DARUL TAQWA TV

DARUL TAQWA TV Educate entertainment

Ango mafi karanchin shekaru da yayi Aure a shekarar 2024 a jihar Katsina Muhammad Kabir Ibrahim (Guys) yayi murna tare d...
19/10/2025

Ango mafi karanchin shekaru da yayi Aure a shekarar 2024 a jihar Katsina Muhammad Kabir Ibrahim (Guys) yayi murna tare da matarsa ta cika shekara 1 da Auren su.

Wane fata zakuyi agaresu ?

🎓 HON. BABANGIDA MALIYA A WAJEN TARON “MAIDA YARA MAKARANTA”Hon. Babangida Maliya ya halarci kuma ya ɗauki nauyin babban...
19/10/2025

🎓 HON. BABANGIDA MALIYA A WAJEN TARON “MAIDA YARA MAKARANTA”

Hon. Babangida Maliya ya halarci kuma ya ɗauki nauyin babban taron Maida Yara Makaranta, wanda aka shirya tare da haɗin gwiwar Hukumar Ilimi Bai Daya ta Jihar Bauchi, ƙarƙashin jagorancin Alhaji Adamu Muhammad Duguri — Hakimin Ƙasar Duguri kuma wakilin Bauchi.

Taron ya kasance wani muhimmin mataki na ƙarfafa ilimi da dawo da yara makaranta domin gina makoma mai haske ga al’umma.

📚 Tekun Maliya
Ƙarfafa Ilimi, Gina Makoma.

Allahu Akbar wata baiwar Allah musulma tasayi wani katon coci ajahar Kaduna Kuma ta Maida gun yazamo wajen karatun Addin...
19/10/2025

Allahu Akbar wata baiwar Allah musulma tasayi wani katon coci ajahar Kaduna Kuma ta Maida gun yazamo wajen karatun Addinin musulunchi Alhamdulillah.

TARON HADIN KAI DA KARFAFA GINSHIKIN JAM’IYYAR PDP A JAMA’AREA yau Asabar, 18 ga Oktoba, 2025, an gudanar da muhimmin ta...
18/10/2025

TARON HADIN KAI DA KARFAFA GINSHIKIN JAM’IYYAR PDP A JAMA’ARE

A yau Asabar, 18 ga Oktoba, 2025, an gudanar da muhimmin taron masu ruwa da tsaki (Stakeholders Meeting) na jam’iyyar PDP a karamar hukumar Jama’are, domin tattauna hanyoyin da za su ƙarfafa jam’iyyar a matakan gida da waje.

Taron ya kasance daya daga cikin mafi muhimmanci a wannan lokaci, kasancewar ya zo ne a daidai lokacin da ake buƙatar haɗin kai, fahimtar juna, da sake gina martabar jam’iyya bisa gaskiya da adalci.

A cikin jawaban da aka gabatar, an jaddada cewa jam’iyyar PDP ta tsaya ne kan ginshiƙan dimokuraɗiyya, adalci da ci gaban al’umma, tare da jan hankali ga muhimmancin aiki tare domin tabbatar da nasara a matakai daban-daban.

Masu ruwa da tsaki sun yi kira da a sake buɗe sabbin hanyoyin haɗin kai da sulhu a tsakanin ’ya’yan jam’iyya, tare da ƙarfafa tushe a mazabu, farfaɗo da ɓangarorin matasa da mata, da kuma inganta hanyoyin sadarwa tsakanin shugabanni da mambobi.

Wani daga cikin jagororin taron ya jaddada cewa:

> “Ba jam’iyya ce kaɗai ke kawo nasara ba idan babu haɗin kai da aiki tare. Lokaci ya yi mu dawo mu ɗora kan tafarkin gaskiya, mutunta juna, da kishin jam’iyya. PDP ba ta rushe ba — tana nan daram, tana ƙara ƙarfafawa.”

Haka kuma, mahalarta taron sun yaba wa shugabannin jam’iyyar a matakan jiha da ƙasa bisa jajircewarsu wajen jagorantar jam’iyya cikin natsuwa da hangen nesa, tare da kira da a ci gaba da mara musu baya domin tabbatar da nasarar siyasa a gaba.

🔵 Jam’iyyar PDP a Jama’are na tabbatar da cewa tare da haɗin kai, mutunta juna, da jajircewa, za ta ci gaba da zama ginshiƙi mai ƙarfafa dimokuraɗiyya da kare muradun al’umma.
Usman Adamu Dawu
Classic TV Albarka Radio Jamaare Gida Jibwis Jama'are

DA DUMI-DUMI: Hukumar Leken Asirin Sojojin Najeriya ta k**a manyan jami’an soja 16 bisa zargin shirin kifar da gwamnatin...
18/10/2025

DA DUMI-DUMI: Hukumar Leken Asirin Sojojin Najeriya ta k**a manyan jami’an soja 16 bisa zargin shirin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu — Rahoton Sahara Reporters

Rahotanni daga Sahara Reporters sun bayyana cewa Hukumar Leken Asirin Rundunar Sojin Najeriya (DMI) ta tsare wasu manyan hafsoshin soja guda 16 da ake zargin suna da hannu a wani shirin juyin mulki da nufin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Majiyar ta bayyana cewa bincike yana ci gaba domin gano sauran jami’an da ake zargin suna da hannu a wannan shiri, wanda ake kira “na cikin gida”, wanda ya jawo hankalin hukumomin tsaro.

Har yanzu ba a bayyana sunayen jami’an da ake tsare da su ba, sai dai majiyar tsaro ta tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya ta dauki lamarin da matuƙar muhimmanci, tare da tabbatar da cewa za a gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiyar al’amari.

Lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce a fagen siyasa da tsaro a ƙasar, yayin da jama’a ke ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan wannan ci gaban mai daukar hankali.

18/10/2025

Assalamualakum waharmatullah Yau ma Kamar Kullum a Shirin DANDALIN MATASA
na tashar Classic TV munsamu bakuncin wani haziki daga gidan Siyasar Dr wato Abdulkadir Muhammad Inuwa Wanda Aka finsani da DULELE Ku biyo mu dan jin abunda yazo mana dashi

Jibwis Jama'are Darus Sunnah TV Adamu Ahmad Muhammad Mahmood Muhammad Chadi Mubarak Ishaq Sarkin Haya Zakaria M Adam Mai Rakumi ChannelTv Jama'are Abdullahi Musa Sintali Siir M D Azare

Idan Ansami Wani abu mak**ancin Haka meyak**ata muyiKuzo mu kari juna Ku rubutamana Yadda zaayi a comment Section 👇👇👇👇👇👇...
18/10/2025

Idan Ansami Wani abu mak**ancin Haka meyak**ata muyi

Kuzo mu kari juna

Ku rubutamana Yadda zaayi a comment Section
👇👇👇👇👇👇👇👇👇
Classic TV Darus Sunnah TV Albarka Radio

ALLAHU AKBAR! 🌙Wani dattijo mai albarka, Alaramma Alhaji Ali Dunjuje, ya kammala rubuta Al-Qur’ani Mai Girma sau 150 — a...
18/10/2025

ALLAHU AKBAR! 🌙

Wani dattijo mai albarka, Alaramma Alhaji Ali Dunjuje, ya kammala rubuta Al-Qur’ani Mai Girma sau 150 — abin mamaki da alfahari daga ƙaramar hukumar Jama’are, Jihar Bauchi.

Lallai wannan aiki ne mai matuƙar daraja, kuma yana da muhimmanci mu taya shi da addu’a da fatan alheri.

🕋 Don Allah, ku raba wannan labari zuwa ƙungiyoyin Musulmai (aƙalla guda 5) domin su saka shi cikin addu’o’insu.

👇
Ku ziyarci shafin Classic TV yanzu,
👉 Ku bi shafin don samun irin waɗannan labarai masu ƙayatarwa.

| | | |

18/10/2025

Kadan daga cikin Abunda ya faru a wasan River Star da kuma Zenith D-jeji shin wannan abun ya chanchanci Penalty ko kuma babu penalty

Kifadamana a comment Section
👇👇👇👇👇👇👇

TATTAUNAWA:A halin yanzu, jam’iyyar APC mai mulkin ƙasa tana da iko a jihohi 24 daga cikin 36 na Najeriya, yayin da PDP ...
17/10/2025

TATTAUNAWA:
A halin yanzu, jam’iyyar APC mai mulkin ƙasa tana da iko a jihohi 24 daga cikin 36 na Najeriya, yayin da PDP ke da jihohi takwas (8).
Jam’iyyun LP, APGA, da NNPP kuma kowacce tana da jiha ɗaya (1) kacal.

Tambaya ita ce👇
Shin, Najeriya ta k**a hanyar zama ƙasa mai tsarin jam’iyya ɗaya?
Ku bayyana ra’ayoyinku a ƙasa 👇

Classic TV Jibwis Jama'are Darus Sunnah TV LABARI DAGA BAUCHI

17/10/2025

Wani daga cikin Yan kwallon Zenith D-jeji kenan yake murna duk da Alkalan Wasa basu yanke hukunci akan abunda yafaru ba,
Me zakuce san gane da wannnn Tataburzar
Muhadu a comment section

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DARUL TAQWA TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to DARUL TAQWA TV:

Share