Jarida Radio

Jarida Radio Kafa Mai Inganci Za a Iya Sauraron Jarida Radio Kai Tsaye Ta www.jaridaradio.com Cikin Sa'o'i 24 a Kowacce Rana.

Sojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Yi Garkuwa da Su, Sun Kwato Dabbobi 281 da ’Yan Bindiga S**a Sace a SakkwatoDaga Aliyu ...
05/08/2026

Sojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Yi Garkuwa da Su, Sun Kwato Dabbobi 281 da ’Yan Bindiga S**a Sace a Sakkwato

Daga Aliyu Samba

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya ta 8 Division Garrison sun ceto mutum 14 da aka yi garkuwa da su tare da kwato dabbobi 281 da wasu ’yan bindiga s**a sace bayan sun kai hari ƙauyen Horo Birni da ke Ƙaramar Hukumar Shagari a Jihar Sakkwato.

Wata majiya mai tushe a rundunar sojin ta shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) cewa lamarin ya faru ne a ranar Talata, inda dakarun s**a gaggauta kai ɗauki bayan samun kiran neman agaji daga mazauna yankin.

Majiyar ta ce da isar sojojin, sun yi arangama da ’yan bindigar da ke tafiya da mutanen da s**a yi garkuwa da su tare da dabbobin da s**a sace daga ƙauyen.

Ta bayyana cewa sojojin sun yi wa ’yan bindigar ruwan wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa cikin ruɗani bayan sun samu raunukan harbin bindiga, s**a bar mutanen da s**a sace da kuma dabbobin.

A cewar majiyar, sojojin sun yi nasarar ceto mutane 14 tare da kwato shanu 195, tumaki 84, rakuma biyu da kuma babura biyu.

Ta ƙara da cewa gaggawar da sojojin s**a yi wajen kai ɗauki ta taimaka wajen ceton rayuka da dukiyoyin al’umma, tana mai yabawa haɗin gwiwar jami’an tsaro da ya taimaka wajen nasarar aikin.

Majiyar ta jaddada cewa dakarun sojin na ci gaba da kasancewa cikin shiri domin yaƙi da duk wani nau’in ta’addanci da laifuffuka, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro cikakken haɗin kai da kuma kai rahoton duk wani abin da ba su yarda da shi ba.

Tinubu Ya Amince da Ƙarin Albashi Har Kashi 80 Ga Jami’an Sojin NajeriyaDaga Aliyu SambaShugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu...
04/08/2026

Tinubu Ya Amince da Ƙarin Albashi Har Kashi 80 Ga Jami’an Sojin Najeriya

Daga Aliyu Samba

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da ƙarin albashi ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya da ya kai tsakanin kashi 30 zuwa 80 cikin ɗari, a wani mataki da gwamnatin tarayya ta ce na inganta jin daɗin jami’an tsaro da ƙarfafa musu gwiwa wajen gudanar da ayyukansu.

Sanarwar da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Talata ta bayyana cewa kimanin jami’ai da sojoji 250,000 ne za su amfana da sabon tsarin albashin, wanda zai fara aiki daga 1 ga Satumban 2026.

A cewar sanarwar, jami’an da ke daga mukamin Brigadier Janar zuwa Janar za su samu ƙarin albashi na kashi 30 cikin ɗari, yayin da jami’an daga mukamin Kanal zuwa Warrant Officer za su samu ƙarin kashi 50 cikin ɗari. Haka kuma, sojojin da ke daga mukamin Private zuwa Staff Sergeant za su amfana da ƙarin albashi mafi girma na kashi 80 cikin ɗari.

Sanarwar ta ƙara da cewa sabon tsarin zai ƙara yawan kuɗin da gwamnati ke kashewa kan albashin jami’an sojin daga Naira biliyan 660 zuwa Naira biliyan 924 a duk shekara.

Shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa na yaba wa jajircewa da sadaukarwar jami’an rundunar sojin wajen yaƙi da matsalolin tsaro da s**a haɗa da ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma ayyukan ‘yan bindiga a wasu sassan ƙasar.

Ya ce, “Mazan da matan da ke tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyinmu sun cancanci a tallafa musu tare da nuna musu godiya saboda hidimar da suke yi wa ƙasa. Gwamnatinmu za ta ci gaba da ba da fifiko ga jin daɗin jami’an tsaro tare da samar musu da mak**ai da fasahohin zamani domin su gudanar da aikinsu yadda ya k**ata.”

Shugaban ya kuma jaddada cewa babu wata ƙasa da za ta iya samun ci gaba mai ɗorewa ba tare da ingantaccen tsaro ba, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen amfani da dukkan rundunonin tsaro domin kawar da barazanar tsaro da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Najeriya.

Tinubu ya kuma yi kira ga jami’an rundunar sojin da su ɗauki wannan ƙarin albashi a matsayin wata alamar godiya daga gwamnati bisa irin hidimar da suke yi wa ƙasa, yana mai bayyana ƙwarin gwiwar cewa Najeriya za ta yi nasara kan masu neman tada zaune tsaye da tarwatsa zaman lafiyar ƙasar.

Dakarun Operation HADIN KAI Sun Cafke Mutane Biyar da Ake Zargi da Garkuwa da Mutane a YobeDakarun rundunar Operation HA...
24/07/2026

Dakarun Operation HADIN KAI Sun Cafke Mutane Biyar da Ake Zargi da Garkuwa da Mutane a Yobe

Dakarun rundunar Operation HADIN KAI tare da haɗin gwiwar ƙungiyar mafarauta ta Jihar Yobe sun k**a wasu mutane biyar da ake zargi da hannu a ayyukan garkuwa da mutane a ƙauyen Jegalari da ke ƙaramar hukumar Fune ta jihar.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Juma’a, ta ce jami’an Bataliya ta 233 da ke sansanin soji na Damaturu ne s**a gudanar da samamen bayan samun sahihan bayanan sirri kan ayyukan waɗanda ake zargin.

Sanarwar ta ce a yayin samamen, an ƙwato bindigogi uku ƙirar AK-47 da aka ƙera a gida, bindiga guda ta gida, harsasai iri-iri da kuma wayoyin hannu huɗu da ake zargin suna da alaƙa da ayyukan laifin.

Rundunar ta ce ana ci gaba da tsare waɗanda ake zargin tare da kayayyakin da aka ƙwato domin gudanar da bincike da tantance rawar da s**a taka a laifukan garkuwa da mutane da sauran ayyukan ta’addanci.

Operation HADIN KAI ta jaddada cewa za ta ci gaba da gudanar da hare-haren da s**a dogara da bayanan sirri domin hana ‘yan ta’adda da sauran masu aikata laifuka samun damar gudanar da ayyukansu a yankin Arewa maso Gabas.

Har ila yau, rundunar ta buƙaci al’umma su kasance masu sa ido tare da kai rahoton duk wani motsi ko mutum da ake zargi ga jami’an tsaro mafi kusa, tana mai cewa haɗin kan jama’a da bayar da sahihan bayanai na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron al’umma.

22/07/2026

Wani matashi mai alwala yayin da yake tukin keke da baya.
A ganinku dan wane gari ne 😂

21/07/2026

Tsawon shekaru biyar, s**a rika aikin sojan gona a yankin Kafanchan na Jihar Kaduna har sai da Rundunar Sojin Najeriya ta k**a su. ゚

Kotu Ta Tabbatar da David Mark da Aregbesola a Matsayin Shugabannin Jam’iyyar ADCBabbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi ...
02/07/2026

Kotu Ta Tabbatar da David Mark da Aregbesola a Matsayin Shugabannin Jam’iyyar ADC

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi watsi da ƙarar da aka shigar domin ƙalubalantar shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), inda ta tabbatar da sahihancin shugabancin tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, a matsayin Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa, da kuma Rauf Aregbesola a matsayin Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa.

Mai shari’a Musa Liman, ya bayyana cewa kotun ba ta da hurumin shiga cikin harkokin cikin gida na jam’iyya, lamarin da ya sa ya yi watsi da ƙarar baki ɗaya.

Kotun ta kuma umarci mai ƙarar, Leke Abejide, tare da lauyansa, da su biya kuɗaɗen shari’a bayan da ta tabbatar da cewa zaɓen shugabancin da David Mark ke jagoranta ya gudana ne bisa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin jam’iyyar ADC da kuma dokar zaɓe ta ƙasa.

Wannan hukunci ya ƙara ƙarfafa matsayin shugabannin jam’iyyar bayan wasu nasarorin shari’a da ADC ta samu a baya-bayan nan. A baya, Kotun Ƙoli ta sake tabbatar da shugabancin David Mark, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta dakatar da aiwatar da wani hukuncin ƙaramar kotu da ke neman soke rajistar jam’iyyar.

Masu sa ido kan harkokin siyasa na ganin cewa wannan hukunci zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da daidaito a cikin jam’iyyar, musamman a daidai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen tunkarar zaɓuɓɓukan siyasa masu zuwa a ƙasar nan.

Shugaban ƙasar Faransa Macron ya gana da Sarkin Oman Haitham bin Tariq Al Said a birnin Paris. Wannan ziyara na zuwa.  e...
29/06/2026

Shugaban ƙasar Faransa Macron ya gana da Sarkin Oman Haitham bin Tariq Al Said a birnin Paris. Wannan ziyara na zuwa. e bayan Amurka ta sake kaddamar da hare-hare a mashigin ruwa na Hormuz wanda ke makwabtaka da kasar Omar.

12/06/2026

Daruruwan masu zanga-zanga sun fito kan titunan Legas da Abuja a ranar Juma'a 12 ga watan Yuni, ranar Dimokuradiyya ta Najeriya, suna buƙatar gwamnati ta ɗauki mataki kan yawaitar garkuwa da mutane, tare da kiran Shugaba Tinubu da ya yi murabus.

Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Kan Ebola, Ya Amince da Naira Biliyan 10 Don Shirin Bada KariyaShugaban Bola Ahm...
09/06/2026

Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Kan Ebola, Ya Amince da Naira Biliyan 10 Don Shirin Bada Kariya

Shugaban Bola Ahmed Tinubu, ya amince da kafa Kwamitin Musamman na Fadar Shugaban Ƙasa kan Shirin Kariya daga Cutar Ebola da Sauran Barazanar Lafiyar Jama’a, tare da bayar da umarnin sakin naira biliyan 10 domin shirye-shiryen gaggawa.

A cewar sanarwar da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata, kuɗaɗen za su taimaka wajen ƙarfafa shirye-shiryen Hukumar Yaƙi da Cututtuka Masu Yaɗuwa ta Ƙasa (NCDC) da kuma ayyukan da s**a shafi tunkarar duk wata barazanar gaggawa ga lafiyar al’umma.

Shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, ne zai jagoranci sabon kwamitin, wanda zai haɗa da wakilai daga ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati daban-daban, da kuma wakilan jihohi.

Matakin ya biyo bayan sake bullar cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC) da kuma Uganda.

Shugaba Tinubu ya amince da kafa kwamitin ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa ya jagoranta domin nazarin irin shirin da Najeriya ta yi da kuma dabarun da za su hana cutar shiga ƙasar.

Daga cikin mahalarta taron akwai wakilai daga Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Hukumar Filayen Jiragen Sama ta Ƙasa (FAAN), Hukumar Shige da Fice (NIS), Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama (NCAA), da gwamnatin jihar Legas.

Shugaban ƙasar ya kuma umarci dukkan jihohin da ke da filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa da kuma manyan hanyoyin shiga ƙasar daga ƙasashen waje da su gabatar da tsare-tsarensu, buƙatun kuɗi da irin tallafin da suke buƙata domin aiwatar da matakan kariya cikin haɗin gwiwa.

A cikin matakan da aka sanar za a ɗauka akwai ƙara tsaurara binciken fasinjoji a dukkan filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa, ciki har da duba zafin jiki da tsara yadda jama’a ke shiga da fita.

Haka kuma za a ƙarfafa sa ido kan fasinjojin da ke shigowa ta wasu hanyoyin jiragen sama da gwamnati ta ayyana a matsayin masu haɗari, ciki har da Air Uganda, RwandAir, Air Tanzania, Air Angola, Kenya Airways da Ethiopian Airlines.

Gwamnatin ta ce za a gaggauta bude cibiyoyin killace marasa lafiya da wuraren tura waɗanda ake zargin sun kamu da cutar a filayen jiragen saman Legas da Abuja, kafin daga baya a faɗaɗa tsarin zuwa sauran filayen jiragen saman ƙasar.

Sauran matakan sun haɗa da wajabta cike bayanan lafiyar matafiya ta hanyar tsarin QR Code kafin su iso ƙasar idan sun fito ko s**a bi ta ƙasashen da aka ayyana masu haɗari, da kuma tsaftace dakunan tashi da saukar jirage, wuraren kaya da sauran sassan filayen jiragen sama.

Shugaba Tinubu ya kuma umarci kwamitin da ya tattauna da hukumomin tsaro, diflomasiyya da sufurin jiragen sama kan yiwuwar ɗaukar ƙarin matakan da s**a shafi zirga-zirgar jirage daga ƙasashen da cutar ta bulla ko waɗanda aka sanya cikin jerin masu haɗari.

Bugu da ƙari, kwamitin zai duba yiwuwar ware wasu filayen jiragen sama ko tashoshi na musamman domin karɓar jiragen da ake ganin suna da haɗari, tare da nazarin sauya lokutan saukar wasu jirage domin rage haɗuwar fasinjojin da ake sa ran za su buƙaci ƙarin bincike da sauran matafiya.

Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Hare-Haren Da Take Kai Wa Isra’ilaRundunar sojin Iran ta sanar da dakatar da hare-haren da t...
08/06/2026

Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Hare-Haren Da Take Kai Wa Isra’ila

Rundunar sojin Iran ta sanar da dakatar da hare-haren da take kai wa Isra’ila bayan abin da ta bayyana a matsayin martani mai radadi kan hare-haren da Isra’ila ta kai a kasar Lebanon.

Sanarwar ta fito ne a ranar Litinin ta cikin wata sanarwa da aka karanta a gidan rediyon kasar.

Matakin ya zo ne bayan Iran da Isra’ila sun yi musayar hare-hare cikin daren Lahadi zuwa safiyar Litinin, lamarin da ake ganin shi ne mafi muni tun bayan yarjejeniyar tsagaita wuta da ta kawo karshen yakin da Amurka da Isra’ila s**a yi da Iran a watan Afrilu.

Iran ta harba mak**ai masu linzami zuwa Isra’ila a daren Lahadi, inda ta ce hakan martani ne ga hare-haren da Isra’ila ta kai a babban birnin Lebanon, wato Beirut.

A martaninta, Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan wasu wurare a fadin Iran da sanyin safiyar Litinin, yayin da hare-haren Iran kan Isra’ila s**a ci gaba.

Wannan sabon tashin hankalin ya jefa kokarin da Shugaban Amurka, Donald Trump, ke yi na kawo karshen rikicin cikin mawuyacin hali.

A ranar Litinin, Trump ya bukaci bangarorin biyu da su dakatar da bude wuta nan take, bayan rahotanni sun nuna cewa ya roki Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, da kada ya mayar da martani kan hare-haren da Iran ta kai.

Sai dai bayan wasu sa’o’i kadan, shugabannin sojojin Iran s**a sanar da kawo karshen farmakin.

A cikin sanarwar, Iran ta ce ta riga ta bayar da “martani mai radadi” ga Isra’ila domin nuna goyon baya ga Lebanon.

“Bisa wannan dalili, ana sanar da dakatar da ayyukan sojojin kasar,” in ji sanarwar.

Jarida Radio ta rawaito cewa wannan mataki na Iran ya zo ne a daidai lokacin da kasashen duniya ke ci gaba da kira ga bangarorin biyu da su kauce wa daukar matakan da za su iya kara rura wutar rikici a yankin Gabas ta Tsakiya.

Address

2 Morija Close Wuse II
Abuja
900110

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jarida Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jarida Radio:

Shortcuts

Share