30/05/2026
MUTANE 18 SUN MUTU 29 SUN JIKKATA A HATSARIN MOTA A AFGHANISTAN
Daga:Bin Muhammad KD
Kakakin gwamnan Laghman Abdul Malik Niyazi, yace' hatsarin ya faru da safiyar yau a yankin Sorkhakan na gundumar Qarghayi a sak**akon hakan mutane 18 ciki har da yara 10 da mata 5 s**a rasa rayukansu, yayin da wasu 29 s**a jikkata.
Wadanda s**a jikkata a wannan hatsarin an kai su babban asibitin Nangarhar, kuma an fara bincike kan musabbabin faruwar hatsarin.
Haka kuma, Zabihullah Mujahid, kakakin gwamnatin Taliban, ya bayyana juyayinsa ga iyalan wadanda s**a rasa rayukansu a wannan hatsari. A cikin wani sakon nasa, ya yi addu'ar Allah ya gafarta wa wadanda s**a mutu, ya yi wa wadanda s**a jikkata addu’ar samun waraka cikin gaggawa, ya kuma bai wa iyalan wadanda s**a rasa rayukansu hakuri da jimiri.
Wannan hatsari ya faru ne da misalin ƙarfe 5:30 na safiyar yau a kan babbar hanyar Kabul - Jalalabad, a cikin iyakar gundumar Qarghayi na lardin Laghman.