Jarida Radio

Jarida Radio Kafa Mai Inganci Za a Iya Sauraron Jarida Radio Kai Tsaye Ta www.jaridaradio.com Cikin Sa'o'i 24 a Kowacce Rana.

24/09/2025

Bidiyon ruftawar babban hanya sak**akon ginin hanyar karkashin kasa (subway) a birnin Bangkok na Thailand.

23/09/2025

Bidiyon yadda kasashe shida sun amince da kasar Falasdinu a hukumance a taron shugabannin kasa na Majalisar Dinkin Duniya karo na 80 a birnin New York, inda ake tattaunawa kan makomar Falasdinawa da kafa kasar Falasdinu.

Mene ne ra'ayinku?

Cc Abdul Journalist 1 fans Follower

A cikin wata daya an tara fiye da Naira biliyan 20 a Asusun Tallafin Ilimi na Matar Shugaban Kasa, Remi Tinubu.Mene ne r...
23/09/2025

A cikin wata daya an tara fiye da Naira biliyan 20 a Asusun Tallafin Ilimi na Matar Shugaban Kasa, Remi Tinubu.

Mene ne ra'ayinku?

Majalisar Wakilai a Nijeriya ta ce tana tare da shugaba Tinubu ɗari bisa ɗari wajen ciwo wa Nijeriya sabon bashi.Mene ne...
22/09/2025

Majalisar Wakilai a Nijeriya ta ce tana tare da shugaba Tinubu ɗari bisa ɗari wajen ciwo wa Nijeriya sabon bashi.

Mene ne ra'ayinku?

Hukumar NDLEA ta k**a wasu da s**a yi yunkurin safarar miyagun kwayoyi inda mutanen s**a yi kashin kulli 116 na hodar ib...
22/09/2025

Hukumar NDLEA ta k**a wasu da s**a yi yunkurin safarar miyagun kwayoyi inda mutanen s**a yi kashin kulli 116 na hodar iblis a filin jirgin Murtala Muhammed na Legas.

Mene ne ra'ayinklu kan wannnan?

Biritaniya da Kanada sun kasance kasashe na farko na G7 da s**a dauki matakin, inda ake sa ran Faransa da sauran kasashe...
22/09/2025

Biritaniya da Kanada sun kasance kasashe na farko na G7 da s**a dauki matakin, inda ake sa ran Faransa da sauran kasashe za su bibiyi taron Majalisar Dinkin Duniya na shekara-shekara (UNGA), wanda zai bude ranar Litinin a birnin New York

https://jaridaradio.com/burtaniya-australia-da-canada-sun-amince-da-kasar-falasdinu/

Karanta cikakken labarin ta link. Mene ne ra'ayinku kan wannan batu?

Burtaniya, Australia da Canada a ranar Lahadin da ta gabata sun amince da kasar Falasdinu a wani sau

Tallafin taki: Sanata Barau ya raba fiye da buhuna 4,600 ga malamai a Kano ta ArewaMataimakin Shugaban Majalisar Dattawa...
15/09/2025

Tallafin taki: Sanata Barau ya raba fiye da buhuna 4,600 ga malamai a Kano ta Arewa

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya raba buhunan taki 4,691 ga malaman makarantun firamare, sakandare da kuma makarantun allo (Tsangaya) a shiyyar Kano ta Arewa.

An gudanar da rabon a yankin masana’antu na Sharada da ke Kano, a wani bangare na kokarinsa na tallafa wa shirin gwamnatin tarayya wajen tabbatar da isasshen abinci a kasa.

Da yake jawabi ta bakin Shugaban Ma’aikatan ofishinsa, Farfesa Muhammad Ibn Abdallah, Sanata Barau ya ce wannan shirin an yi shi ne domin karfafawa malaman makarantu da malaman allo, kasancewar su ginshikin ci gaban al’umma.

Ya ce: “A baya mun raba buhunan taki sama da 40,000 ga manoma a fadin jihar Kano. Yau kuma mun mayar da hankali ga malamai, malaman Tsangaya, shugabannin makarantu da malamai na firamare da sakandare, domin su ma su ci gajiyar wannan shiri.”

Sanatan ya kara da cewa an bayar da takin kyauta, tare da kira ga masu karɓa da su yi amfani da shi yadda ya dace domin cimma burin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na samar da wadataccen abinci a kasa.

A cikin rabon, malaman Tsangaya za su samu buhuna 661, malaman sakandare na matakin karamar sakandire za su samu buhu 221, na matakin babbar sakandire za su samu buhu 392, yayin da malaman firamare za su samu buhu 227, sauran kuma za a rarraba su ga wasu rukuni daban-daban.

Shugaban kungiyar Shugabannin Makarantun Firamare na yankin, Musa Auwalu Gwarzo, ya gode wa Sanata Barau bisa wannan taimako, inda ya bayyana shi a matsayin “shugaba na kowa da kowa.”

12/09/2025

Barayin waya a Abuja sun shiga hannu bayan yunkurin kwace wayar wata mata mai tuki a daidai Chocolate Mall dake Wuse ll

09/09/2025

Isra'ila ta kai sabon harin sama kasar Qatar kan shugabannin Hamas a yau Talata yayin da ake tattaunawar tsagaita wuta a birnin Doha.

Allah Ya takaita

Mene ne ra'ayinku?

Gada ta rufta a unguwar Kureken Sani dake jihar Kano kuma dubban jama'a na neman mafita yayin da al'umma s**a aika sakon...
09/09/2025

Gada ta rufta a unguwar Kureken Sani dake jihar Kano kuma dubban jama'a na neman mafita yayin da al'umma s**a aika sakon agajin gaggawa ga Gwamna Abba Kabir Yusuf

05/09/2025

Bidiyo: An gano gawar mutanen da s**a nutse a kogi yayin tsere wa ‘yan bindiga 😭 Allah Ya jikansu Ya kuma takaita.

Akalla mutane 13 ne s**a mutu yayin da wasu sama da 20 s**a bace a Birnin Magaji da ke jihar Zamfara bayan wani jirgin ruwa da mazaunan yankin da s**a tsere daga harin ‘yan bindiga ya nutse a cikin wani kogi, k**ar yadda jami’an yankin da mazauna yankin s**a bayyana a ranar Asabar 30 ga watan Agusta.

Bayyana mana ra'ayinku?

A cewarta, matakin da hukumar babban birnin tarayya Abuja ta dauka ya saba wa ‘yancin da tsarin mulki ya ba kowane dan N...
05/09/2025

A cewarta, matakin da hukumar babban birnin tarayya Abuja ta dauka ya saba wa ‘yancin da tsarin mulki ya ba kowane dan Najeriya na zama da kuma neman abin rayuwa a kowane yanki na kasar nan, matukar ba za su kawo barazana ga zaman lafiya da tsaron jama’a ba.

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana damuwarta kan yadda ake ta mayar da ‘yan kasar daga babban birnin ta

Address

No. 2 Morijo Close Wuse II Abuja
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jarida Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jarida Radio:

Share