Jarida Radio

Jarida Radio Kafa Mai Inganci Za a Iya Sauraron Jarida Radio Kai Tsaye Ta www.jaridaradio.com Cikin Sa'o'i 24 a Kowacce Rana.

Dubban ‘yan Isra’ila ne s**a gudanar da zanga-zanga jiya Asabar a birnin Tel Aviv, inda s**a bukaci a dawo da mutanen da...
06/07/2025

Dubban ‘yan Isra’ila ne s**a gudanar da zanga-zanga jiya Asabar a birnin Tel Aviv, inda s**a bukaci a dawo da mutanen da aka yi garkuwa da su daga zirin Gaza a wani bangare na “cikakkiyar yarjejeniya” da Hamas.

Jaridar Yedioth Ahronoth ta bayar da rahoton cewa, masu zanga-zangar sun yi kira da a cimma yarjejeniya da za ta kai ga sako duk wadanda ake tsare da su a Gaza, a raye ko a mace.

'Yan uwa da dama kuma sun ba da jawabai, inda s**a bukaci matsin lamba ga gwamnatin Benjamin Netanyahu da ta gaggauta kammala yarjejeniyar ba tare da bata lokaci ba.

'Yan uwa da dama na wadanda aka yi garkuwa da su ne s**a halarci zanga-zangar, suna rera taken kin amincewa da duk wata yarjejeniya da za ta iya takaita sakin mutane kadan, a cewar jaridar.

Shahararren mai tsaron ragar Najeriya, Peter Rufa'i, ya rasu yana da shekaru 61 a duniya. 'Yan Najeriya sun yi jimamin m...
06/07/2025

Shahararren mai tsaron ragar Najeriya, Peter Rufa'i, ya rasu yana da shekaru 61 a duniya. 'Yan Najeriya sun yi jimamin mutuwar wannan gwarzon ne a ranar Alhamis bayan fama da wata cuta da ba a bayyana ba.

Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF) ta bayyana Peter Rufa'i a matsayin jigo a fagen kwallon kafa, la'akari da gudumawar da ya bai wa kungiyar.

Rubuta mana abun da ka sani game da Peter Rufai

An kafa kungiyar BRICS ne a shekarar 2009 da Brazil da Rasha da Indiya da kuma China s**a kafa, bayan shekara daya Afrik...
06/07/2025

An kafa kungiyar BRICS ne a shekarar 2009 da Brazil da Rasha da Indiya da kuma China s**a kafa, bayan shekara daya Afrika ta Kudu ta shiga.

Shugabanni da wakilai daga kawancen kasashen BRICS za su halarci taron koli karo na 17 na kungiyar a

30/06/2025

Bidiyo: Harin Isra'ila ya kashe mutum 15 a yankin Jabalia da ke Gaza 😭

A sanyin safiyar ranar Lahadi 29 ga Yuni Isra'ila ta kai wannan hari da ya kashe akalla mutane 15, jim kadan bayan da sojojinta sun ba da umarnin Falasdinawa su bar yankin na Jabalia da ke birnin Gaza.

Me za ku ce game da wannan?

28/06/2025

An umurci sojojin Isra'ila da su harbi Falasdinawa fararen hula da ke fama da yunwa a wuraren karbar kayan agaji a Gaza, kamar yadda wani bincike da jaridar Haaretz ta gudanar ya nuna.

Zuwa yanzu an kashe mutum 549 tun daga ranar 27 ga watan Mayu.

Allah ya tabbatar da kasar Falasdinu 'Amin'

Jarida Radio 28 ga Yuni, 2025

28/06/2025

Da Dumi-Dumi: Donald Trump ya ce ya yi imanin za a iya cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza a cikin mako mai zuwa.

Me zaku ce?

Jarida Radio 28 ga Yuni 2025



Sanata Barau Ya Bayyana Jimaminsa Bisa Rasuwar Dattijon Dan Kasuwa, Alhaji Aminu DantataMataimakin Shugaban Majalisar Da...
28/06/2025

Sanata Barau Ya Bayyana Jimaminsa Bisa Rasuwar Dattijon Dan Kasuwa, Alhaji Aminu Dantata

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Barau I. Jibrin, CFR, ya bayyana jimaminsa kan rasuwar tsohon dan kasuwa, dattijo, hazikin attajiri kuma babban mai taimakon al’umma, Alhaji Aminu Dantata, wanda ya rasu ranar Asabar yana da shekaru 94 a duniya.

A cikin wata sanarwa da mai bai wa Sanata Barau shawara kan harkokin yada labarai, Ismail Mudashir, ya fitar, Sanata Barau ya bayyana cewa marigayin ya taka gagarumar rawa wajen ci gaban Jihar Kano, Arewacin Najeriya da kuma kasa baki daya.

“Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Na yi matukar kaduwa da rasuwar mahaifinmu, dattijo kuma babban dan kasuwa mai taimakon al’umma, Alhaji Aminu Dantata, wanda ya rasu a ranar Asabar. Ya rayu cikin bautar Allah Madaukakin Sarki da kuma hidima ga al'umma.”

“Ina mika ta’aziyyata ga iyalan marigayin, ‘yan kasuwar jihar Kano, da daukacin al’ummar jihar Kano. Lallai mun yi rashin uba wanda gudunmawarsa wajen cigaban jihar mu da kasar nan gaba daya ba zai taba mantuwa ba.”

“Tsawon shekaru, ya kasance jigo a fannoni da dama na harkokin kasuwanci, cinikayya, gine-gine, kadarori, banki, masana’antu, da man fetur. Kwarewarsa a harkokin kasuwanci, ayyukan alheri da kuma kishin kasar sa za su ci gaba da zamo mana abin koyi. Alhaji Dantata ya kasance abin alfahari, abin koyi a rayuwa.” Inji Sanata Barau.

Sanata Barau ya kuma yi addu’ar Allah ya gafarta masa kurakuransa ya kuma karbi kyawawan ayyukansa.

“Allah ya jikan Alhaji Aminu Dantata ya kuma sanya shi cikin Aljannatul Firdausi. Allah ya ba iyalan sa da mu baki daya hakurin jure wannan babban rashi.”

26/06/2025

Jama'a rayuwa babu garanti, ya zama dole a matsayinka na matashi ka yi nazarin wannan karatun. Allah Ya sa mu dace 🤲

26 ga Yuni 2025

Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan a yau Alhamis ya yaba da kokarin shugaban Amurka Donald Trump na cimma yarj...
26/06/2025

Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan a yau Alhamis ya yaba da kokarin shugaban Amurka Donald Trump na cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Iran da Isra'ila.

Shugaban ya ce "Na shaida wa Trump cewa, dangane da kokarin da ya yi na tsagaita bude wuta tsakanin Isra'ila da Iran, ana sa ran irin wannan matakin zai taimaka wajen kawo karshen tashe-tashen hankula a Gaza da kuma yakin Rasha da Ukraine."

Erdogan ya bayyana haka ne ga manema labarai a hanyarsa ta dawowa daga taron kungiyar tsaro ta NATO a kasar Holland.

Jarida Radio 26 ga Yunin 2025

26/06/2025

Kasar Rasha da Mali sun sanya hannu kan yarjejeniyoyin karfafa huldar kasuwanci da tattalin arziki da hadin gwiwa a fannin makamashin nukiliya.

Me zaku ce kan wannan hhaddin gwiwa?

Hotuna: Fuskokin wasu yan ta'adda da jami'an tsaro s**a kashe yau Laraba a Jihar Zamfara, Karamar Hukumar Maru.Jarida Ra...
25/06/2025

Hotuna: Fuskokin wasu yan ta'adda da jami'an tsaro s**a kashe yau Laraba a Jihar Zamfara, Karamar Hukumar Maru.

Jarida Radio 25 ga Yuni 2025

Idan za a tuna a karshen watan Maris an yi wa wasu ’yan Kano mafarauta mummunan kisan gilla a garin Uromi na Jihar Edo y...
25/06/2025

Idan za a tuna a karshen watan Maris an yi wa wasu ’yan Kano mafarauta mummunan kisan gilla a garin Uromi na Jihar Edo yayin da suke kan hanyarsu ta komawa gida yin bikin karamar sallah.

https://jaridaradio.com/yadda-wasu-jihohi-ke-huce-haushin-fulani-kan-hausawa/

Latsa domin karanta cikakken makalar

Ba a gama fita daga cikin alhinin kisan gillar da aka yi wa wasu matafiya 12 ’yan Jihar Kaduna a Jih

Address

No. 2 Morijo Close Wuse II Abuja
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jarida Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jarida Radio:

Share