
06/10/2025
WADANDA SUKA MUTU SAKAMAKON RUFTAWAR MAKARANTA YA KAI 54,
-Bin Muhammad KD
Daraktan ayyuka na hukumar bincike da ceto ta kasar, ya shaidawa taron manema labarai cewa: "Mun gano gawarwakin mutane 54 da suka hada da ragowar mutane biyar," Yudhi Bramantyo,
Jami'an ceto na ci gaba da aiki ba dare ba rana domin gano wadanda suka bata. "Muna fatan kammala bincike a yau (Litinin) tare da mika gawarwakin" ga iyalai, in ji Yudhi.
Mataimakin darektan hukumar kula da bala'o'i ta kasar Budi Irawan, ya ce rugujewar ita ce bala'i mafi muni da aka taba samu a kasar Indonesia a bana. Ya kara da cewa akalla mutane 13 ne suka bata.