29/05/2026
Dan majalisar Bichi ya rabawa alhazai 193 dala 300 kowanne a Mina domin Barka da Sallah
Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Bichi ta Tarayya, Hon. Abubakar Kabir Bichi, ya rabawa alhazan da s**a fito daga karamar hukumar Bichi su 193 dala 300 kowannensu yayin gudanar da aikin Hajjin bana a kasar Saudiyya.
An gudanar da rabon kudin ne a matsayin tallafin “Barka da Sallah” lokacin da dan majalisar ya kai ziyara sansanin alhazan Bichi da ke Mina a daren Alhamis.
Hon. Bichi ya gana da alhazan ne bayan kammala wasu muhimman ayyukan Hajji, inda ya taya su murnar zagayowar Sallar Layya tare da yi musu fatan alheri a kasa mai tsarki.
Da yake jawabi yayin ziyarar, dan majalisar ya ce ya bayar da tallafin ne domin tallafa wa alhazansa tare da nuna musu kulawa da kauna a lokacin bukukuwan Sallah duk da kasancewarsu nesa da gida.
Ya kuma bukaci alhazan da su ci gaba da yi wa Najeriya addu’o’in zaman lafiya, hadin kai da ci gaba, musamman Jihar Kano da mazabar Bichi.
Wasu daga cikin alhazan da s**a ci gajiyar tallafin sun bayyana jin dadinsu kan wannan karamci, suna masu cewa tallafin ya zo a daidai lokacin da ake bukatar hakan a Mina.
Alhazan sun kuma yi addu’ar Allah Ya saka wa Hon. Abubakar Kabir Bichi da alheri tare da kara ba shi damar yi wa al’umma hidima.