukunci ba tare da la’akari da matsayinsa ko ƙarfin ikonsa ba.

CNG ta jaddada cewa Arewa ta sha wahala matuƙa sakamakon ‘yan bindiga, kuma wannan lokaci wata dama ce ta fuskantar tushen matsalar. Kare masu aikata laifi zai lalata makomar tsaro da amincewar jama’a. Lokacin ɓoyewa ya wuce, lokacin gaskiya da adalci ya yi.

Sa Hannun
Comr Jamilu Aliyu Charanchi
National Coordinator CNG

OPA Ta Soki Naɗin Amupitan a Matsayin Shugaban INEC, Ta Ce Cancantarsa Ba Ta Kai Ya Riƙe Hukumar Zaɓe BaOdua People’s As...
28/11/2025

OPA Ta Soki Naɗin Amupitan a Matsayin Shugaban INEC, Ta Ce Cancantarsa Ba Ta Kai Ya Riƙe Hukumar Zaɓe Ba

Odua People’s Assembly (OPA) ta fito fili ta bayyana rashin gamsuwarta da nadin Joash Ojo Amupitan, SAN, a matsayin sabon Shugaban INEC, tana cewa wannan nadin na iya zama barazana ga sahihancin zaɓe da kwanciyar hankali na demokradiyya a Najeriya.

A cikin sanarwar da Richard Olatunji Kayode ya fitar, OPA ta ce kasar tana fuskantar mawuyacin hali na rashin amincewa da sakamakon zaɓe, don haka wajibi ne INEC ta samu shugaba mai gaskiya, kwarjini da cikakken tarihin tsayuwa kan adalci wanda duka wannan halayen Amupitan bai cika su ba.

Kungiyar ta goyi bayan ƙungiyar kwararrun lauyoyi sama da 1,000 (ALDRAP), wadda ta riga ta yi tir da nadin, tana cewa akwai bayanan da ke nuna alakar siyasa tsakanin Amupitan da Ministan Abuja, Nyesom Wike, wasu majiyoyin ma na zargin yaron Wike ne, alakar da OPA ta ce na iya haifar da shakku game da ikon Amupitan na yin aikin da bai dace ba.

OPA ta yi gargadin cewa duk wani shugaban INEC da ke da inuwa ko kusanci da manyan ‘yan siyasa ba zai iya gina sahihin tsarin zaɓe ba. Ta ce idan aka yi watsi da waɗannan korafe-korafe, za a iya sake fadawa cikin rikici, rashin tabbas da asarar amincewar jama’a ga INEC.

Ta bukaci Majalisar Dattawa da ta yi amfani da mukamin amincewa cikin gaskiya, ba tare da siyasa ta shige ciki ba, domin kare demokradiyyar Najeriya.

A ƙarshe, OPA ta kira kungiyoyin farar hula, matasa, lauyoyi da ‘yan jarida su kasance masu sa ido, su kare muradun kasa, domin a samar da INEC da za ta yi aiki bisa gaskiya, ba tare da fargaba ko tsoron siyasa ba.

NDYC Ta Caccaki Wike da INEC Kan Yunkurin Rusa Dimokuraɗiyyar NajeriyaƘungiyar Niger Delta Youth Congress (NDYC) ta yi t...
25/11/2025

NDYC Ta Caccaki Wike da INEC Kan Yunkurin Rusa Dimokuraɗiyyar Najeriya

Ƙungiyar Niger Delta Youth Congress (NDYC) ta yi taron ’yan jarida domin bayyana damuwa kan yadda Ministan FCT, Nyesom Wike, da kuma yadda INEC ke nuna rashin adalaci game da sakamakon gangamin PDP na Ibadan ke zama babbar barazana ga dimokuraɗiyyar Najeriya.

NDYC ta zargi Wike da amfani da muƙaminsa wajen tsoma baki cikin jam’iyya, tayar da rikici, tsoratarwa da kokarin tilasta ra’ayinsa, abin da ke yi wa tsarin dimokuraɗiyya mummunar illa. Ta ce halayensa na nuna girman kai, raina doka da neman iko su na iya tarwatsa ƙasa.

Kungiyar ta roki Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gargaɗi Wike, ya tunasar da shi cewa shi bawa ne na jama’a, ba sarki ba.

A bangaren INEC kuwa, NDYC ta nuna damuwa kan yadda take jan kafa wajen tabbatar da zababben shugaban PDP Kabiru Turaki, tana nuna fifiko ga Damagum. Ta ce wannan ya tauye adalci, ya kuma lalata amincewar jama’a da hukumar zabe.

NDYC ta jaddada cewa sakamakon taron Ibadan halastacce ne, kuma INEC dole ta tsaya kan doka ba tare da shiga hannun masu son murde sakamakon siyasa ba don biyan buƙatar Wike.

Ta kuma bayyana cewa halayen Wike ba sa wakiltar mutanen Niger Delta gaba ɗaya.

A ƙarshe, NDYC ta ce za ta ci gaba da kare dimokuraɗiyya da doka, domin Najeriya ta fi kowane mutum girma, kuma duk wanda ya yi barazana ga tsarin mulki dole a tsawatar masa.

Da hannun
Comr. Israel Uwejeyan, National Coordinator, NDYC

22/11/2025

INEC's Shameful Bias

It’s now clear that INEC under this new chairman has abandoned neutrality and is gradually turning into Wike’s personal agency. The same INEC that spoke with confidence on Arise News on November 11 is now contradicting itself just to please Wike.

This sudden turnaround shows dangerous bias, a deliberate attempt to weaken the PDP and serve selfish political interests. A national institution should not dance to the tune of one politician, yet this INEC chairman seems ready to destroy credibility at all cost.

Tsayuwar Daka a Ibadan: Yadda Kauran Bauchi, Dauda Lawal da Makinde S**a Ceto Mutuncin Jam'iyyar PDPA babban taron da ja...
21/11/2025

Tsayuwar Daka a Ibadan: Yadda Kauran Bauchi, Dauda Lawal da Makinde S**a Ceto Mutuncin Jam'iyyar PDP

A babban taron da jam’iyyar PDP ta gudanar a Ibadan ranar Asabar da ta gabata, an ga wani sabon salo na shugabanci da jajircewa wanda ya tabbatarwa ‘yan Najeriya cewa PDP har yanzu tana da waɗanda za su tsaya tsayin daka domin kare darajarta.

A cikin waɗanda s**a fito fili wajen nuna wannan kwazo, akwai Kauran Bauchi, wanda ya jagoranci aikin gyara da tsaftace jam’iyya da tsantseni. Tsayuwarsa wajen korar masu tada zaune tsaye a ciki, musamman waɗanda ke aiki da boyayyun manufa don rusa jam’iyyar daga cikin gida, ya zama abin yabo da koyi. A gaskiya, Kauran Bauchi ya zama ginshiƙin da ya hana jam’iyyar durkushewa.

Baya ga haka, Gwamnan Zamfara Dr. Dauda Lawal ya nuna irin kishinsa ga dimokuraɗiyya. Goyon bayansa ga sahihin tsari da adalci a cikin jam’iyya ya karfafa gwiwar mambobi da magoya baya, ya tabbatar masu cewa PDP na da shugabanni da ba za su lamunci karya ko shisshigi ba.

A bangaren Seyi Makinde, Gwamnan jihar Oyo, ya ba da cikakken gudunmawa wajen tabbatar da cewa taron Ibadan ya kasance sahihi, kuma cikin tsarin da ya dace. Makinde ya tabbatar da cewa jam’iyya ta gudana bisa ka’ida, ba tare da batan batu ko rikice-rikice ba, aikin da ya kara tabbatar da cewa PDP jam’iyyar da take da ni’imar shugabanni masu hangen nesa.

A tare, waɗannan manyan shugabanni uku sun yi abin da ake kira ceto martabar PDP, tare da dawo da yarda da kwarin gwiwar jama’a. Sun nuna cewa jam’iyyar adawa ba ta mutu ba, kuma ba za ta mutu ba, muddin akwai shugabanni irin su Kauran Bauchi, Dr. Dauda Lawal da Seyi Makinde.

A Ibadan, PDP ta sake tsayawa kan kafafunta kuma hakan ya sake busawa dimokuraɗiyya a rai.

INEC Tayi Watsi Da Buƙatar Masu Yiwa PDP Zagon Kasa, Ta Tabbatar Da Damagun a Matsayin Shugaban Jam'iyyar  PDP Daga Jimo...
19/11/2025

INEC Tayi Watsi Da Buƙatar Masu Yiwa PDP Zagon Kasa, Ta Tabbatar Da Damagun a Matsayin Shugaban Jam'iyyar PDP

Daga Jimoh Isma'il Adetunji

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta tabbatar da cewa Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na jam’iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya na ƙasa Kabiru Tanimu Turaki (SAN) ita ce hukuma ɗaya tilo da ta dace a doka.

INEC ta ƙi yarda da takardar bogi da wasu korarru Mohammed Abdulrahman da Samuel Anyanwu s**a aika suna kiran a dage zaben fidda gwani na gwamnan Jihar Ekiti, matakin da ya fallasa yunƙurinsu na rugujewa jam’iyyar adawa ta ƙasa ta hanyar karya doka da son zuciya.

INEC ta jaddada cewa wannan takardar da waɗannan haramtattun shugabanni s**a turo a ranar 6 ga Nuwamba, 2025, ba ta da wani inganci. Su kansu sun yi ikirarin shugabanci ne bisa ƙarya, inda s**a jingina dalilan karya na wai “matsalolin shirye-shirye” domin su kawo tangarda ga zaɓen ranar 8 ga Nuwamba.

Hukumar ta bayyana a fili cewa kawai sa hannun shugaban jam’iyya na ƙasa da sakataren ƙasa na halastattaccen NWC ne ake karɓa a hukumance.

Matakin INEC ya yi daidai da hukuncin da jam’iyyar PDP ta yanke tun farko na dakatar da Anyanwu, Abdulrahman da wasu abokan aikinsu a ranar 1 ga Nuwamba, 2025 saboda aikata laifukan karya tsarin jam’iyya, wanda ya sabawa sassan 57(3), 58(1)(a)(b)(c)(h), da 59(1) na kundin tsarin PDP (2017 da aka gyara).

Wadannan hukunci an tabbatar da su ne a babban taron jam’iyyar da aka yi a Ibadan a ranar 15 ga Nuwamba, 2025, inda aka zaɓi Barrister Tanimu Turaki a matsayin sabon shugaban jam’iyya na ƙasa, tare da tsige manyan masu tada fitina ciki har da Anyanwu, Abdulrahman, Nyesom Wike da Ayo Fayose saboda aikata manyan laifuka na tafka ayyukan adawa da jam’iyyar, ƙirƙiro bangarori, da amfani da kotu wajen rugujewa jam’iyya.

DA DUMI-DUMI: Jam'iyyar APC ta jihar Zamfara karkashin ministan tsaro Dr Bello Matawalle da Sanata Abdul'aziz Yari, sun ...
14/11/2025

DA DUMI-DUMI: Jam'iyyar APC ta jihar Zamfara karkashin ministan tsaro Dr Bello Matawalle da Sanata Abdul'aziz Yari, sun goyi bayan tazarcen shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027, inda dubunnan yayan jam'iyyar s**a yi cikar kwari a wurin taron da Dr Bello Matawalle ya jagoranta yau Jumma'a a jihar Zamfara.

Daga Al'Mansoor Gusau

Wike Na Kawo Barazana Ga Demokradiyyar Najeriya – Ƙungiyar Nigeria Unite Ta Gargadi EUƘungiyar Nigeria Unite ta aika wa ...
14/11/2025

Wike Na Kawo Barazana Ga Demokradiyyar Najeriya – Ƙungiyar Nigeria Unite Ta Gargadi EU

Ƙungiyar Nigeria Unite ta aika wa ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) da wasika mai zafi, tana zargin Ministan Abuja, Nyesom Wike, da haifar da barazana ga dimokiraɗiyar Najeriya ta hanyar murkushe ‘yan adawa da goyon bayan shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu domin tabbatar da wa’adi na biyu ba tare da hamayya ba.

Ƙungiyar ta ce bayan rugujewar dimokiraɗiya a Mali, Burkina Faso da Nijar, yanzu haka Najeriya ma na kan layin tangal-tangal, saboda irin matakan zaluntar ‘yan adawa da kuma amfani da cin hanci wajen tilasta sauya sheƙa.

Ta gargadi cewar idan ba a dauki mataki ba, lamarin zai iya jefa Najeriya cikin rikici, ya kawo bacewar tsaro a yankin Sahel, tare da tura miliyoyin ‘yan Najeriya zuwa Turai da Amurka a matsayin ‘yan gudun hijira.

Nigeria Unite ta kuma bukaci EU, AU, Amurka da Birtaniya su sanya takunkumi kan Wike da dakatar da shi daga tafiye-tafiye, tare da daukar mataki kan wasu manyan alkalan ƙasar, kwamishinan ‘yan sanda Abuja da hukumar INEC, domin cewar suna sabawa dokokin siyasa da na aikinsu.

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa For Asiwaju posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa For Asiwaju:

Share