05/08/2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Yi Garkuwa da Su, Sun Kwato Dabbobi 281 da ’Yan Bindiga S**a Sace a Sakkwato
Daga Aliyu Samba
Dakarun Rundunar Sojin Najeriya ta 8 Division Garrison sun ceto mutum 14 da aka yi garkuwa da su tare da kwato dabbobi 281 da wasu ’yan bindiga s**a sace bayan sun kai hari ƙauyen Horo Birni da ke Ƙaramar Hukumar Shagari a Jihar Sakkwato.
Wata majiya mai tushe a rundunar sojin ta shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) cewa lamarin ya faru ne a ranar Talata, inda dakarun s**a gaggauta kai ɗauki bayan samun kiran neman agaji daga mazauna yankin.
Majiyar ta ce da isar sojojin, sun yi arangama da ’yan bindigar da ke tafiya da mutanen da s**a yi garkuwa da su tare da dabbobin da s**a sace daga ƙauyen.
Ta bayyana cewa sojojin sun yi wa ’yan bindigar ruwan wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa cikin ruɗani bayan sun samu raunukan harbin bindiga, s**a bar mutanen da s**a sace da kuma dabbobin.
A cewar majiyar, sojojin sun yi nasarar ceto mutane 14 tare da kwato shanu 195, tumaki 84, rakuma biyu da kuma babura biyu.
Ta ƙara da cewa gaggawar da sojojin s**a yi wajen kai ɗauki ta taimaka wajen ceton rayuka da dukiyoyin al’umma, tana mai yabawa haɗin gwiwar jami’an tsaro da ya taimaka wajen nasarar aikin.
Majiyar ta jaddada cewa dakarun sojin na ci gaba da kasancewa cikin shiri domin yaƙi da duk wani nau’in ta’addanci da laifuffuka, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro cikakken haɗin kai da kuma kai rahoton duk wani abin da ba su yarda da shi ba.