Jarida Radio

Jarida Radio Kafa Mai Inganci Za a Iya Sauraron Jarida Radio Kai Tsaye Ta www.jaridaradio.com Cikin Sa'o'i 24 a Kowacce Rana.

Dan majalisar Bichi ya rabawa alhazai 193 dala 300 kowanne a Mina domin Barka da SallahDan majalisar wakilai mai wakilta...
29/05/2026

Dan majalisar Bichi ya rabawa alhazai 193 dala 300 kowanne a Mina domin Barka da Sallah

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Bichi ta Tarayya, Hon. Abubakar Kabir Bichi, ya rabawa alhazan da s**a fito daga karamar hukumar Bichi su 193 dala 300 kowannensu yayin gudanar da aikin Hajjin bana a kasar Saudiyya.

An gudanar da rabon kudin ne a matsayin tallafin “Barka da Sallah” lokacin da dan majalisar ya kai ziyara sansanin alhazan Bichi da ke Mina a daren Alhamis.

Hon. Bichi ya gana da alhazan ne bayan kammala wasu muhimman ayyukan Hajji, inda ya taya su murnar zagayowar Sallar Layya tare da yi musu fatan alheri a kasa mai tsarki.

Da yake jawabi yayin ziyarar, dan majalisar ya ce ya bayar da tallafin ne domin tallafa wa alhazansa tare da nuna musu kulawa da kauna a lokacin bukukuwan Sallah duk da kasancewarsu nesa da gida.

Ya kuma bukaci alhazan da su ci gaba da yi wa Najeriya addu’o’in zaman lafiya, hadin kai da ci gaba, musamman Jihar Kano da mazabar Bichi.

Wasu daga cikin alhazan da s**a ci gajiyar tallafin sun bayyana jin dadinsu kan wannan karamci, suna masu cewa tallafin ya zo a daidai lokacin da ake bukatar hakan a Mina.

Alhazan sun kuma yi addu’ar Allah Ya saka wa Hon. Abubakar Kabir Bichi da alheri tare da kara ba shi damar yi wa al’umma hidima.

Jam'iyyar ADC (African Democratic Congress) a ranar Jumma'a ta zargi Hukumar Yaki da Karban Rashawa da Sauran Laifuka Ma...
22/05/2026

Jam'iyyar ADC (African Democratic Congress) a ranar Jumma'a ta zargi Hukumar Yaki da Karban Rashawa da Sauran Laifuka Masu Alaka da Hakan (ICPC) da hana musu damar ganawa da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, bayan da aka hana wata tawaga da ta kunshi Sakataren Jam'iyyar na Kasa, Rauf Aregbesola; Sakataren Yada Labarai na Kasa, Mallam Bolaji Abdullahi; da kuma Sakataren Kwamitin Manufofi da Siffofin Jam'iyyar ADC, Mallam Salihu Lukman, ganawa da shi a babban ofishin hukumar da ke Abuja.

A cikin wata sanarwa mai zafi da jam'iyyar ta fitar, ta bayyana cewa a baya ta riga ta aike da wasika zuwa ga Shugaban Hukumar ICPC, Dr. Musa Adamu Aliyu, tana neman izinin ziyartar El-Rufai sak**akon fargabar da iyalansa s**a nuna game da zargin da ake yi na hana shi ganawa da likitoci da kuma hana ba shi abinci.

Jam'iyyar ADC ta yi gargaɗin cewa "Najeriya da ma duniya baki ɗaya suna kallo," inda ta ƙarfafa cewa ana fuskantar da tsohon gwamnan da tsoratarwa gami da bita-da-ƙullin siyasa, yayin da kuma ta yi barazanar tara mambobin jam'iyyar na ƙasa baki ɗaya idan har aka ci gaba da hana musu damar ganawa da shi.

Jam'iyyar ADC ba za ta zuba ido tana kallo ana muzguna wa ɗaya daga cikin shugabanninta da wannan tsari na tsangwama da kuma wulaƙanci da aka tsara shi da gangan ba. Najeriya tana kallo kuma kungiyoyin ƙasa da ƙasa suna kallo. Duniya baki ɗaya tana kallo.

"Saboda haka, muna buƙatar da lallai Hukumar ICPC ta ba iyalansa, likitoci, lauyoyi, da kuma shugabannin jam'iyyarsa ta siyasa damar ganawa da Mallam El-Rufai ba tare da wani shinge ba cikin gaggawa. Tun abin da bai kai haka ba, zai ƙara tabbatar da tunanin da mutane suke da shi ne na cewa ana amfani da hukumomin gwamnati a matsayin makamin yaƙi da muryoyin 'yan hamayya."

Hotunan yakin neman zaben shugaban kasa na jigo a jam'iyyar ADC (African Democratic Congress) kuma tsohon Ministan Harko...
22/05/2026

Hotunan yakin neman zaben shugaban kasa na jigo a jam'iyyar ADC (African Democratic Congress) kuma tsohon Ministan Harkokin Sufuri, Rotimi Chibuike Amaechi, a halin yanzu sun bazu a manyan sassan jihar Katsina.

Tsohon ministan ya tsallake tantancewa a gaban kwamitin tantance 'yan takarar shugaban kasa na jam'iyyar ADC a kwanakin baya.

Zai yi fafutukar neman tikitin takarar shugaban kasa na jam'iyyar ADC tare da dan kasuwa Mohammed Hayatudeen da kuma tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar.

Hotunan masu taken ‘Sai Amaechi a Shugaban Kasa’ suna nan baje a manyan titunan cikin garin Katsina da kuma gadar sama ta Kofar Kaura, da sauran wurare.

Majiyoyi sun bayyana cewa wata kungiyar magoya baya mai suna ‘Amaechi Ambassadors’ (Jakadun Amaechi) ce ke da alhakin samar da wannan ci gaba.

Hukumar Gudanar da Al'amuran Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta yi gargaɗin cewa watan Satumba na wannan shekara shi ne za...
22/05/2026

Hukumar Gudanar da Al'amuran Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta yi gargaɗin cewa watan Satumba na wannan shekara shi ne zai kasance lokacin da ambaliyar ruwa za ta kai kololuwa a Jihar Kebbi, inda hasashen ke nuna cewa za a sami ambaliyar ruwa mai tsanani a fadin ƙananan hukumomi 12.

Hukumar ta bayyana cewa ana sa ran Kogin Neja zai cika ya ambaliya a wannan lokacin, wanda hakan zai janyo nutsar da gonaki, matsugunan da ke gaɓar kogi, da kuma manyan abubuwan more rayuwa a faɗin jihar.

Shugabar Hukumar NEMA ta Ƙasa, Zubaida Umar wadda Darakta a Shiyyar Arewa maso Yamma Aliyu Shehu Kafindongi ya wakilta, ita ce ta bayyana hakan a lokacin taron masu ruwa da tsaki kan kamfen ɗin shiri da dakile masifu na kasa na shekarar 2026 da aka gudanar a Birnin Kebbi.

Ta bayyana cewa ana sa ran matakin ruwan zai ci gaba da karuwa har zuwa watannin Oktoba da Nuwamba, wanda hakan zai tsawaita illar ambaliyar a cikin al'ummomin da abin zai shafa.

A cewarta, Kebbi tana ɗaya daga cikin jihohin da ke cikin babban haɗari a wannan shekara, inda aka gano ƙananan hukumomi 12 a matsayin waɗanda za su iya fuskantar barazanar.

Waɗannan ƙananan hukumomi sun haɗa da Argungu, Augie, Bagudu, Birnin Kebbi, Dandi, Fakai, Koko/Besse, Maiyama, Ngaski, Shanga, Zuru da kuma Yauri.

"Muna kira ga dukkan abokan haɗin gwiwa, sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin addini, ƙungiyoyin mata da na matasa, kafofin watsa labarai da kamfanoni masu zaman kansu da su tallafa wa NEMA wajen yaɗa saƙon gargaɗin farko-farko," in ji ta.

Tun da fari, Babban Sakatare na Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Kebbi (SEMA), Abubakar Abdullahi, ya bayyana cewa taron an shirya shi ne domin haɗa ƙarfi da ƙarfe na masu ruwa da tsaki don magance matsalar ambaliyar ruwa a jihar.

Ya ce gwamnatin jihar ta riga ta ɗauki matakai don tunkarar ambaliyar ruwan da aka yi hasashenta.

“Gara mu yi shiri domin ambaliyar da aka yi hasashe da a ce mun jira har sai masifar ta auku. Muna yaba wa matakan da gwamnati ta riga ta ɗauka,” in ji shi.

Shi ma da yake jawabi, Darakta na Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) na Jihar, Nasiru Karofi, ya bayyana cewa Jihar Kebbi tana ɗaya daga cikin guraren da ke fuskantar babban haɗari na sauyin yanayi, inda ya yi kira da a ci gaba da gudanar da ayyukan wayar da kai da kuma shiri na gari.

Ƙasashen ƙawance na NATO da jami'an tsaro sun nuna damuwa a ranar Jumma'a game da sanarwar da Shugaban Amurka Donald Tru...
22/05/2026

Ƙasashen ƙawance na NATO da jami'an tsaro sun nuna damuwa a ranar Jumma'a game da sanarwar da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi, na cewa zai tura sojojin Amurka 5,000 zuwa ƙasar Poland, makonni kaɗan kacal bayan ya ba da umarnin janye adadin dakarun daga nahiyar Turai.

Wannan canjin tunani na ba-zata ya zo ne bayan makonni da dama da Trump da gwamnatinsa s**a shafe suna kalaman rage dakarun Amurka a Turai — ba wai ƙarawa ba. Umarnin farko na Trump ya janyo hargitsi da gaggawa a tsakanin kwamandojin soja, kuma ya bar ƙasashen ƙawance, waɗanda dama can suke shakku kan sadaukarwar Amurka ga tsaron Turai, cikin tunanin irin dakarun da za su maye gurbinsu a gabacin yankin NATO da ke makwabtaka da Rasha da Ukraine.

A farkon wannan watan, gwamnatin Trump ta bayyana cewa tana rage adadin dakarunta a Turai da kusan sojoji 5,000, kuma jami'an Amurka sun tabbatar da cewa dakarun soja kusan 4,000 ne aka dakatar da kai-komonsu zuwa Poland daga Jamus. Haka kuma, an dakatar da tura jami'an Amurka zuwa Jamus waɗanda aka horar da su kan harba manyan mak**ai masu dogon zango.

Sai dai, a wani sako da ya wallafa a shafin Truth Social a ranar Alhamis, Trump ya ce yanzu zai tura "ƙarin sojoji 5,000 zuwa Poland," inda ya buga misali da kusancinsa da Shugaban ƙasar Poland Karol Nawrocki, wanda Trump ya goyi bayansa a zaɓen da aka yi a shekarar da ta gabata.

Jami'an tsaron Amurka su ma sun nuna nasu damuwar. “Mun kwashe kusan makonni biyu muna ƙoƙarin daidaita alamura bayan sanarwar farko. Mu kanmu ba mu san me wannan yake nufi ba,” in ji ɗaya daga cikin jami'ai biyu da s**a yi magana da sharaɗin ɓoye sunansu domin tattauna batutuwan tsaro na sirri.

Amma Rubio ya ce ƙasashen ƙawance na Washington sun fahimci cewa canje-canje a zaman sojojin Amurka a Turai zai ci gaba da faruwa yayin da gwamtatin Trump take sake nazarin buƙatun dakarunta. “Ina jin akwai kyakkyawar fahimta cewa a ƙarshe dai za a sami ragowar sojojin Amurka a Turai fiye da yadda aka saba gani a tarihi saboda dalilai daban-daban,” in ji shi.

10/05/2026

Jarumin fina-finai wanda ya koma harkar siyasa, Joseph Vijay, ya rantsu a matsayin babban ministan jihar Tamil Nadu da ke kudancin Indiya a ranar Lahadi (10 ga Mayu).

Jam’iyyar Vijay ce ta zo ta daya a zaben jihar da aka gudanar kwanan nan, inda ta lashe kujeru 108 daga cikin kujeru 234 na majalisar dokokin jihar, tare da doke wasu jam’iyyu biyu da s**a kwashe shekaru da dama suna mulkin jihar.

Vijay ya yi rantsuwar ne a gaban manyan shugabannin jam’iyya, abokan kawancen siyasa, da kuma fitattun mutane daga masana’antar fina-finai.

Wasu jam’iyyu biyar, ciki har da babbar jam’iyyar hamayya ta Indiya wato "Congress" da kuma jam’iyyar "Communist" ta Indiya, sun bayar da goyon bayansu domin kafa gwamnati a karkashin jagorancinsa.

❤️😎

Mutane na gudanar da zanga-zangar nuna adawa da takaddama kan zaɓe da ta ki ci ta ki cinyewa a ƙarƙashin jagorancin Shug...
10/05/2026

Mutane na gudanar da zanga-zangar nuna adawa da takaddama kan zaɓe da ta ki ci ta ki cinyewa a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Hassan Sheikh Mohamud da kuma wa’adin mulkin gwamnatin tarayya na yanzu; yayin da hukumomi ke cewa an tsawaita wa’adin, su kuwa jiga-jigan ’yan hamayya da wasu shugabannin yankuna na cewa wa’adin zai ƙare ne a ranar 15 ga Mayu, 2026. Ana gudanar da zanga-zangar ne a filin wasa na Eng. Yariisow da ke kan titin Dr. Kadare a birnin Mogadishu na ƙasar Somaliya, a yau 10 ga Mayu, 2026.

Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Bayan Ganawar Ribadu Da VanceKasashen Najeriya da Amurka sun kulla yarjejeni...
09/05/2026

Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Bayan Ganawar Ribadu Da Vance

Kasashen Najeriya da Amurka sun kulla yarjejeniyar kara zurfafa hadin gwiwa a fannin tsaro, yaki da ta’addanci da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin Yammacin Afirka.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mai Taimakawa Shugaban Kasa kan Yada Labarai, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Asabar, 9 ga watan Mayun 2026.

Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro (NSA), Mallam Nuhu Ribadu, ya kai ziyarar aiki ta kwanaki uku a Amurka, inda ya gana da manyan kusoshin gwamnatin kasar. A yayin ziyarar, Ribadu ya isar da sakon Shugaba Bola Ahmed Tinubu na jajircewa wajen dorewar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

Ribadu ya gana da Mataimakin Shugaban Amurka, J.D. Vance, Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio da Sauran manyan jami’an diflomasiyya da na tsaro na kasar Amurka.

Babban makasudin wannan ganawa shi ne duba yadda za a inganta raba bayanan sirri da kuma karfafa ayyukan soji na hadin gwiwa. NSA Ribadu ya jaddada muhimmancin taimakon juna don magance matsalolin tsaro da s**a addabi yankin Sahel, musamman Ayukan ta’addanci da tsagera, Safarar miyagun kwayoyi da mak**ai da Laifukan da ake aikatawa ta hanyar yanar gizo.

Hukumomin Amurka sun jinjina wa Najeriya a matsayinta na jagora a yankin Afirka, musamman wajen jagorantar yaki da ta'addanci a tafkin Chadi.

A nata bangaren, Najeriya ta bayyana cewa tana amfani da dabarun karfin soja da kuma tattaunawa da inganta rayuwar jama'a don magance tushen matsalar rashin tsaro.

"Najeriya tana godiya ga Amurka bisa taimakon da take bayarwa a bangaren horar da jami'ai, ba da bayanan sirri, da kuma tallafin jinkai." — Ribadu

A karshen taron, bangarorin biyu sun amince su ci gaba da tuntubar juna akai-akai ta hanyar hadin gwiwa na musamman don tabbatar da cewa dukkan yarjejeniyoyin da aka kulla sun fara aiki yadda ya k**ata.

Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa, Sun Ceto Mutum 50 – DHQRundunar Tsaro ta Kasa (DHQ) ta bayyana cewa dakarun k...
09/05/2026

Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa, Sun Ceto Mutum 50 – DHQ

Rundunar Tsaro ta Kasa (DHQ) ta bayyana cewa dakarun kasar nan sun samu nasarar ragargazar dimbin ’yan ta’adda, inda s**a k**a wasu da dama tare da ceto mutum sama da 50 da aka yi garkuwa da su a fadin kasar nan.

Wadannan nasarori sun faru ne a yayin ayyukan kakkaba da sojoji s**a gudanar tsakanin ranar 30 ga watan Afrilu zuwa 7 ga watan Mayun 2026.

Daraktan Yada Labarai na Rundunar Tsaro, Manjo Janar Michael Onoja, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Abuja. Ga yadda nasarorin suke kasance a kowacce shiyya:

• Arewa maso Gabas (Operation HADIN KAI): Rundunar ta dakile hare-haren ’yan ta’adda a Magumeri da ke jihar Borno. Haka kuma, wasu daga cikin maharan sun mika wuya, yayin da aka k**a masu kai musu kayan abinci da mak**ai.

• Arewa maso Yamma (Operation FANSAN YAMMA): Sojoji sun yi artabu da ’yan fashi a jihohin Katsina da Zamfara, inda aka kashe da dama tare da kwace babura da mak**ai.

• Arewa ta Tsakiya (Operation SAVANNAH SHIELD): An ceto wadanda aka yi garkuwa da su tare da k**a masu safarar harsasai har guda 250 a cikin birnin Abuja.

• Jihar Filato: Jami'an tsaro sun bankado wata masana’antar kera mak**ai ba bisa ka’ida ba a Jos ta Kudu, inda aka k**a mutanen da ake zargi da kera bindigogi.

• Jihar Benuwai da Kogi: An samu nasarar ceto wasu yara dalibai da aka sace daga gidan marayu.

Janar Onoja ya kara da cewa, dakarun Operation DELTA SAFE a Kudancin kasar da kuma Operation UDO KA a Kudu maso Gabas duk sun samu nasarar k**a masu garkuwa da mutane da kuma dillalan mak**ai na kungiyar IPOB/ESN.

"Rundunar sojin kasa a karkashin jagorancin Shugaban Hafsun Tsaro, Olufemi Oluyede, ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa ’yan Najeriya sun rayu cikin lumana da kwanciyar hankali." — Maj. Gen. Onoja

Wannan gagarumar nasara ta nuna cewa jami’an tsaro sun sake zage damtse wajen ganin sun kawo karshen matsalolin tsaro da s**a addabi sassan kasar nan.

Zaben 2027: Sanata Barau Jibrin Ya Cike Tare Da Mika Fom Din Takarar Sanatan Kano Ta Arewa​​Mataimakin Shugaban Majalisa...
07/05/2026

Zaben 2027: Sanata Barau Jibrin Ya Cike Tare Da Mika Fom Din Takarar Sanatan Kano Ta Arewa

​Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya mika fom dinsa na tsayawa takarar neman kujerar Sanatan Kano ta Arewa a karkashin inuwar jam’iyyar APC mai mulki.

​Sanata Barau, wanda ke rike da lambar girmamawa ta kasa ta CFR, ya mika fom din ne a safiyar yau Alhamis a sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja, inda ya bayyana jam’iyyar ta APC a matsayin "jam’iyya mafi girma a nahiyar Afirka."

​Cikin wata sanarwa da ya fitar jim kadan bayan mika fom din a shafinsa na Facebook, Sanata Barau ya nuna matukar godiyarsa ga daukacin al’ummar mazabarsa ta Kano ta Arewa. Ya bayyana cewa goyon baya da amincewar da suke ba shi a tsawon shekaru shi ne kashin bayan nasarorin da yake samu.

​"Ina matuƙar godiya ga al’ummar Kano ta Arewa bisa goyon baya, amincewa da haɗin kai da suke nuna min a tsawon shekaru," in ji Sanatan.

​Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan ya sake nanata kudurinsa na ci gaba da aiki tukuru domin magance matsalolin da ke damun yankinsa. Ya bayyana cewa babban burinsa shi ne kaddamar da shirye-shiryen da za su taba rayuwar talaka kai-tsaye a dukkan kananan hukumomi 13 da ke karkashin mazabar tasa.

Address

2 Morija Close Wuse II
Abuja
900110

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jarida Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jarida Radio:

Share