SR TV HAUSA

SR TV HAUSA Domin Samun Ingantattun Labaru Cikin Harshen Hausa Kuci Gaba da Kasancewa da SR TV HAUSA
(1)

YANZU-YANZU _Al'ummar unguwar nasarawa Kaduna sun ziyarci jagoran harkar muslunci a Nigeria sheikh Ibraheem Zakzaky a gi...
05/11/2025

YANZU-YANZU _Al'ummar unguwar nasarawa Kaduna sun ziyarci jagoran harkar muslunci a Nigeria sheikh Ibraheem Zakzaky a gidansa dake birnin Abuja jiya talata: daga cikin wadanda suka kai masa ziyarar akwai limaman maslalacin Jumu'a da malaman kiristoci inda suka baiwa shehin lambar yabo ta zaman lafiya,

Bin Muhammad
_SR-TV-HAUSA

YAKIN SUDAN YANA KARE MASLAHAR KASASHEN YAMMA NE: Cewar El, Zakzaky Bin Muhammad KD 3rd November 2205A wata hira da kafa...
03/11/2025

YAKIN SUDAN YANA KARE MASLAHAR KASASHEN YAMMA NE: Cewar El, Zakzaky

Bin Muhammad KD
3rd November 2205

A wata hira da kafar watsa labarai ta iran press ta yi da jagoran harkar musulunci a najeriya shaikh Ibrahim Zakzaky yayi tir da ci gaba da kashe mutane da ake yi a kasar sudan inda kungiyar RSF ta kasashe sama da mutane 2000 a garin el-fishar, ya zargi kasar hadaddiyar daular larabawa da ruruta wutar yaki a madadin kasashen masu girma na duniya.

Yakin basasar dake ci gaba da gudana a kasar sudan ya dauki mummunan yanayi yayin da kungiyoyin masu samun goyon bayan kasashen waje ke kara kai hare-hare kan fararen hula da basu ji ba basu gani ba, bayanan na shaikh Zakzaky sun kara haskaka yanayin siyasar da ke mayar da kasashen afrika fagen yaki don rarrabasu,

Har ila yau shaikh Zakzaky yayi tir da mummunan rikicin da ya keta kasar sudan din gida biyu, kana ya jaddada cewa dukkan dakarun sojin kasar sudan da kuma kungiyar RSF yan kasar Sudan ne wadanda suke aiwatar da agenda kasashen waje, yace lamari ne mai taba zuciya a ce dan uwa yana kashe dan uwansa kawai don kare masalar wasu a waje,

Sheikh Zakzaky yace kasar hadaddiyar daular larabawa tana aiki ne a madadin kasashen yamma kuma matukar baa yanke hannun kasashen waje ba to yaki ba zai tsaya ba, fararen hula ne kawai zasu ci gaba da zama cikin mawuyacin hali.

SOJOJIN AMERICANA CI GABA DA KUSAN TAR KASAR VENEZUELA DA KAYAN YAKI Naurorin tauraron dan adam sun nuna hoton yadda soj...
02/11/2025

SOJOJIN AMERICANA CI GABA DA KUSAN TAR KASAR VENEZUELA DA KAYAN YAKI

Naurorin tauraron dan adam sun nuna hoton yadda sojojin Amurka suke kara kusantar kasar venuzuwela ciki har da jiragen yaki masu kai hare-hare duk da yake cewa shugaban Amurka Dolad trump ya karyata batun da ake yi na yunkurin kai mata harin soji,

Wannan matakin yana daya daga cikin yadda sojojin ruwan Amurka suka mayar da hankali a yankin karebiya, wanda hakan ya haifar da damuwa a latin Amurka game da yiyuwar daukar matakin soji na bangare daya kan kasar Venuzuwela ba tare da izinin majalisar dinkin duniya ko kuma kasashen duniya ba,

Washington ta yi ikirarin cewa za ta kai hari kan masu fataucin miyagun kwayoyi ne sai dai masu sa ido kan alamuran yankin sun bayyana cewa yanayin yadda ake turawa da sojoji da makamai a yankin yana nuna shirin da ake yi ne na daukar matakin soji ko kuma matsin lamba kan gwamnati venuzuwela don ta mika wuya.

Ana sa bangaren shugaban kasar venuzuwela yayi kira ga kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya da ya dauki mataki kan harin da Amurka ta kai kan wasu jirage dake kusa da ita a matsayin haramtacce kuma ta kare yancin kasar venuzuela

Bin Muhammad
_SR-TV-HAUSA

DA DUMI-DUMI: Farfesa Maqari ya Kai Ziyarar Haɗin Kan Malamai ga Sheikh Zakzaky a AbujaA wani yunƙuri na ƙarfafa haɗin k...
02/11/2025

DA DUMI-DUMI: Farfesa Maqari ya Kai Ziyarar Haɗin Kan Malamai ga Sheikh Zakzaky a Abuja

A wani yunƙuri na ƙarfafa haɗin kai tsakanin malamai da mabiya addinin Musulunci, Farfesa Ibraheem Maqari tare da tawagarsa sun kai ziyara ga Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky, a gidansa da ke Abuja, ranar Lahadi 2 ga watan Nuwamba 2025. A cikin tawagar Malaman akwai Shaikh Nura Khalid da sauran Malamai.

Ziyarar ta mayar da hankali ne kan buƙatar haɗin kai, fahimtar juna da kusanci a tsakanin malamai daga bangarori daban-daban na addinin Musulunci, domin ƙarfafa zumunci da kawar da sabani a tsakanin al’umma.

Rahoton da ya fito ne daga ofishin Jagora, ya labarta cewa Sheikh Zakzaky ya yi maraba da wannan yunƙuri, inda ya yabawa ƙoƙarin Farfesa Maqari da tawagarsa wajen ganin an samu haɗin kai da zaman lafiya a tsakanin malamai da mabiya addini.

A yayin ziyarar, Sheikh Zakzaky ya ƙarfafa buƙatar ci gaba da irin waɗannan tattaunawa, yana mai addu’ar alkhairi da nasara ga dukkanin ɓangarorin da ke neman haɗin kai da fahimtar juna.

Ziyarar ta Farfesa Maqari ta zo a lokaci mai muhimmanci, inda ake ci gaba da kira ga haɗin kan Musulmi a fadin duniya da kuma addu’a ga al’ummar Falasdinu da shahidan Musulunci.

Shugaban kasar Amurka Donald trump ya umarci jami'an Tsaron kasar ta Amurka da cewa su shirya daukar matakin soji kan Ni...
02/11/2025

Shugaban kasar Amurka Donald trump ya umarci jami'an Tsaron kasar ta Amurka da cewa su shirya daukar matakin soji kan Nigeria,

Me zakuce kan wannan kalami?

Bayan tsige shugaban sojojin Najeriya Kiristofa Musa, Sabon Hafsan Sojojin Najeriya, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, Ya ...
24/10/2025

Bayan tsige shugaban sojojin Najeriya Kiristofa Musa, Sabon Hafsan Sojojin Najeriya, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, Ya Yi Alkawarin Dawo da Zaman Lafiya a Ƙasar.

Sabon Babban Hafsan Sojojin Najeriya (COAS), Laftanar Janar Olufemi Oluyede, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya naɗa yau, ya yi alkawarin dawo da zaman lafiya da ƙarfafa yaƙi da ta’addanci a faɗin ƙasar. A jawabinsa na farko, Oluyede ya jaddada kudirinsa na shawo kan barazanar Boko Haram a jihar Borno da kuma kamo manyan shugabannin ’yan fashi kamar Bello Turji. An haifi Oluyede a garin Ikere, Jihar Ekiti, a shekarar 1968, inda ya fara aikin soja a shekarar 1987 a matsayin ɗalibi a Kwalejin Tsaro ta Najeriya, kuma aka ba shi mukamin Laftana na Biyu (Second Lieutenant) a hukumance a shekarar 1992 bayan ya kammala horo.

"Bani Da Hujjar Da Zan Faɗawa Allah Idan Na Yarda Cewa Malam Sheikh Dr Abduljabbar Kabara Ya Zagi Annabi (s.A.w)"Cewar F...
24/10/2025

"Bani Da Hujjar Da Zan Faɗawa Allah Idan Na Yarda Cewa Malam Sheikh Dr Abduljabbar Kabara Ya Zagi Annabi (s.A.w)"
Cewar Fitaccen Mai Yabon Manzon Allah (s.A.w) Shehi Mai Tajul Izzi.

Me zaku Ce...??

Al'ummar Najeriya Na Tafka Muhawara Kan Yadda shugabannin Ƙungiyar Izala Sukai ruwa sukai tsaki suka Jagoranci Hukumta S...
11/10/2025

Al'ummar Najeriya Na Tafka Muhawara Kan Yadda shugabannin Ƙungiyar Izala Sukai ruwa sukai tsaki suka Jagoranci Hukumta Shaikh Abduljabbar A Gefe Guda Kuma Basa Goyon Bayan A Hukumta Malam Lawan Triumph

Me zaku ce kan wannan zargi ?

WADANDA SUKA MUTU SAKAMAKON RUFTAWAR MAKARANTA YA KAI 54,-Bin Muhammad KD Daraktan ayyuka na hukumar bincike da ceto ta ...
06/10/2025

WADANDA SUKA MUTU SAKAMAKON RUFTAWAR MAKARANTA YA KAI 54,

-Bin Muhammad KD

Daraktan ayyuka na hukumar bincike da ceto ta kasar, ya shaidawa taron manema labarai cewa: "Mun gano gawarwakin mutane 54 da suka hada da ragowar mutane biyar," Yudhi Bramantyo,

Jami'an ceto na ci gaba da aiki ba dare ba rana domin gano wadanda suka bata. "Muna fatan kammala bincike a yau (Litinin) tare da mika gawarwakin" ga iyalai, in ji Yudhi.

Mataimakin darektan hukumar kula da bala'o'i ta kasar Budi Irawan, ya ce rugujewar ita ce bala'i mafi muni da aka taba samu a kasar Indonesia a bana. Ya kara da cewa akalla mutane 13 ne suka bata.

IRAN ZA TA CILLA TAURARON DAN ADAM DA SANDARARREN MAKAMASHI,-Bin Muhammad KD Hukumar sararin samaniya ta kasar Iran ta b...
04/10/2025

IRAN ZA TA CILLA TAURARON DAN ADAM DA SANDARARREN MAKAMASHI,

-Bin Muhammad KD

Hukumar sararin samaniya ta kasar Iran ta bada sanarwan shirin cilla tauraron dan’adam a cibiyar cilla taurarin dan’adam na Chabahar tare da amfani da sandarerren makamashi.

Kamfanin ndillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto shugaban hukumar Hassan Salarieh yana fadar haka a yau Asabar ya kuma kara da cewa, an kammala bangare na farko na cibiyar cilla taurarin yan’adam na Chabahar kuma hukumar ta fara shirin amfani da sandarerren makamashi don cillan taurarin yan’adam da suke gabanta, wadanda a shirye suke a cillasu.

Salarieh yace a halin yanzu akwai tauraron dan Adam mai suna Pars-2 da ke jiran cillawa, sannan hukumar zata ci gaba da aiki a bangare na 2 na cibiyar don kammala aikin cibiyar cilla tararin yan’adam mai amfani da makamashin ruwa.

Kamfanonin taurarin yan’adam na kasar Iran dai suna samar da taurarin yan’adam don ayyukan daban-daban, daga ciki har da sadarwa da kuma ayyukan noma da kula da yanayi da sauransu.

Banda haka hukumar tansa gina taurarin yan’adam haka ma kamfanoni masu zaman kansu a cikin gida, ba tare da taimakon wani daga waje ba.

KASAR IRAN TACE BA TA MARABA DA YAKI AMMA TA SHIRYA DON KARE KANTA,-Daga Bin Muhammad KD Mai magana da yawun gwamnatin I...
02/10/2025

KASAR IRAN TACE BA TA MARABA DA YAKI AMMA TA SHIRYA DON KARE KANTA,

-Daga Bin Muhammad KD

Mai magana da yawun gwamnatin Iran Fatemah Mohajerani ta fayyace cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta maraba da yaki, amma tana ci gaba da shirye-shiryen tsaro mafi girma don kare kanta.

Ta kara da cewa Tehran ta bayar da shawarar tattaunawa da Amurka kai tsaye a wata ganawa tare da ministocin Turai, amma wakilin Amurka Steve Witkoff ya ki isa a lokacin da aka tsara.

Mai magana da yawun gwamnatin ta Iran ta kuma bayyana cewa, kasarta na ci gaba da musayar sakwanni kai tsaye da kuma a fakaice, kuma tana ci gaba da kokarinta, sai dai kuma gwamnatocin yammacin duniya su ne ke warware alkawuran da suke dauka.

A nasa bangaren, sakataren majalisar kula da harkokin tsaron kasar, Ahmad Jannati, ya bayyana cewa mayar da takunkumin da aka kakabawa kasar Iran yana yadda ma’abota girman kan duniya ke saba alkawuran da suka yi da kuma rashin rikon amana.

Haka nan kuma ya kara da cewa, ‘yancin kai da karfin da Iran take da shi a kodayaushe su ne tushen kiyayya da gaba da kasashe masu girman kai suke nuna mata.

KASAR AMURKA TA AIKA DA JIRAGEN RUWAN NUKILIYA ZUWA KUSA DA RASHA,-Daga Bin Muhammad KD Shugaban kasar Amurka Donald Tru...
01/10/2025

KASAR AMURKA TA AIKA DA JIRAGEN RUWAN NUKILIYA ZUWA KUSA DA RASHA,

-Daga Bin Muhammad KD

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya fada a jiya Talata cewa ya bayar da umarnin aikewa da jiragen ruwa masu ninkaya a karkashin ruwa dake dauke da makaman Nukiliya da su karaci gabar ruwan kasar Rasha, a matsayin kandagarko.

Trump ya kara da cewa; A cikin kwanakin bayan an aiko mana sakon barazana daga Rasha, don haka na aike da jiragen ruwa masu makaman Nukiliya da shi ne makamai mafi hatsari.

Shugaban kasar na Amurka ya riya cewa kasarsa tana gaba da kasashen Rasha da China da ci gaban shekau 25 a fagagen kimiyya dakuma kera jiragen ruwa masu ninkaya a karkashin ruwa.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SR TV HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to SR TV HAUSA:

Share

Category