Jarida.ng

Jarida.ng Wannan shafi ne da zai rika kawo muku sabbin labarai na gida Najeriya da kuma na kasashen ketare cikin harshen Hausa.

Sannan za ku iya ziyartar shafinmu domin karin bayani game damu a https://jarida.ng

06/09/2024

Halin da ake ciki fa yanzu ya wuce batun satar kudin gwamnati, an shiga zamanin "ku kawo na hannunku".

Wannan yana daga cikin matsalolin siyasar kudi.

Sun biya an zabesu, ya k**ata mu sani cewa duk Wanda ya bada kudi domin a zave shi, ya san duk wata hanya da zai bi domin ya mayar da kudinsa ya kuma ci riba.

Idan bamu gyara ba, ba za a samu gyara ba a kasar nan.

Dole mu ajiye siyasar kudi, mu koma zaben nagarta da cancanta.

Mu hada Kai mu yiwa 'yan jari hujja da marasa kishin kasa da jama'a ritaya daga siyasa.

Mulki, a tsari na hankali da gaskiya, ba hanyar samun kudi ko tara abin duniya ko Jin dadi da more rayuwa bane.

Matukar mutanen kirki masu hikima da kishin jama'a basu shiga an dama dasu a siyasa da tsarin Mulki ba, haka 'yan WAWA zasu cigaba da zuwa da jakar kudi suna siyen hanyarsu ta zuwa baitulmanin gwamnati domin jidar duk Wani arziki da kasa da jama'ar kasa s**a mallaka.

A yayin da jikinmu yake gaya mana, Allah yasa a gaba mu yi aiki da maganar Bahaushe ta "IDAN KUNNE YA JI JIKI YA TSIRA".

©Malam Naziru

15/07/2020

Wata mata mai shekaru 35 ta yi 'wuff' da ɗa bayan mahaifin ɗan ya sake ta.

Gwamnan jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai ya tsawaita dokar hana fita a jihar da kwanaki 30.
26/04/2020

Gwamnan jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai ya tsawaita dokar hana fita a jihar da kwanaki 30.

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da tsawaita dokar zaman gida saboda annobar coronavirus a jihar da kwanaki 3O daga ranar 26 ga watan Afrilun 2020. Gwamnatin jihar ta ce, “Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El Rufai ya tsawaita dokar zaman gida da aka saka a jihar da kwanaki 3O. “Gwamnatin jihar ta dauk...

An k**a wasu mutane 39 a otel suna taro na nuna tsiraici da rawar badala a Legas.
26/04/2020

An k**a wasu mutane 39 a otel suna taro na nuna tsiraici da rawar badala a Legas.

‘Yan sanda a Legas sun k**a mutum 620 da s**a saba dokar kulle da aka saka a jihar domin dakile yaduwar cutar Korona a birnin. Kakakin rundunar yan sandan jihar, Bala Elkana ya ce an k**a mutanen ne daga ranar 21 ga watan Afrilu zuwa 24 ga watan Afrilun 2020 k**ar yadda Sahara reporters ta […]

Allah ya yi wa Farfesa Balarabe Maikaba na Jami'ar Bayero ta Kano rasuwa.
26/04/2020

Allah ya yi wa Farfesa Balarabe Maikaba na Jami'ar Bayero ta Kano rasuwa.

Farfesa a tsangayar nazarin aikin jarida a Jam’iar Bayero ta Kano, Balarabe Maikaba ya rasu. Sahara Reporters ta ruwaito cewa Maikaba shine Farfesa na shida da ya mutu a Kano cikin kwanaki shida. Wata majiya mai kusanci da marigayin ta shaida wa majiyar Jarida.ng cewa za ayi janaizarsa bayan salla...

An yi girgizar kasa a wani yanki na Makkah ran jajiberin Azumin Ramadan
24/04/2020

An yi girgizar kasa a wani yanki na Makkah ran jajiberin Azumin Ramadan

An samu girgizan kasa mara muni mai karfin digiri 2.7 a kan maaunin Richter wadda ya yi zurfin kilomita 9 a yankin Qunfudah na garin Makkah k**ar yadda kafar watsa labarai na kasar, SPA, ta ruwaito a ranar Alhamis. Duk da cewa girgizan kasar ba ta yi tsanani ba, wasu mutane a da ke zaune […]

Wasu ƙasashen duniya 15 da har yanzu Korona ba ta shiga ba.
24/04/2020

Wasu ƙasashen duniya 15 da har yanzu Korona ba ta shiga ba.

A yayin da gwamnatoci na kasashen duniya ke kokarin dakile yaduwar annobar coronavirus, akwai wasu kasashe kimanin 15 a duniya da har yanzu ba su bayar da rahoton bullar cutar a kasar su ba. Tun bayan bullar cutar a birnin Wuhan da ke lardin Hubei a watan Disamban 2019, kimanin mutum miliyan 2.6 ne....

Wa’iyazubillah: An k**a mutane 21 suna daukar fim din batsa a yayin da ake fama da wannan masifa ta Coronavirus
24/04/2020

Wa’iyazubillah: An k**a mutane 21 suna daukar fim din batsa a yayin da ake fama da wannan masifa ta Coronavirus

Mutane 21 ciki kuwa hadda wata ‘yar kasar Jamus sun shiga hannun jami’an tsaro a kasar Kenya, bayan an k**a su suna daukar fim din batsa a yankin Nakuru a wannan lokaci da aka sanya dokar hana zirga-zirga saboda annobar Coronavirus. A yadda gidan talabijin na Kenya’s Citizen TV ya ruwaito, duk...

Ramadana: Manyan Malaman addini sun koma tafsiri ta yanar gizo saboda Coronavirus
24/04/2020

Ramadana: Manyan Malaman addini sun koma tafsiri ta yanar gizo saboda Coronavirus

Bayan dakatar da taron addini a Najeriya saboda matsalar Coronavirus, Malaman addini da yawa da kungiyoyin dake gabatar da tafsiri a watan Ramadana zasu koma gabatar da tafsiri ta yanar gizo. Malaman addini da dama a jihohin Najeriya sun bayyanawa Daily Trust cewa wannan matsala ta saka dole zasu ca...

Annobar covid-19 ta harbi karin mutane 108 a Najeriya, jimilla ta kusa 1,000
24/04/2020

Annobar covid-19 ta harbi karin mutane 108 a Najeriya, jimilla ta kusa 1,000

NCDC ta fitar da sanarwar ne da kusan karfe 12:00 na dare, inda ta bayyana cewa annobar ta hallaka jimillar mutane 31 a fadin Najeriya, wasu mutane 197 kuma su ka samu waraka.

Gwamnatin Afghanistan ta saki yan kungiyar Taliban da ke tsare a kurkuku ana gobe fara azumin Ramadan
23/04/2020

Gwamnatin Afghanistan ta saki yan kungiyar Taliban da ke tsare a kurkuku ana gobe fara azumin Ramadan

Ana goba fara azumin watan Ramadan, gwamnatin kasar Afganistan ta sake sakin wasu yan Taliban da ke tsare a kurkuku a cewar Kwamitin Tsaro na kasar a ranar Alhamis duk da yawaitar hare hare a kasar. A ranar Laraba ne aka sako fursunoni 55 daga kurkuku daga a wani yunkuri da gwamnatin ke yi domin [.....

An ga watan Azumin watan Ramadana a Saudiyya, gobe Juma'a za ta zama 1 ga watan Ramadan na shekarar 1441 a Saudiyya.
23/04/2020

An ga watan Azumin watan Ramadana a Saudiyya, gobe Juma'a za ta zama 1 ga watan Ramadan na shekarar 1441 a Saudiyya.

Mahukunta a kasar Saudiyya sun sanar da ganin jaririn watan Azumin Ramadana. Sanarwar ya fito ne daga masallatan Harami biyu ta shafin su na Facebook. Hakan na nufin cewa gobe Jumaa za ta zama 1 ga watan Ramadana na shekarar 1441 wanda zai yi dai dai dai 24 ga watan Afrilun 2020. DUBA WANNAN: An [.....

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jarida.ng posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share