28/06/2025
Sanata Barau Ya Bayyana Jimaminsa Bisa Rasuwar Dattijon Dan Kasuwa, Alhaji Aminu Dantata
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Barau I. Jibrin, CFR, ya bayyana jimaminsa kan rasuwar tsohon dan kasuwa, dattijo, hazikin attajiri kuma babban mai taimakon al’umma, Alhaji Aminu Dantata, wanda ya rasu ranar Asabar yana da shekaru 94 a duniya.
A cikin wata sanarwa da mai bai wa Sanata Barau shawara kan harkokin yada labarai, Ismail Mudashir, ya fitar, Sanata Barau ya bayyana cewa marigayin ya taka gagarumar rawa wajen ci gaban Jihar Kano, Arewacin Najeriya da kuma kasa baki daya.
“Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Na yi matukar kaduwa da rasuwar mahaifinmu, dattijo kuma babban dan kasuwa mai taimakon al’umma, Alhaji Aminu Dantata, wanda ya rasu a ranar Asabar. Ya rayu cikin bautar Allah Madaukakin Sarki da kuma hidima ga al'umma.”
“Ina mika ta’aziyyata ga iyalan marigayin, ‘yan kasuwar jihar Kano, da daukacin al’ummar jihar Kano. Lallai mun yi rashin uba wanda gudunmawarsa wajen cigaban jihar mu da kasar nan gaba daya ba zai taba mantuwa ba.”
“Tsawon shekaru, ya kasance jigo a fannoni da dama na harkokin kasuwanci, cinikayya, gine-gine, kadarori, banki, masana’antu, da man fetur. Kwarewarsa a harkokin kasuwanci, ayyukan alheri da kuma kishin kasar sa za su ci gaba da zamo mana abin koyi. Alhaji Dantata ya kasance abin alfahari, abin koyi a rayuwa.” Inji Sanata Barau.
Sanata Barau ya kuma yi addu’ar Allah ya gafarta masa kurakuransa ya kuma karbi kyawawan ayyukansa.
“Allah ya jikan Alhaji Aminu Dantata ya kuma sanya shi cikin Aljannatul Firdausi. Allah ya ba iyalan sa da mu baki daya hakurin jure wannan babban rashi.”